An Horas Da Likitoci Akan Magance Tsananin Zazzabin Cizon Sauro
Published: 14th, May 2025 GMT
Gwamnatin jihar Kwara ta shirya wani gagarumin horo ga likitocin kiwon lafiya a fadin cibiyoyin kiwon lafiya na jihar kan yadda za a shawo kan cutar zazzabin cizon sauro.
Da yake sanar da bude horon a Ilorin, daraktan kula da lafiyar jama’a na jihar, Dokta Oluwatosin Fakayode, ya jadadda bukatar gaggawar gano cutar da wuri da kuma gaggauta magance cutar zazzabin cizon sauro, musamman a cikin mutane masu rauni kamar yara ‘yan kasa da shekaru biyar da mata masu juna biyu.
A cewarsa shirin ya kasance wani bangare na faffadan kokarin yaki da cutar zazzabin cizon sauro a jihar, gami da shirye-shiryen yakin rigakafin cutar zazzabin cizon sauro na 2025 (SMC).
Dokta Fakayode ya bayyana cewa horon zai kunshi zuwa gida-gida da maganin rigakafin zazzabin cizon sauro ga yara ‘yan watanni 3-59 a fadin kananan hukumomi 11 da suka cancanta a jihar Kwara.
Ya yi nuni da cewa har yanzu cutar zazzabin cizon sauro ta kasance babbar barazana ga lafiyar al’umma a Najeriya da jihar Kwara.
Dokta Fakayode ya yaba wa gwamnatin jihar bisa jajircewarta na kawar da cutar zazzabin cizon sauro da kuma saka hannun jarin da yake ci gaba da yi wajen karfafa karfin asibitoci a duk matakan kulawa.
A nata jawabin shugabar shirin na sashin zazzabin cizon sauro, Alhaja Latifat Abdullahi, ta bayyana jin dadin ta ga likitocin da suka halarci wannan taro kan sadaukarwar da suka yi a wannan fanni.
Ta jaddada mahimmancin ci gaba da haɓaka ƙwararru don samun ingantaccen sakamako na kiwon lafiya, ta ƙara da cewa ya kamata likitocin su yi amfani da sabbin dabarun da suka samu a aikace.
COV/ALI MUHAMMAD RABIU
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Kwara cutar zazzabin cizon sauro
এছাড়াও পড়ুন:
Sojoji sun hallaka ’yan ta’adda 5 a Borno
Rundunar sojin Najeriya, ta bayyana cewa dakarunta sun kashe ’yan ta’adda biyar a wani samame da suka kai yankin Magumeri da Gajiram, a Jihar Borno.
Kakakin rundunar Operation Haɗin Kai, Kanar Sani Uba, ya ce dakarun sun yi arangama da wasu ’yan ta’adda 24 da ke tafe a ƙafa a ranar Juma’a.
Mutane 2 sun rasu a rikicin manoma da makiyaya a Kebbi Rashin wutar lantarki ta kassara kasuwanci a Kaduna, Kano da KatsinaA cewar sanarwar da ya fitar, sojojin sun yi nasarar kashe biyar daga cikinsu tare da ƙwato kuɗi Naira miliyan biyar.
“An hangi ’yan ta’addan suna ƙone gidaje da kuma kai wa mutane hari, sai dakarun suka fara bin su, inda suka tsere zuwa ƙauyen Damjiyakiri,” in ji Kanar Sani.
Ya ƙara da cewa bayan awanni huɗu ana bin su, sojoji suka sake kai musu farmaki, inda suka kashe biyar daga cikinsu, sauran 19 kuma suka tsere da raunuka.
Abubuwan da aka ƙwato daga hannunsu, sun haɗa da bindiga ƙirar AK-47, jakar harsashi gyda biyar, waya guda ɗaya da wuƙa.