Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya bayyana fatan ganin kasashen India da Pakistan sun kai zuciya nesa, tare da warware sabani ta hanyar shawarwari da tattaunawa, kana su gujewa sake rura wutar tashin hankali.

Wang ya bayyana hakan ne a jiya Asabar, yayin tattaunawa ta wayar tarho da mashawarcin gwamnatin India ta fuskar tsaro Ajit Doval, inda ya ce Sin na goyon baya, da fatan sassan biyu za su kai ga cimma cikakken yanayi mai dorewa na dakatar da bude wuta ta hanyar tattaunawa, wanda hakan muhimmiyar moriya ce ta kasashen biyu, kuma zai cika burin sassan kasa da kasa.

Ya ce Sin ta yi tir da harin ta’addanci da ya auku a yankin Pahalgam, tana kuma adawa da duk wani nau’i na ayyukan ta’adanci.

2027: Har Yanzu Ba Mu Saka Ranar Fara Sabunta Katin Zabe Ba — INEC 2027: Har Yanzu Ba Mu Saka Ranar Fara Sabunta Katin Zabe Ba — INEC

Wang ya kara da cewa, a yanayin duniya na sauye-sauye da tangal-tangal, samun zaman lafiya da daidaito a yankin Asiya abu ne mai kima da ya wajaba a martaba.

A wani ci gaban kuma, Wang Yi ya zanta ta wayar tarho da mataimakin firaminista, kuma ministan harkokin wajen Pakistan Mohammad Ishaq Dar, inda ya ce a matsayin Pakistan da India na kasashe makwaftanta, Sin ta damu matuka da kara ta’azzarar rikici tsakanin kasashen biyu. Ya ce Sin ta gamsu Pakistan za ta tunkari wannan lamari cikin lumana, da aiwatar da matakai daidai da babban burin cimma moriya mai dorewa. (Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Nijeriya Ta Horar Da Likitoci 360 Don Magance Mutuwar Mata Masu Juna Biyu

Shugaban tsangayar Kula da Lafiyar Mata Masu Juna Biyu A Kwalejin Likitanci Ta Ƙasa (NPMCN), Farfesa Ayodeji Oluwole, ya bayyana hanyoyin da shirin ke bi wajen aiwatar da aikin:

” Wannan horo ya samar wa likitocinmu da fasaha ta zamani, kuma a cikin shekaru biyar, muna sa ran raguwar mutuwar mata masu juna biyu.

“Babban abin da ake buƙata shi ne a rage yawan mace-macen mata masu ciki a Nijeriya da Afirka, mun horar da likitoci kusan 220 da masu ba da shawara 140 a duk yankuna shida na siyasa.

“A yanzu haka, likitocin suna samun horo a babban asibitin ƙasa dake Abuja; hakan na da matuƙar muhimmanci wajen cimma manufofin gwamnatin tarayya na kula da lafiyar mata masu juna biyu,” in ji shi.

Farfesa Sanusi Ibrahim na Asibitin Koyarwa na Jami’ar Maiduguri ya bayyana cewa a Arewacin Nijeriya, mace-macen mata masu juna biyu na da matuƙar tayar da hankali.

“Wannan shirin ya ƙarfafa wa likitoci da ma’aikata, da dabarun ceton rai.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu
  • Dole Ne Afrika Ta Mayar Da Hankali Wajen Amfana Da Damarmakin Da Ke Tekunanta – Ɗantsoho
  • Dubban mutane sun yi zanga-zangar goyon bayan Falasɗinu a Isra’ila da Pakistan
  • Tehran Times: Mai Yiwuwa Iran da Amurka su koma Tattaunawa
  • Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan
  • Nijeriya Ta Horar Da Likitoci 360 Don Magance Mutuwar Mata Masu Juna Biyu
  • Tashin Gurneti Ya Hallaka Yara Uku A Borno
  • Ansarullah Ta Yi Gargadi Ga Amurka Da HKI Kan Kara Tada Hankali A Yakin
  • Iran Ta Kira Taron Gaggawa Na Kasashen Kungiyar OIC Dangane Da Gaza
  • Shugaban Ansarullah Ya Yi Gargadi Ga Amurka Da HKI Kan Kara Tada Hankali A Yakin