Babban hafsan hafsoshin sojojin JMI ya bayyana cewa sojojin kasar musamman sojojin ruwa a shirye suke su shigaba yaki dank are kasar a ko yauce, ya kuma kara da cewa idan makiya sun yi wani kuskure zasu yi nadamar hakan.

Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ya nakalto Manjo Janar Mohammad Hussain Bakiri yana fadar haka a jiya litinin a lokacinda shi da wasu manya manayan jami’an sojojin kasar suka kai ziyarar ganewa kansu irin shirin da sojojin kasar suke ciki a tashoshin jiragen ruwa da suke gabar tekun Farisa da kuma arewacin mashigar ruwa ta Hurmus

Tare da manjo janar Bakiri dai akwai kwamandan sojojin ruwa na dakarun IRGC  Manjo Janar Abdolrahim Mousavi, sai kuma Manjo Janar Hossein Salami shugaban Lundunonin IRGC da kuma wasu manya-manyan jami’an sojojin kasar.

A wani labarin kuma Janar Salami babban kwamandan sojojin IRGC gaba daya ya bayyana cewa Iran zata kai hari a kan duk wani wurin da makami ya rashi zuwa kasar.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: sojojin kasar

এছাড়াও পড়ুন:

Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Game Da Babban Shirin Shekaru Biyar-Biyar Na Bunkasa Tattalin Arziki Da Zamantakewar Kasar Sin Na 15

Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya ba da umurni kan babban shirin shekaru biyar-biyar na bunkasa tattalin arziki da zamantakewar kasar Sin karo na 15, inda ya nanata wajibcin tsai da shiri bisa halin da ake ciki, matakin da ya kasance muhimmiyar dabarar jam’iyyar kwaminis ta Sin wato JKS a fannin gudanar da harkokin kasa, kuma fifiko a siyasance na tsarin mulkin gurguzu mai salon musamman na Sin.

Xi ya ce tsai da babban shiri na 15 na da babbar ma’ana ga tabbatar da manyan tsare-tsare da aka tanada a yayin babban taro karo na 20 na JKS, da gaggauta zamanantar da al’ummar Sinawa. Don haka dole ne a samar da shiri bisa halin da ake ciki, bisa tushen demokuradiyya da doka da shari’a, ta yadda al’ummun kasa za su iya cin gajiyar manyan tsare-tsare.

Ban da wannan kuma, an saurari ra’ayin jama’a daga dukkan fannoni, da koyi da dabarun da aka samu a ayyukan yau da kullum, don dunkule ayyukan da za a yi da manufofin da za a dauka, ta yadda za a cimma nasarar aiwatar da shiri mai inganci.

Sin za ta gudanar da shiri na shekaru biyar-biyar na 15 a badi, yanzu kwamitin kolin JKS na rubuta shawarar tsai da shirin. (Amina Xu)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jirgin Karshe Na Alhazan Jihar Kwara Ya Isa Kasa Mai Tsarki
  • Sojojin HKI Sun Bude Wuta Kan Jami’an Diblomasiyyar Wadanda Suka Je Jenin
  • Sojojin Sudan Sun Gama Tsarkaka Birnin Khartoum Daga ‘Yan Tawayen Rapid Support Forces
  • Sojojin Sudan Sun Sanar Da Kammala “Tsarkake” Birnin Kahartum Daga Dakarun  RSF
  • Ana Kara Samun Karuwar Sojojin HKI Da Suke Kashe Kansu
  •  Sojojin HKI Suna Ci Gaba Da Kashe Falasdinawa ‘Yan Gudun Hijira A Lokacin Da Suke Bacci
  • ‘Yan Gwagwarmayar Falasdinawa Sun Halaka Sojojin Sahayoniyya Tare Da Jikkata Wasu A Beit Lahiya
  • Rasha Ta Ce Za Ta Tattauna Da Ukraine Don Yin Sulhu Game Da Yaƙin Da Suke Tafkawa
  • Xi Jinping Ya Ba Da Umurni Game Da Babban Shirin Shekaru Biyar-Biyar Na Bunkasa Tattalin Arziki Da Zamantakewar Kasar Sin Na 15
  • NAJERIYA A YAU: Mece ce Makomar Dimokuraɗiyya Idan Aka Wajabta Kada Kuri’a?