A yau Talata ne shugaban kasar Amurka Donald Trump ya isa kasar Saudiyya domin fara ziyarar aiki a karon farko tun da ya zama shugaban kasa.

Baya ga kasar Saudiyya shugaban kasar ta Amurka zai kuma kai Ziyara zuwa kasashen Qatar da Hadaddiyar Daular Larabawa da zummar bunkasa alaka  da larabawan yankin tekun Pasha kamar yadda majiyar bangarorin biyu take ambatawa.

Bugu da kari, kafafen watsa labarun Amurka sun ce, a yayin wannan ziyarar tashi, shugaban kasar Amurkan, zai yi kokarin samarwa kasarsa hannun jari da kasashen larabawa masu arziki za su zuba. Tun a baya dai Donald Trump ya bukacin ganin Saudiyya kadai ta kara yawan hannun jarinta a cikin Amurka da zai kai dala tiriliyan 1.

Kafar watsa labaru ta Axios ta ce; Babu wata ajanda a ziyarar ta Donald Trump zuwa kasashen larabawan da ta wuce ta kudi.”

Bugu da kari wani jami’in a yankin kasashen larabawan tekun pasha ya fada wa wannan kafar watsa labarun cewa; Kasuwanci shi ne babbar ajandar ziyarar Donald Trump.”

Yarima mai jiran gado na Saudiyya Muhammad Bin Salman ya yi alkawalin zuba hannun jari na dalar Amruka biliyan 600 a cikin shekaru 4 masu zuwa. Haka nan kuma Saudiyyar za ta sayi makamai na dala biliyan 100 daga Amurkan.

Ita ma kasar Qatar za ta zuba jarin dala biliyan 200 zuwa 300 a Amurka, kamar kuma yadda za ta sayi jiragen saman a kasuwanci da kudinsu zai kai dalar Amurka biliyan 2.

Ita kuwa Hadaddiyar Daular Larabawa ta yi alkawalin zuba hannun jari na dala tirliyan 1.4 a Amurka a cikin shekaru 10 masu zuwa.

A halin yanzu shugaban kasar ta Amurka ya cire batun kulla alaka a tsakanin Saudiyya da HKI daga cikin manufofin ziyarar tashi saboda yakin da ake ci gaba da yi a Gaza.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: shugaban kasar

এছাড়াও পড়ুন:

Ma’aikatan shari’a 97 sun samu ƙarin girma a Borno

Hukumar Shari’a ta Jihar Borno ta ƙara wa ma’aikatanta 97 girma bayan wani taro na kwanaki huɗu da ta gudanar a Maiduguri.

Muƙaddashin sakataren hukumar, Saleh Khala Jidda ne, ya bayyana hakan a wata sanarwa cewa ma’aikatan sun samu ƙarin girma ne saboda ƙwazonsu.

EFCC ta kama ’yan damfara a ɗakin karatun Obasanjo  ’Yan bindiga sun kashe gomman mutane a ƙauyukan Sakkwato

Waɗanda abin ya shafa sun hada da Majistare 10 daga matakin Majistare mataki na ɗaya zuwa Babban Majistare mataki na biyu.

Sai Majistare daga matakin farko zuwa Babban Majistare na biyu.

Sauran sun haɗa manyan Magatakarda daga mataki na ɗaya zuwa na biyu.

Sai dai a gefe guda, hukumar ta ɗauki mataki kan wani alƙalin Babban Kotun Majistare ta 4 da ke Wulari, Maiduguri, mai suna Yusuf Garba.

Binciken da kwamitin ƙorafe-ƙorafen jama’a ya gudanar ya gano cewa alƙalin ya karkatar da kuɗaɗen shiga na gwamnati har Naira 100,000.

Saboda haka aka sauke shi daga muƙaminsa tare da umartar ya kai rahoto ga Babban Magatakarda domin a sake masa muƙami.

Hukumar ta tabbatar wa jama’a cewa tana da niyyar ci gaba da tabbatar da gaskiya da adalci a kotuna.

Sannan ta ce za ta ladabtar da masu cin hanci da rashawa da kuma girmama masu gaskiya da riƙon amana.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Batun Rashin Lafiyar Tinubu
  • Mahukuntan Iraki Sun Bayyana Cewa: Akwai Yiwuwar Masu Ziyarar Arba’een Na Imam Husaini {a.s} Zasu Zarce Miliyan 4
  • Ofishin Jakadancin Sin A Birtaniya Ya Soki Furucin Kasashen G7 Dangane Da Yankin HK
  • Iraki: An bankado wani yunkurin kai wa masu ziyarar Arbaeen hari
  • Ma’aikatan shari’a 97 sun samu ƙarin girma a Borno
  • NDLEA Ta Kama Fasto Bisa Laifin Safarar Miyagun Kwayoyi A Legas 
  • Shirin Iskar Gas Na CNG Abin A Yaba Wa Shugaba Tinubu Ne -Shugaban IPMAN Na Ƙasa
  • Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan
  • ASUU na shirin sake tsunduma yajin aiki
  • Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar