Gwamnatin jihar Kwara ta shirya wani gagarumin horo ga likitocin kiwon lafiya a fadin cibiyoyin kiwon lafiya na jihar kan yadda za a shawo kan cutar zazzabin cizon sauro.

 

Da yake sanar da bude horon a Ilorin, daraktan kula da lafiyar jama’a na jihar, Dokta Oluwatosin Fakayode, ya jadadda bukatar gaggawar gano cutar da wuri da kuma gaggauta magance cutar zazzabin cizon sauro, musamman a cikin mutane masu rauni kamar yara ‘yan kasa da shekaru biyar da mata masu juna biyu.

 

A cewarsa shirin ya kasance wani bangare na faffadan kokarin yaki da cutar zazzabin cizon sauro a jihar, gami da shirye-shiryen yakin rigakafin cutar zazzabin cizon sauro na 2025 (SMC).

 

Dokta Fakayode ya bayyana cewa horon zai kunshi zuwa gida-gida da maganin rigakafin zazzabin cizon sauro ga yara ‘yan watanni 3-59 a fadin kananan hukumomi 11 da suka cancanta a jihar Kwara.

 

Ya yi nuni da cewa har yanzu cutar zazzabin cizon sauro ta kasance babbar barazana ga lafiyar al’umma a Najeriya da jihar Kwara.

 

Dokta Fakayode ya yaba wa gwamnatin jihar bisa jajircewarta na kawar da cutar zazzabin cizon sauro da kuma saka hannun jarin da yake ci gaba da yi wajen karfafa karfin asibitoci a duk matakan kulawa.

 

A nata jawabin shugabar shirin na sashin zazzabin cizon sauro, Alhaja Latifat Abdullahi, ta bayyana jin dadin ta ga likitocin da suka halarci wannan taro kan sadaukarwar da suka yi a wannan fanni.

 

Ta jaddada mahimmancin ci gaba da haɓaka ƙwararru don samun ingantaccen sakamako na kiwon lafiya, ta ƙara da cewa ya kamata likitocin su yi amfani da sabbin dabarun da suka samu a aikace.

COV/ALI MUHAMMAD RABIU

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Kwara cutar zazzabin cizon sauro

এছাড়াও পড়ুন:

Yadda Iran ta yi jana’izar kwamandojinta da Isra’ila ta kashe

Iran ta gudanar da gagarumin jana’izar tare da karramawq ga kwamandojinta da masana kimiyyar nukiliya da wasu ’yan kasar da Isra’ila ta kashe a yankin kwana 12 da aka gwabza a tsakanin ƙasashen.

Iran ta shirya gagarumin jana’izar a ƙwaryar birnin Tehran kwana huɗu bayan Isra’ila ta amince da yarjejeniyar tsagaita wuta a yaƙin da ɓangarorin biyu ke iƙirarin nasara a yaƙin da aka fara ranar 13 ga Yuni, 2025.

A safiyar Asabar daruruwan dubban mutane ne suka fito ɗauke da tutocin ƙasar suna wake-waken jinjina domin karrama kwamandojin da suka kwanta dama a wurin jana’izar.

Mutanen sun kuma riƙa daga hotunan mamatan a matsayin waɗanda suka yi mutuwar shahada, a yayin da suke la’antar Isra’ila da Amurka.

Daga cikin kwamandojin da Isra’ila ta kashen har da jagoran Rundunar Juyin Juya Halin Musulunci na Iran Janar Hossein Salami da Janar Amir Ali Hajizadeh da wani ƙwararren masanin kimiyyar makamashin nukiliya, Mohammad Mehdi Tehranchi.

Za a iya tuna cewa Amurka ta kai wa cibiyoyin nukiliyar Iran hare-hare a ƙarshen makon da ya gabata, kafin daga bisani a tsagaita wuta.

Amurka da Isra’ila sun yi iƙirarin cewa hare-haren sun yi gagarumar nasarar ruguza shirin kera makaman nukiliya na Iran.

Amma daga bisani Iran ta ƙaryata su, da cewa babu wata illa da hare-haren suka yi wa shirinta da makamashin nukiliya.

A ranar Talata Shugaban addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya karyata abin da ya kira kambama harin da shugaban kasar Amurka, Donald Trump ya yi na cewa harin hare-haren sun mayar da shirin nukiliyar Iran baya da shekaru.

An kashe manyan sojojin da masa kimiyyar nukiliyar Iran ne a harin da Isra’ila ta fara kaiwa bisa hujjar neman daƙile shirin Iran na mallakar makamin nukiliya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin
  • An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata
  • ‘An kashe ’ya’yana da mijina da ’yan uwana a hanyar ɗaurin auren ɗana’
  • Yadda Iran ta yi jana’izar kwamandojinta da Isra’ila ta kashe
  • Jiniyoyin Gargadi Sun Tashi A HKI A Lokacinda Mayakan Ansarallah Suka Cilla Makamai Masu Linzami Kan Kasar
  •  Arakci:  Idan Aka Kai Iran Bango Za Ta Fito Da Hakikanin Karfin Da Take Da Shi
  • Bom ya kashe mutum hudu da raunata 21 a Yobe
  • Sojoji sun yi wa ’yan bindiga luguden wuta a Neja
  • Gwamnatin Katsina ta amince da ƙidayar almajirai, makarantun Islamiyya
  • Gwamnatin Katsina ta amince da ƙidayar almajirai da makarantun Islamiyya