Batun Zuba Hannun Jari A Amurka Ne Babbar Ajandar Ziyarar Shugaba Donald Trump Zuwa Kasashen Larabawan Yankin Tekun Pasha
Published: 13th, May 2025 GMT
A yau Talata ne shugaban kasar Amurka Donald Trump ya isa kasar Saudiyya domin fara ziyarar aiki a karon farko tun da ya zama shugaban kasa.
Baya ga kasar Saudiyya shugaban kasar ta Amurka zai kuma kai Ziyara zuwa kasashen Qatar da Hadaddiyar Daular Larabawa da zummar bunkasa alaka da larabawan yankin tekun Pasha kamar yadda majiyar bangarorin biyu take ambatawa.
Bugu da kari, kafafen watsa labarun Amurka sun ce, a yayin wannan ziyarar tashi, shugaban kasar Amurkan, zai yi kokarin samarwa kasarsa hannun jari da kasashen larabawa masu arziki za su zuba. Tun a baya dai Donald Trump ya bukacin ganin Saudiyya kadai ta kara yawan hannun jarinta a cikin Amurka da zai kai dala tiriliyan 1.
Kafar watsa labaru ta Axios ta ce; Babu wata ajanda a ziyarar ta Donald Trump zuwa kasashen larabawan da ta wuce ta kudi.”
Bugu da kari wani jami’in a yankin kasashen larabawan tekun pasha ya fada wa wannan kafar watsa labarun cewa; Kasuwanci shi ne babbar ajandar ziyarar Donald Trump.”
Yarima mai jiran gado na Saudiyya Muhammad Bin Salman ya yi alkawalin zuba hannun jari na dalar Amruka biliyan 600 a cikin shekaru 4 masu zuwa. Haka nan kuma Saudiyyar za ta sayi makamai na dala biliyan 100 daga Amurkan.
Ita ma kasar Qatar za ta zuba jarin dala biliyan 200 zuwa 300 a Amurka, kamar kuma yadda za ta sayi jiragen saman a kasuwanci da kudinsu zai kai dalar Amurka biliyan 2.
Ita kuwa Hadaddiyar Daular Larabawa ta yi alkawalin zuba hannun jari na dala tirliyan 1.4 a Amurka a cikin shekaru 10 masu zuwa.
A halin yanzu shugaban kasar ta Amurka ya cire batun kulla alaka a tsakanin Saudiyya da HKI daga cikin manufofin ziyarar tashi saboda yakin da ake ci gaba da yi a Gaza.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: shugaban kasar
এছাড়াও পড়ুন:
Barazanar Amurka Ta Kara Haraji Game Da Batun Ma’adanan Farin Karfe Ba Hanya Ce Mai Bullewa Ba
Ya kuma ce matakan takaita fitar da ma’adanan farin karfe da Sin ta dauka a baya bayan nan, ba su da alaka da kasar Pakistan. Yana cewa matakai ne da gwamnatin Sin ta dauka bisa doka da oda da nufin inganta tsarinta na fitar da kayayyaki. (Fa’iza Mustapha)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA