Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje
Published: 9th, May 2025 GMT
Minista Tuggar ya bayyana cewa, kasar Cuba ta taka mihimmiyar rawa wajen samar da ‘yancin kai ga wasu kasashen Afrika a lokacin da ake gwagwarmaryar kwato ‘yanci daga ‘yan mulkin mallaka a shekkarun 60s, 70s, 80s da 90s.
“Cuba da Nijeriya sun yi aiki tare wajen yaki da ‘yan mulkin mallaka a kasashen Angola, Namibia, Afrika ta Kudu da Zimbabwe” in ji shi, ya kara da cewa, wannan sabon yarjejeniyar za ta karfafa hadin kai a bangarorin kimiyya da fasaha, bincike da kuma samar da ci gaba mai dorewa.
A nasa tsokacin, Ministan harkokin waje na Cuba, ya ce, dangantakar da ke tsakanin Cuba da Afrika mai karfi ne, ya kuma gode wa Nijeriya a kan goyon bayan da ta bata a lokacin da Amurka ta sanya wa kasar takunkumin karya tattalin arziki.
Amma kuma yana da muhimmanci a fahimci cewa, fiye da shekara daya kenan Nijeriya bata nada cikakken ambasada ko wani wakili a kasar ta Cuba, hakan kuma yana matukar shafar harkokin huldar diflomasiya dana kasuwanci a tsakanin kasashen biyu.
A taron manema labarai na shekara-shekara (2025), da ma’aikatar harkokin kasashen waje ta yi kwananan, Minista Tuggar ya bayyana wa Duniya yadda ya tafiyar da harkokin ma’aikatar hulda da kasashen duniya, ya bayyana cewa, gwamnatin tarayya ta yi nisa wajen nada ambasadoji a kasashen duniya domin tuni sunayen wadanda za a nada yake a gaban majalisar dattawa domin amincewa.
Tuggar, wanda ya yi jawabi mai taken “Nasarori da kalubalen hulda da kasashen waje a karkashin mulkin Shugaba Bola Ahmed Tinubu”, ya kuma bayyana cewa, Nijeriya na aiki tukuru wajen gudanar da harkoki da kasahen waje ta hanyar la’akari da mutunci da kuma jin dadin ‘yan Nieriya a kasashe waje da kuma dawo da mutumcin Fasfot din Nijeriya a sassan duniya.
A wani bangaren kuma, kokarin Nijeriya na bunkasa tattalin arzikin kasa, ma’aikatar harkokin kasashen waje ta samo wa Nijeriya jarin Dala Biliyan 14 daga kasar Indiya, za a zuba jarin ne a bangarori da daban-daban na rayuwa da tattalin arzikin kasa haka kuma kasar Netherlands ta zuba jarin Fam miliyan 250 a bangarori daban-daban na tattalin arzikin Nijeriya.
A nasa tsokacin, tsohon Ambasadan kasar Jamus a Nijeriya, ya bayyana cewa, “An samu fiye da kashi 300 na wadanda suka yanki hannun jarin Nijeriya ‘Eurobond’. Wannan kuma alama ce na yadda duniya ta amince tare da rungumar Nijeriya domin gudanar da harkokin kasuwanci, tuni Nijeriya ta sanya hannu a yarjejeniya kasuwanci a tsakaninta da kasashen Jamus, Saudi Arabia, China, Ekuatorial Guinea, Faransa, Cuba, Katar, Birtaniya India, da kuma Brazil wanda hakan ya karfafa bangaren samar da wutar lantatrki, man fetur aikin gona da kuma samar da ayyukan yi ga dinbin matasan mu.”
Haka kuma masana sun bayyana cewa, tattaunawa da kasa Sin ya bude kofofin kasuwanci a tsakanin kasashen biyu ya kuma katse dukkan tarnakin da yake kawo cikas a harkokin kasashe biyu a baya. A halin yanzu an fara wata gaggarumar kasuwancin Kashu a tsakanin kasashen biyu an kuma kafa wata kwamiti domin samar da kyakyawar kalkibla domin samun nasarar hulda da juna a tsakanin kasashen. Haka kuma an samar da wata yarjejeniya a tsakanin kasar Ekuatorial Guinea, yarjejeniya nada nufin samar da butun gas tare da bunkasa yankin kahon Guinea gaba daya.
Duk da muhimmanci kasuwanci da zuba jari ga rayuwar kasa, a ‘yan shekarun baya an bata sunan Nijeriya saboda ayyukan rashin gaskiya da wasu ‘yan Nijeriya ke aikatawa a kasashe waje.
Amma a halin yanzu, Minista Tuggar ya bayar da tabbacin cewa, wannan gwamnatin za ta yi dukkan mai yiyuwa don farfado da mutumcin kasar nan tare da kuma kare mutumcin ‘yan Nijeriya a kasashe waje. Ya ce, ‘’muna fatan samun kasar da dukkan ‘yan Nijeriya za su shiga kowacce ofishin jakadanci ko filin jiragen sama ko kuma shiga wata yarjejeniyar kasuwanci ba tare da wani tsoron barazana ba.
“Ka sawwala Nijeriyar da farfot dinta ke bude wa ‘yan kasa kofofin kasuwanci a dukkan fadin duniya kuma a cikin mutuntawa.”
Duk da muhimmancin wadannan matakai da ake kokarin dauka da kuma wadanda aka dauka, ba za su yi wani tasiri ba har sai matakan sun kai ga bunkasa rayuwar al’ummar kasa, kasar da ke fama da dimbin marasa aikin yi da kuma hauhawar farashin kayan abinci dana makamashi.
Masu lura da al’amurran yau da kullum sun jinjina wa Ministan harkokin kasashen wajen Nijeriya a kan yadda ya tsayu wajen daukaka suna da mutuncin Nijeriya a idanun duniya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Nijeriya Tugar harkokin kasashe kasashen waje bayyana cewa kasuwanci a
এছাড়াও পড়ুন:
Najeriya ta yi watsi da sanya sunanta cikin jerin kasashen da ake tauye ’yancin addini
Gwamnatin Tarayya ta yi watsi da matakin da Gwamnatin Amurka ta dauka na sanya sunan Najeriya cikin jerin “Kasashen Da Ake Tauye ’Yancin Addini” , wato jerin kasashen da ake zargi da take hakkin addini.
Ministan Yada Labarai da Al’adu, Mohammed Idris Malagi ne, ya bayyana hakan a ranar Laraba a Abuja, inda ya ce matsalar tsaro da ake fuskanta a Najeriya ba ta shafi wani rukuni na addini ko kabila kai-tsaye ba.
Gwamnatin Tarayya ta fara shirin sayar da matatun manta ga ’yan kasuwa Hafsan sojin sama ya umarci a yawaita yi wa ’yan ta’adda ruwan bama-bamaiYa ce masu yada bayanan karya ne suka sa ake ganin kamar Najeriya tana nuna bambanci ta fuskar addini.
Malagi, ya ce gwamnati tana ci gaba da kokari wajen inganta harkar tsaro, sai dai ya bayyana cewa jami’an tsaro na wahala wajen isa wasu yankuna masu nisa a kan lokaci, don kai dauki.
Ya kara da cewa gwamnati na shirin dawo da tsarin tsaron al’umma domin tallafa wa rundunar tsaro ta kasa.
Da aka tambaye shi ko rashin nada jakadu ne ya haddasa wannan ce-ce-ku-ce da Amurka, Malagi ya ce dangantakar Najeriya da Amurka da sauran kasashe na tafiya daidai, kuma Shugaba Bola Tinubu na kokarin warware batun nada jakadu.
’Yan siyasar da suka fadi zabe ne ke yada labaran karya — AlakeA nasa bangaren, Ministan Harkokin Ma’adanai, Dele Alake, ya ce wasu ’yan siyasa da suka fadi a zabe ne ke yada labaran karya a Amurka cewa ana kashe Kiristoci a Najeriya.
Ya gargade su da cewa irin wadannan maganganu na iya haddasa karin tashin hankali wanda zai iya shafar kowa, ba tare da la’akari da addini ba.
Keyamo ya karyata zarginShi ma Ministan Harkokin Sufurin Jiragen Sama, Festus Keyamo, ya ce ikirarin Amurka karya ne, domin gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ba ta nuna wariyar addini.
Ya bayyana cewa yawancin manyan hafsoshin tsaro a Najeriya Kiristoci ne, sannan kuma Tinubu Musulmi ne matarsa Kirista, wacce malamar coci ce.
Keyamo, ya kara da cewa matsalolin tsaro a Najeriya suna shafar Musulmi da Kiristoci baki daya, don haka ya roki gwamnatin Amurka ta taimaka wajen yaki da ta’addanci maimakon dogaro da rahotannin karya.