Mali : An rushe dukkan jam’iyyun siyasa a hukumance
Published: 13th, May 2025 GMT
A kasar Mali a rushe dukkan jam’iyyun siyasa na kasar a hukumance.
bisa ga bukatar shugaban kasa da aka amince da shi a wannan Talata, yayin wani taron majalisar ministocin kasar, an rusa jam’iyyun siyasa a duk fadin kasar.
An kuma haramta tarurruka da sauran ayyukan jam’iyyun siyasar da kungiyoyin dake da alaka da siyasa ko kuma su fuskanci takunkumi.
Gwamnatin rikon kwarya ta ayyana cewa wannan matakin ya biyo bayan soke kundin tsarin mulkin jam’iyyun siyasa.
Dole ne a samar da sabuwar doka musamman don tafiyar da harkokin siyasar Mali, inji karamin minsitan kula da sauye-sauyen al’amuran siyasa a gidan talabijin na kasar.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: jam iyyun siyasa
এছাড়াও পড়ুন:
Kamfanonin Jiragen Ruwa Sun Yanke Hulda Da Isra’ila Saboda Matsalar Hare-Haren Kasar Yemen
Kamfanonin inshora za su kauracewa jiragen ruwa da ke da alaka da haramtacciyar kasar Isra’ila saboda tsoron fuskantar hare-haren Yemen
Jiragen ruwan da ke da alaka da haramtacciyar kasar Isra’ila za su fuskanci kaurace daga kamfanonin inshora, sakamakon munanan hare-haren baya-bayan nan da sojojin Yemen suka kai kan jiragen Magic Seas da Eternity Sea, wadanda suka kai ga nutsewa, a teku a ranar Alhamis.
A cewar wani rahoto da kamfanin dillancin labarai na Reuters ya wallafa ya bayyana cewa: Majiyoyin masana’antar inshora sun ce “kamfanonin inshora za su yi kokarin kauce wa rufe duk wani jirgin ruwa da ke da alaka da haramtacciyar kasar Isra’ila, ko da kuwa alakar a kaikaice ne.”
Kamfanin dillancin na Reuters ya nakalto daga Munro Anderson babban jami’in gudanarwa a Vessel Protect, wani kamfanin inshorar haɗarin ruwa na teku cewa: “Abin da suka gani a wannan makon yana kama da komawa ga ka’idojin kai hari a tsakiyar shekara ta 2024, wanda a zahiri ya haɗa da duk wani jirgin ruwa ko da kuwa yana da alaƙa mai nisa da haramtacciyar kasar Isra’ila.