Gwamnatin kasar Burtaniya ta gabatarwa majalisar dokokin kasar sabbin tsare-tsare na shigar kasar ta hanyoyi daban-daban.

Jaridar Premium times ta Najeriya ta nakalto Firai ministan kasar ta Burtania Keir Starmer yana fadar cewa abinda yake gabatarwa Majalisar don neman amincewarta, wani tsari ne wanda zai kawo tsabta a harkokin bada Visar shiga kasar Burtaniya daga kasashen duniya daban-daban.

Starmer ya kara da cewa kafin haka tsarin shige da fice a kasar ta zama a tarwatse yake. A halin yanzu bayan samar da wadannan tsare-tsare masu zuwa kasar Burtania ko wadanda suke son zama a kasar dole ne su zama masu amfanar kasar,. Da farko dole su iya turancin ingishi da wasu abubuwan da zasu taimawa ci gaban kasar.

Kafin haka dai kididdiga ta nuna cewa zuwa cikin watan Yunin shekarar da ta gabata kadai mutane kimani 906, 000 suka kaura zuwa kasar. Wanda ya ninka na shekara ta 2019 har sau 4.

Yan Najeriya dai na daga cikin wadanda suke kaura zuwa kasar Burtaniya, ko don karatu ko aiki.

 Mai yuwa wannan sabon tsarin yana iya shafar kasar.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su
  • Amince Wa Al’umma Mallakar Makamai Zai Ƙara Tsananta Rashin Tsaro — IGP
  • Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada
  • Afirka CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwa Kan Kiwon Lafiya Da Kasar Sin
  • Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…
  • Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji
  • Sin Ta Sha Alwashin Rarraba Fasahohinta Na Ainihi Da Dabarunta Na Kirkire-Kirkire Tare Da Sauran Sassan Kasa Da Kasa
  • Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa
  • Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba
  • Barau Ya Nisanta Kansa Daga Kiraye-kirayen Ya Zama Mataimakin Tinubu A Zaben 2027