Aminiya:
2025-05-12@15:55:13 GMT

Za mu ci gaba da aikin haƙo ɗanyen mai a Arewa —NNPCL

Published: 12th, May 2025 GMT

Kamfanin Mai na Kasa (NNPCL) ya bayyana cewa zai ci gaba da aikin haƙa danyen mai a Arewa da ke yankin Kolmani.

Shugaban NNPCL, Bayo Ojulari ne ya sanar da aniyar kamfanin na ci gaba da aikin haƙar mai a yankunan arewa da gwamnatin Buhari da ta gabata ta fara.

Bayo Ojulari ya kuma addada aniyar NNPCL na kammala aikin bututun iskar gas da ya taso daga Ajaokuta a Jihar Kogi ya bi ta Abuja da Kaduna zuwa Kano (AKK).

A zantawarsa da kafar yaɗa labarai ta BBC, Injiniya Bayo ya ce, Za mu ci gaba da aikin haƙo mai a Kolmani da sauran wurare. Bayan aikin haƙo man, za mu kuma tabbatar da cewa mun gama aikin bututun man gas daga Ajaokuta zuwa Kano,” in ji shi.

An kama ɗan daba mai yin fashi a cikin shigar mata a Kano Boko Haram ta ƙwace makaman sojoji na tiriliyoyin naira —Majalisa

A cewarsa, ayyukan haƙar man da na bututun iskar gas ɗin AKK za su taimaka wajen farfaɗo da kamfanonin da aka rufe a baya domin su ci gaba da aiki sannan a buɗe wasu sababbi.

“Wannan zai amfanar da yankin Arewa ta yadda kowa zai ci moriyarsa saboda za a samu bunƙasar arziki,” a cewarsa.

Game da ce-ce-ku-ce da ya biyo bayan naɗa, inda ake zargin Shugaba Tinubu da fifita ’yan yankin Kudu wajen rabon mukamai a gwamnatinsa, shugaban na NNPC ya ce, shi ma ɗan Arewa ne, kuma ya yi maganganu a lokacin da aka sanar da naɗa shi.

Don haka ya buƙaci al’ummar Arewa da ma ƙasar baki ɗaya da su ba shi goyon baya, kuma su taimaka masa da addu’a domin ya samu nasarar ciyar da yankin da ma ƙasar gaba.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Arewa haƙar mai

এছাড়াও পড়ুন:

Za a faɗaɗa Gasar Kofin Duniya ta Mata zuwa ƙasashe 48 — FIFA

Hukumar Ƙwallon Kafa ta Duniya, FIFA, ta ce za ta faɗaɗa Gasar Kofin Duniya ta Mata daga tawagogi 32 zuwa 48.

FIFA ta ce sabon tsarin zai fara aiki ne daga gasar 2031, wadda Amurka ce kawai ke neman ɗaukar nauyinta.

Sauya sheƙa bayan cin moriyar jam’iyya butulci ne — Kwankwaso HOTUNA: An ƙaddamar da tashin sahun farko na maniyyatan Nijeriya zuwa Saudiyya

Tuni dai FIFA ta faɗaɗa gasar cin Kofin Duniya ta Maza da za a yi nan gaba, zuwa wannan adadi.

FIFA ta ce ta ɗauki matakin ne saboda yadda gasar ke ci gaba da samun karɓuwa da farin jini tsakanin masoya ƙwallon ƙafa a duniya.

Masu suka sun zargi hukumar da fifita kuɗin da za ta samau fiye da la’akari da yawan wasanni da ’yan wasa za su fuskanta.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • NNPP Ta Yi Asarar Ɗan Majalisa A Kano, Ya Koma APC
  • An kama ɗan daba mai yin fashi a cikin shigar mata a Kano
  • Zamfara Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Kula Da Aikin 2025 Domin Kyautata Jin Dadin Alhazan Jihar 
  • Trump Ya Bukaci Ukraine Ta Amince Da Tayin Putin Na Bude Tattaunawa A Birnin Istambul
  • Iran ta ce tattaunawa ta hudu da Amurka tana da wahala amma tana da amfani  
  • Muhawarar da ta ɓarke kan saya wa Sarkin Kano motocin naira miliyan 670
  • Matakan da gwamnonin Arewa suke so a ɗauka kan matsalar tsaron yankin
  • Za a faɗaɗa Gasar Kofin Duniya ta Mata zuwa ƙasashe 48 — FIFA
  • Yemen Tana Bukukuwan Samun Nasara Kan Amurka Kuma Zata Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Gaza