“Babu shakka cewa INEC na fuskantar matsin lamba mai tsanani, daga mambobin APC da sauran abokan huldarsu wadanda ke tsoron TNN, domin sun shirya yin magudi a zaben 2027 wajen samun nasararsu.

“Amma muna kira ga INEC da ka da ta bayar da kai bori ya hau a matsayinta na hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa tare da kare mutuncnta ta hanyar kin yin abin da ya saba wa doka.

 

“Muna tunatar da hukumar INEC cewa ‘yan Nijeriya suna sa ido sosai kan yadda za ta magance wannan batun na TNN, kuma duk abin da za ta yi zai tantance ko ‘yan Nijeriya za su iya dogaro da ita don shirya sahihin zabbe mai cike da adalci a 2027,” in ji sanarwar.

Ya kuma ce, “Idan aka yi la’akari da siyasar da ta riga ta wuce gona da iri gabanin zaben 2027, mun yi imanin INEC ba za ta yi wani abu da zai kara ta’azzara lamarin ba”.

Ya bukaci INEC da ta bi ka’idojinta da kuma kundin tsarin mulkin tarayyar Nijeriya, wanda hakan zai ba da damar kungiyarsa ta yi rajista a matsayin jam’iyyar siyasa daidai da dokokin kasar da kuma yin takara a dukkan matakai daga kananan hukumomi a babban zabe mai zuwa.

A halin da ake ciki, TNN ta yi kira ga dukkan magoya bayanta su kwantar da hankulansu kan batun yin rajista.

“Mun san cewa da yawa daga cikin magoya bayanmu masu yawa sun fusata da rahoton matsin lambar da ake yi wa INEC kan wannan batun. Amma dole ne su ci gaba da bin doka da oda yayin da muke jiran hukuncin INEC.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Za a kwaso ’yan Nijeriya 15,000 da ke gudun hijira a ƙetare

Gwamnatin Nijeriya ta ce tattaunawa ta yi nisa domin kwaso ’yan ƙasar guda 15,000 da suke gudun hijira a ƙasashen Kamaru da Nijar da Chadi da wasu ƙasashen cikin mutunci.

Kwamishinan hukumar kula da ’yan gudun hijira ta Nijeriya, Alhaji Tijjani Ahmed ne ya bayyana haka a zantawarsa da manema labarai a Abuja.

Matakan da gwamnonin Arewa suke so a ɗauka kan matsalar tsaron yankin An kama matashi da kawunan mutanen a Legas

Ya ce akwai aƙalla ’yan Nijeriya miliyan shida da ke zaman gudun hijira a cikin ƙasar, sannan akwai wasu dubbai da suke zaune a wasu ƙasashen na duniya.

“Akwai ’yan Nijeriya 15,000 da suke so su dawo da kansu; haka kuma muna da ’yan ƙasashen waje aƙalla 100,000 da suke zaman gudun hijira a ƙasar nan.

“Dukkan mutanen nan suna da alhaki a hukumarmu na ba su kulawar da ta dace,” in ji shi.

Ahmed ya yi godiya ga Shugaban Bola Tinubu bisa gudunmuwar da yake ba ma’aikatar jinƙai, sannan ya nanata ƙudurinsu na tabbatar da kwaso ’yan ƙasar da ke zaune a wasu ƙasashen.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Zamfara Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Kula Da Aikin 2025 Domin Kyautata Jin Dadin Alhazan Jihar 
  • Minista Ya Ƙaddamar Da Yekuwar Wayar da Kan Ɗalibai Kan Kafofin Sadarwa
  • Nijeriya Za Ta Karɓi Baƙuncin Taro Karo Na 4 Na Ƙananan Sana’oi Na Ƙungiyar AU
  • 2027: Har Yanzu Ba Mu Saka Ranar Fara Sabunta Katin Zabe Ba — INEC
  • Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan El Classico Na Yau
  • Putin  Na Rasha Ya Gana Da Shugabannin Afirka Akan Batun Tsaro
  • Za a kwaso ’yan Nijeriya 15,000 da ke gudun hijira a ƙetare
  • Bayan Cin Kamfanin META Tarar Dala Miliyan 220: Sun Yi Bazaranar Katse Kafofin Facebook, WhatsApp, Da Instagram A Nijeriya
  • Yemen Tana Bukukuwan Samun Nasara Kan Amurka Kuma Zata Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Gaza