Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi, ya bayyana fatan ganin kasashen India da Pakistan sun kai zuciya nesa, tare da warware sabani ta hanyar shawarwari da tattaunawa, kana su gujewa sake rura wutar tashin hankali.

Wang ya bayyana hakan ne a jiya Asabar, yayin tattaunawa ta wayar tarho da mashawarcin gwamnatin India ta fuskar tsaro Ajit Doval, inda ya ce Sin na goyon baya, da fatan sassan biyu za su kai ga cimma cikakken yanayi mai dorewa na dakatar da bude wuta ta hanyar tattaunawa, wanda hakan muhimmiyar moriya ce ta kasashen biyu, kuma zai cika burin sassan kasa da kasa.

Ya ce Sin ta yi tir da harin ta’addanci da ya auku a yankin Pahalgam, tana kuma adawa da duk wani nau’i na ayyukan ta’adanci.

2027: Har Yanzu Ba Mu Saka Ranar Fara Sabunta Katin Zabe Ba — INEC 2027: Har Yanzu Ba Mu Saka Ranar Fara Sabunta Katin Zabe Ba — INEC

Wang ya kara da cewa, a yanayin duniya na sauye-sauye da tangal-tangal, samun zaman lafiya da daidaito a yankin Asiya abu ne mai kima da ya wajaba a martaba.

A wani ci gaban kuma, Wang Yi ya zanta ta wayar tarho da mataimakin firaminista, kuma ministan harkokin wajen Pakistan Mohammad Ishaq Dar, inda ya ce a matsayin Pakistan da India na kasashe makwaftanta, Sin ta damu matuka da kara ta’azzarar rikici tsakanin kasashen biyu. Ya ce Sin ta gamsu Pakistan za ta tunkari wannan lamari cikin lumana, da aiwatar da matakai daidai da babban burin cimma moriya mai dorewa. (Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Tehran ta bayyana aniyarta na karfafa hadin gwiwar ‘yan sanda da Nijar

Iran ta bayyana aniyarta ta karfafa hadin guiwar ‘yan sanda da Nijar.

Wanna bayanin ya fito ne a wani bangare na ziyarar da, Birgediya Janar Ahmad-Reza Radan, babban kwamandan rundunar tsaron Jamhuriyar Musulunci ta Iran ya kai ziyara a kasar Nijar a ran gadinsa a Afrika.

A ziyarar tasa ya gana da firaministan Nijar Ali Lamine Zeine, da ministan harkokin wajen kasar Bakary Yaou Sangaré, da ministan harkokin cikin gida Janar Mohammed Tomba, da shugaban ‘yan sandan Nijar Janar Omar Chiyani.

A yayin ganawar, M. Zein ya jaddada karfafa hadin gwiwar ‘yan sanda a tsakanin kasashen biyu inda ya ce: “A shirye muke mu yi amfani da gogewar da ‘yan sandan Jamhuriyar Musulunci ta Iran suke da ita a dukkan fannoni.”

A nasa bangaren Janar Radan ya bayyana aniyar Iran ta mika kwarewar aikin ‘yan sanda zuwa Nijar tare da bayyana fatan kasashen biyu za su iya fadada hadin gwiwarsu a dukkan fannoni da suka hada da yaki da ta’addanci da safarar muggan kwayoyi da manyan laifuka.

A yayin ganawarsa da Mista Sangare, babban jami’in na Iran ya jaddada saukaka hadin gwiwa wajen musayar bayanai tsakanin  kasashen biyu, da mika wadanda ake zargi ta hanyar Interpol.

Tunda farko dama bangarorin sun sanya hannu kan yarjejeniyar hadin gwiwa da fahimtar juna wacce Janar Radan na Iran da Janar Mohammed Tomba, ministan cikin gida na Nijar suka rattabawa hannu

Bangarorin biyu sun jaddada karfafa hadin gwiwar ‘yan sanda, da musayar bayanai da yaki da ta’addanci.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Da Amurka Sun Fahinci Juna Sosai A Zagaye Na 4 A Tattaunawa A Mascat
  • Kungiyar Hamas Ta Amince Ta Saki Fursinan Yaki Wanda Yake Da Jinsiyar Amurka Da HKI
  • Wang Yi: Ziyarar Shugaba Xi A Rasha Ta Kara Yaukaka Kawance Da Daidaito Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa
  • Tehran ta bayyana aniyarta na karfafa hadin gwiwar ‘yan sanda da Nijar
  • Pakisatan Ta Kore Cewa Ta Keta Yarjejeniyar Tsagaita Wutar Yaki
  •   Iran Ta Yi Maraba Da Tsayar Da Wutar Yaki A Tsakanin Indiya Da Pakistan
  • Shugaban Putin Ya Gana Da Sisi Don Karfafa Harkokin Kasuwanci Tsakanin Kasashen Biyu
  • Shugaban Amurka Ya Ce An Cimma Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta Tsakanin Pakistan Da Indiya
  • Sin Ta Nemi Indiya Da Pakistan Su Muhimmanta Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali