Za mu ci gaba da aikin haƙo ɗanyen mai a Arewa —NNPCL
Published: 12th, May 2025 GMT
Kamfanin Mai na Kasa (NNPCL) ya bayyana cewa zai ci gaba da aikin haƙa danyen mai a Arewa da ke yankin Kolmani.
Shugaban NNPCL, Bayo Ojulari ne ya sanar da aniyar kamfanin na ci gaba da aikin haƙar mai a yankunan arewa da gwamnatin Buhari da ta gabata ta fara.
Bayo Ojulari ya kuma addada aniyar NNPCL na kammala aikin bututun iskar gas da ya taso daga Ajaokuta a Jihar Kogi ya bi ta Abuja da Kaduna zuwa Kano (AKK).
A zantawarsa da kafar yaɗa labarai ta BBC, Injiniya Bayo ya ce, Za mu ci gaba da aikin haƙo mai a Kolmani da sauran wurare. Bayan aikin haƙo man, za mu kuma tabbatar da cewa mun gama aikin bututun man gas daga Ajaokuta zuwa Kano,” in ji shi.
An kama ɗan daba mai yin fashi a cikin shigar mata a Kano Boko Haram ta ƙwace makaman sojoji na tiriliyoyin naira —MajalisaA cewarsa, ayyukan haƙar man da na bututun iskar gas ɗin AKK za su taimaka wajen farfaɗo da kamfanonin da aka rufe a baya domin su ci gaba da aiki sannan a buɗe wasu sababbi.
“Wannan zai amfanar da yankin Arewa ta yadda kowa zai ci moriyarsa saboda za a samu bunƙasar arziki,” a cewarsa.
Game da ce-ce-ku-ce da ya biyo bayan naɗa, inda ake zargin Shugaba Tinubu da fifita ’yan yankin Kudu wajen rabon mukamai a gwamnatinsa, shugaban na NNPC ya ce, shi ma ɗan Arewa ne, kuma ya yi maganganu a lokacin da aka sanar da naɗa shi.
Don haka ya buƙaci al’ummar Arewa da ma ƙasar baki ɗaya da su ba shi goyon baya, kuma su taimaka masa da addu’a domin ya samu nasarar ciyar da yankin da ma ƙasar gaba.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Ƙarancin Abinci: UNICEF ta tallafa wa yara 600,000 a Borno da Yobe
Asusun kula da Ƙananan yara na Majalisar Ɗinkin Duniya (UNICEF) ya bayar da rahoton samun gagarumin ci gaba a ƙoƙarin da take yi na ceto rayukan ƙananan yara.
Da kuma samar da damammakin ci gaba a jihohin Borno da Yobe duk da ƙalubalen da ke tattare da tashe-tashen hankula da talauci, UNICEF ta samu gagarumar nasara a jihohin.
Gwamnatin Katsina ta amince da ƙidayar almajirai, makarantun Islamiyya ’Yan sanda sun kashe ’yan fashi da ƙwato makamai a KadunaShugaban ofishin UNICEF na Maiduguri, Joseph Senesie ne ya bayyana hakan a jawabin da ya yi a lokacin wani taron tattaunawa da manema labarai kan ɗa’ar aikin jarida da rahoton kare haƙƙin yara a Damaturu, babban birnin Jihar Yobe.
A cewarsa, a shekarar 2024 UNICEF ta tallafawa jinyar yara kimanin dubu 600 da ke fama da matsanancin halin rashin abinci mai gina jiki, tare da yi wa yara miliyan 1.2 allurar rigakafin cutar kwalara, tare da kai wa mutane miliyan 1.6 allurar rigakafin cutar kwalara.
Bugu da kari, an tallafa wa sama da yara rabin miliyan masu watanni 0-59 da rajistar haihuwa, kuma yara 500,000 sun samu ilimin boko a jihohin Borno da Yobe.
“Duk da haka, duk da waɗannan yunƙurin, ƙalubalen ya ci gaba ne kawai yadda yara 3 cikin yara 10 a Borno, Yobe, da Adamawa aka yi musu rajistar haihuwarsu. Duk da haka, kusan yara miliyan 2 ba sa zuwa makaranta a Arewa maso Gabas, wanda ke nuna buƙatar halin gaggawa na jin ƙai da ci gaba”.
Lamarin da ya ce ya ƙara dagulewa da matsalar ilimi, inda kashi 72 cikin 100 na ɗaliban da suka kammala firamare a yankin ba su iya karatu da rubutu ba, wadda wannan yana nuna babbar gazawa wajen ba da ilimi a matakin farko, kuma yana nuna buƙatar shiga lamarin cikin gaggawa.
UNICEF ta ci gaba da jajircewa wajen yin aiki tare da gwamnatoci da abokan hulɗa domin magance waɗannan ƙalubale.
Haka nan hukumar ta sadaukar da dala miliyan 270 don bayar da agajin jin ƙai da kawar da fatara a Najeriya, inda ta mayar da hankali kan ilimi da lafiya da kuma kariya ga yara masu rauni.