Babban hafsan hafsoshin sojojin JMI ya bayyana cewa sojojin kasar musamman sojojin ruwa a shirye suke su shigaba yaki dank are kasar a ko yauce, ya kuma kara da cewa idan makiya sun yi wani kuskure zasu yi nadamar hakan.

Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ya nakalto Manjo Janar Mohammad Hussain Bakiri yana fadar haka a jiya litinin a lokacinda shi da wasu manya manayan jami’an sojojin kasar suka kai ziyarar ganewa kansu irin shirin da sojojin kasar suke ciki a tashoshin jiragen ruwa da suke gabar tekun Farisa da kuma arewacin mashigar ruwa ta Hurmus

Tare da manjo janar Bakiri dai akwai kwamandan sojojin ruwa na dakarun IRGC  Manjo Janar Abdolrahim Mousavi, sai kuma Manjo Janar Hossein Salami shugaban Lundunonin IRGC da kuma wasu manya-manyan jami’an sojojin kasar.

A wani labarin kuma Janar Salami babban kwamandan sojojin IRGC gaba daya ya bayyana cewa Iran zata kai hari a kan duk wani wurin da makami ya rashi zuwa kasar.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: sojojin kasar

এছাড়াও পড়ুন:

NPA Ta Bukaci Samar Da Tsare-tsare Kan Baraguzan Jiragen Ruwa A Cikin Teku

Dantsoho wanda ya samu wakilicin Babban Manajan a Hukumar ta NPA Femi Oyewole, ya bayyana cewa, Shugaban Hukumar ta NPA, Hukumar ta mayar da hankali wajen ganin cewa, ana kare kimar Tekunan kasar.

“Hadurran zuba baraguzan kusan a kurkusa suke, wanda kuma, suke ci gaba da karuwa, wanda hakan ya nuna cewa, akwai matukar bukatar a dakile yadda ake duba baragunzan, a cikin Tekunan, baki daya,” Inji Dantsoho.

Ya ci gaba da cewa, Hukumar ta NPA bata yi kasa a guiwa ba, wajen daukar matakan da suka kamata, domin magance wannan matsalar.

“Duba da cewa, muna gudanar da ayyukan NPA yadda ya kamata da kuma bin ka;idojin da ke tafiyar da Hukumar, musamman wajen bai wa kayan Hukumar da ke a daukacin Tashoshin Jiragen Ruwan kasar kariya, kamar yadda suka kasance a matakin na kasa da kasa na dakile gurbatar da Jiragen Ruwa ke janyo wa, musamman duba da kundin tsari na (MARPOL 73/78), za mu ci gaba da lalubo da mafita kan zubar baraguzai a Tekunan kasar,” A cewarsa.

Shugaban ya kara da cewa, kayan aikin NPA na bukatar a samar masu kariyar da kamata, musamman ta hanyar bai wa Jiragen ruwa da ke tsayawa a Tashoshin kariyar da ta kamata.

Dantsoho ya bayyana cewa, NPA akai-akai ta kan tabbatar da ana ci gaba da tsaftace Tekunan daga kalubalen baraguzan da duk wata bola, da ake zubawa a cikin Tekunan kasar a daukacin Tashohin Jiragen Ruwan kasar.

Shugaban ya yi nuni da cewa, ta hanyar kwashe baraguzan da sauran bolar robobin da ake zubawar a cikin Tekunan ne, kadai, za a iya kare rayuwar dabbobin da ke rayuwa a cikin Tekunan tare da kuma samar wa Jiragen Ruwan saukin yin zirga-zirga a kan Tekunan kasar.

Shi kuwa a na sa jawabin a wajen taron Babab Sakataren Cibiyar kungiyar masu fito kaya a Jiragen Ruwa na kasa Dakta Pius Akutah, yabawa kungiyar ta wakilan masu wallafa rahotanin a Tashoshin Jiragen Ruwan kasar kan zabo wannan maudu’in domin a tattauna a kansa

Ya kuma jaddda bukatar da a tabbatar da ana tsaftace hanyoyin Ruwa da ke a Tekunan kasar, musamman domin Jiragen Ruwan da ke hawansu, su samu saukin tafiya akai ba tare da wata tangarda ba.

Akutah, wanda Mataimakin Darakata a sashen sanya ido na cibiyar ya wakilce shi a wajen taron Adeshina Sarumi, ya yi nuni da cewa, samun baraguzan a hanyoyin Ruwan na haifar da cikas ga zirga-zirgar Jiragen Ruwan.

Shi kuwa Manajin Darakta na Hukumar NIWA Bolaji Oyebamiji, ya bukaci masu ruwa da tsaki a fannin da su yi dukkan mai yuwa, domin a dakile wannan kalubalen da ake fuskanta, musaman ta hanyar wyar da kan alummar da ke da zama a daura da Tekunan kasar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  IRGC: Duk Wani Wuce Gona Da Iri Na ‘Yan Sahayoniya Zai Gaggauta Rushewarsu
  • Sheikh Na’im Kasim Yace Kare Kasa Baya Bukatar Izini Daga Wani
  • Sojojin HKI Kimani 40 Ne Suka Halaka Ko Suka Jikata A Jiya Jumma’a A Yankin Shuja’iyya Na Birnin Gaza
  • Shugaban Kasar Iran Ya Gabatar Da Jawabio A Taron Kolin Kungiyar ECO Musamman Kan Harin Da Kasarsa Ta Fuskanta
  •  Antonio Guterres Ya Kadu Saboda Mummunan Halin Da Falasdinawan Gaza Suke Ciki
  • NPA Ta Bukaci Samar Da Tsare-tsare Kan Baraguzan Jiragen Ruwa A Cikin Teku
  • Kwamandan Sojojin Iran Ya Ziyarci Gidan Babban Jami’in Sojin Kasar Da Ya Yii Shahada Lokacin Yakin Baya-Bayan Nan
  • Isra’ila Zata Gamu Da Maida Martani Mai Tsanani Idan Ta Kuskura Ta Sabonta Yaki Da Iran
  • An Gudanar Da Taron Girmama Shahidan Yakin Kwanaki 12 A Nan Tehran
  • Kalibof Yace: Iran Zata Maida Martani Mai Tsanani Kan HKI Idan Ta Sake Bude Yaki da Iran