Za mu ci gaba da aikin haƙo ɗanyen mai a Arewa —NNPCL
Published: 12th, May 2025 GMT
Kamfanin Mai na Kasa (NNPCL) ya bayyana cewa zai ci gaba da aikin haƙa danyen mai a Arewa da ke yankin Kolmani.
Shugaban NNPCL, Bayo Ojulari ne ya sanar da aniyar kamfanin na ci gaba da aikin haƙar mai a yankunan arewa da gwamnatin Buhari da ta gabata ta fara.
Bayo Ojulari ya kuma addada aniyar NNPCL na kammala aikin bututun iskar gas da ya taso daga Ajaokuta a Jihar Kogi ya bi ta Abuja da Kaduna zuwa Kano (AKK).
A zantawarsa da kafar yaɗa labarai ta BBC, Injiniya Bayo ya ce, Za mu ci gaba da aikin haƙo mai a Kolmani da sauran wurare. Bayan aikin haƙo man, za mu kuma tabbatar da cewa mun gama aikin bututun man gas daga Ajaokuta zuwa Kano,” in ji shi.
An kama ɗan daba mai yin fashi a cikin shigar mata a Kano Boko Haram ta ƙwace makaman sojoji na tiriliyoyin naira —MajalisaA cewarsa, ayyukan haƙar man da na bututun iskar gas ɗin AKK za su taimaka wajen farfaɗo da kamfanonin da aka rufe a baya domin su ci gaba da aiki sannan a buɗe wasu sababbi.
“Wannan zai amfanar da yankin Arewa ta yadda kowa zai ci moriyarsa saboda za a samu bunƙasar arziki,” a cewarsa.
Game da ce-ce-ku-ce da ya biyo bayan naɗa, inda ake zargin Shugaba Tinubu da fifita ’yan yankin Kudu wajen rabon mukamai a gwamnatinsa, shugaban na NNPC ya ce, shi ma ɗan Arewa ne, kuma ya yi maganganu a lokacin da aka sanar da naɗa shi.
Don haka ya buƙaci al’ummar Arewa da ma ƙasar baki ɗaya da su ba shi goyon baya, kuma su taimaka masa da addu’a domin ya samu nasarar ciyar da yankin da ma ƙasar gaba.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Za a gyara tarbiyar tubabbun ’yan daban Kano
Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ya shawarci matasan da ake ribatarsu a matsayin ’yan daban siyasa da suka tuba da su guji tashin hankali, yana tabbatar musu da shirye-shiryen gwamnatinsa na gyara tarbiyarsu tare da mayar da su cikin al’umma.
Gwamnan ya yi wannan alkawari ne a taron wuni ɗaya da aka gudanar tare da shugabannin rukunan ’yan daban da suka tuba a ƙarƙashin Shirin Safe Corridor.
Direba ɗaya ya tsira a hatsarin tankokin dakon iskar gas a Zariya An kama mutumin da ake zargi da kashe jami’in sibil difens a JigawaGwamnan, wanda Kwamishinan Yaɗa Labarai da Harkokin Cikin Gida, Ibrahim Waiya, ya wakilta, ya ce: “Ba za a sake ɗaukar makami da sunan fadan siyasa ko wasu munanan dabi’u ba.
“Za mu gyara muku tarbiya, mu tabbatar kun samu ababen yi da suka dace domin samun abun dogaro da kai. Za mu karɓe ku ɗaya bayan ɗaya, mu gyara ku, mu tura ku inda kuka fi dacewa.”
Waiya ya bayyana cewa wasu daga cikin tubabbun mutanen da aka yi wa rajista a baya a cikin shirin sun riga sun rasu, inda gwamnati za ta sake gudanar da sabon aikin tantancewa domin sabunta bayanai.
Ya jaddada cewa wannan shiri ba na siyasa ba ne, yana mai cewa manufarsa ita ce kawar da matsalar ‘yan daba da sauran munanan halaye a jihar.
“Mutane da dama masu shekarunku suna yin abubuwa masu kyau. Mun fahimci cewa ba ku ci moriyar wasu shirye-shirye na tallafi ba a baya, amma yanzu mun tsaya tsayin daka domin ku,” in ji shi.
Sauran masu jawabi a yayin taron sun haɗa da Kwamandan Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi (NDLEA) na Kano, Kwamishinan ’Yan Sanda na Jihar, da sauran masu ruwa da tsaki wajen yaƙi da shan miyagun ƙwayoyi a Kano.