Kazalika, sanarwar ta sanar da cewa, ana bukatar kwamtin ya sanya ido wajen ganin an gabatar da kasidu da alkalan da za su yi hunci kan bayanan da za a tattauna a wajen taron da baje kolin kanana da matsakaitan sana’oi da za a yi a wajen taron tare da kuma mika kyaututtuka ga ‘yan kasuwar kasar da suka dace, a wajen taron.

Acewar sanarwar, Mataimakin Shugaban Ma’aikata da ke a ofishin Mataimakin Shugaban kasa Sanata Ibrahim Hassan Hadejia ne, zai shugabaci kwamtin.

Sauran ‘ya’yan kwamtin sun hada da, Ministar Ma’aikatar Kasuwanci da zuba hannun jari Dakta Jumoke Oduwole; Ministan sadarwa da kere-kere da kuma tattalin arziki na fasahar zamani Dakta Bosun Tijani; Ministar yawon bude ido da kirkiren tattalin arziki Hannatu Musawa da kuma karamin Ministan Kasuwanci da zuba hannun jari Sanata John Owan-Enoh.

Sauran su ne, Babbar Darakta ta Hukumar NEPC Madam Nonye Ayeni; Babban Sakatariya ta Hukumar NIPC Madam Aisha Rimi; Manajin Darakta na Bankin Masana’antu Dakta Olasupo Olusi; Shugaban Hukumar FIRS Mista . Zacch Adedeji da sauransu.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Nijeriya

এছাড়াও পড়ুন:

Nijeriya ta soke ba da tallafin karatu a ƙetare

Gwamnatin Nijeriya ta sanar da dakatar da tsarin bai wa ɗalibai tallafi domin samun damar zuwa ƙetare ƙarin ilimi.

Ministan Ilimi, Tunji Alausa, shi ne ya sanar da wannan mataki, da ke nufin cewa za a kawo ƙarshen wannan tsari da aka share tsawon shekaru ana aiwatarwa.

Yadda yara 5 suka mutu a cikin motar da aka yi watsi da ita Yadda rashin wutar lantarki ke ajalin rayuka a manyan asibitoci

Mista Alausa ya bayyana cewa wannan matakai ya samu ne sakamako nazari da aka yi wajen sanya ƙaƙƙarfan jari a manyan makarantun ƙasar.

Ministan ya ce daga yanzu babu batun bai wa ’yan ƙasar kuɗaɗen ƙaro ilimi daga ƙetare, saboda yanayi da ake ciki da ma kyawun tsari da ake da shi a cikin ƙasar.

A cewarsa, dukkannin kwasa-kwasan da ’yan Nijeriyar ke zuwa wasu ƙasashen domin nazarin su, akwai su a cikin jami’o’i da ma kwalejojin fasaha masu nagarta da ake da su.

Ministan ya ce kuɗaɗen da ake kashewa wajen daukar nauyin karatun ɗaliban a ƙetare, zai fi dacewa a sanya su wajen inganta jami’o’in da kwalejojin da ake da su.

Sanarwar na zuwa ne a yayin da Hukumar Bunƙasa Arewa maso Yamma NWDC ta soke bayar da tallafin karatu ga ɗaliban da suka fito daga yankin.

Makonni kaɗan da suka gabata ne Hukumar ta NWDC ta fitar da sanarwar cewa tana neman haziƙan ɗalibai da suka fito daga yankin domin ɗaukar nauyin karatunsu a wasu ƙasashe ƙetare.

Sai dai wata sanarwa da hukumar ta fitar safiyar wannan Juma’ar, ta ce an soke tsarin, inda za ta mayar da hankali kan wasu ababen domin bunƙasa yankin.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaba Xi Zai Halarci Bikin Bude Taron Ministoci Na Dandalin Sin Da CELAC Karo Na 4
  • Shugaban NPA Ya Sha Yabo Kan Yadda Ya Bunƙasa Tashar Jiragen Ruwa Ta Onne
  • An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva
  • Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet
  • Sin Da Rasha Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Game Da Zurfafa Dangantakar Abokantaka Ta Hadin Gwiwa Bisa Manyan Tsare-tsare A Sabon Zamani
  • Hukumar Fina-Finai Ta Kasar Sin Ta Kulla Takardar Hada Hannu Da Hukumar Al’adu Ta Kasar Rasha
  • Nijeriya ta soke ba da tallafin karatu a ƙetare
  • 2027: Tsohon IGP ya fito takarar gwamna, ƙungiya ta mara masa baya a Nasarawa 
  • Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje