Burtaniya Ta Gabatar Da Sabbin Tsare-Tsare Na Shige Da Fice Da Kuma Bisar Shiga Kasar
Published: 13th, May 2025 GMT
Gwamnatin kasar Burtaniya ta gabatarwa majalisar dokokin kasar sabbin tsare-tsare na shigar kasar ta hanyoyi daban-daban.
Jaridar Premium times ta Najeriya ta nakalto Firai ministan kasar ta Burtania Keir Starmer yana fadar cewa abinda yake gabatarwa Majalisar don neman amincewarta, wani tsari ne wanda zai kawo tsabta a harkokin bada Visar shiga kasar Burtaniya daga kasashen duniya daban-daban.
Starmer ya kara da cewa kafin haka tsarin shige da fice a kasar ta zama a tarwatse yake. A halin yanzu bayan samar da wadannan tsare-tsare masu zuwa kasar Burtania ko wadanda suke son zama a kasar dole ne su zama masu amfanar kasar,. Da farko dole su iya turancin ingishi da wasu abubuwan da zasu taimawa ci gaban kasar.
Kafin haka dai kididdiga ta nuna cewa zuwa cikin watan Yunin shekarar da ta gabata kadai mutane kimani 906, 000 suka kaura zuwa kasar. Wanda ya ninka na shekara ta 2019 har sau 4.
Yan Najeriya dai na daga cikin wadanda suke kaura zuwa kasar Burtaniya, ko don karatu ko aiki.
Mai yuwa wannan sabon tsarin yana iya shafar kasar.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Yadda NATO Ta Yi Amfani Da Ita A Matsayin Dalilin Neman Fadada
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp