Masan sun ƙalubalanci sojoji kan maharan ƙasashen waje
Published: 9th, May 2025 GMT
Masana harkokin masana tsaro sun nuna rashin amincewarsu da iƙirarin sojojin Najeriya cewa baƙi daga ƙasashen waje ne ke kai yawancin hare-haren da ake kaiwa al’ummomin ƙasar, musamman a jihohin Filato da Benue.
Wannan ƙalubalen ya fito ne bayan wata sanarwa da Hedikwatar Tsaro ta yi a ranar Alhamis, cewa yawancin hare-haren da ake kai wa manoma da kashe-kashe a sassan kasar, makiyaya ne ’yan kasashen waje suka fi aikatawa.
Daraktan Ayyukan Yada Labarai na Tsaro, Manjo-Janar Markus Kangye, ya bayyana haka ne lokacin da yake amsa tambayoyin manema labarai game da hare-haren a kan manoman.
An kashe mutane da yawa tare da raba wasu dubbai da gidajensu a jihohin Filato da Benue a sakamakon hare-hare da makiyaya ɗauke da makamai suka kai a kwanakin baya.
Manjo-Janar Kangye ya ce duk da cewa ana magana da Hausa a sassa daban-daban na Afirka, amma abu mai sauƙi ne a gane waɗanda ba ’yan Najeriya ba ne. Ya ce, “idan aka ji su suna magana, za a iya gane ’yan ƙasa ne ko baƙi.”
Ya bayyana cewa sun kama wasu daga cikin ’yan ta’addan, kuma yadda suke magana da kamanninsu da ma gashin kansu, yana nuna cewa ba ’yan Najeriya ba ne.
Y amince cewa yawancin masu aikata ta’addanci a Najeriya baƙi ne, duk da cewa akwai ’yan ƙasar a cikinsu. Ya ƙara da cewa yawancin tashin hankalin da ake ji a wasu sassan ƙasar nan, galibi waɗanda suka shigo ƙasar ta bayan fage ne ke aikata su.
Ya yi kira ga hadin gwiwa tsakanin hukumomin tsaro don tabbatar da an yi ɗauki bayanan duk wanda ya shigo Najeriya.
Masana sun ɗiga ayar tambayaSai dai, wasu masana tsaro sun nuna shakku game da wannan iƙirarin.
Dakta Kabiru Adamu, Shugaban Kamfanin Beacon Consult, ya amince cewa sojojin Najeriya suna fuskantar matsin lamba sosai saboda ƙaruwar hare-hare da kuma yadda ake bibiyar su daga kafafen yada labarai da manyan jami’an gwamnati.
Ya ce wannan matsin lamba zai iya shafar ƙarfin guiwar sojoji da kuma yadda suke gudanar da ayyukansu, wanda zai iya kai su ga bayar da irin wannan sanarwa don nuna cewa suna samun ci gaba tare da ɗora alhakin ga wasu.
Ya yi nuni da yarjejeniyar ECOWAS kan zirga-zirgar dabbobi da makiyaya, yana mai cewa duk da manufarta ta sauƙaƙa zirga-zirga, ana ganin ta a matsayin hanyar da ’yan bindiga za su iya shigowa kasar ba tare da an san su ba.
Kabiru Adamu ya yi kira da a sake duba yadda ake aiwatar da wannan yarjejeniya tare da samar da hanyoyin da za a iya bibiyar masu shigowa ƙasar.
Ya kuma jaddada matsalar iyakar Najeriya da ba ta da tsaro, yana mai kira da a inganta haɗin gwiwa da ƙasashe makwabta tare da saka hannun jari a yankunan kan iyaka.
Wani tsohon kwamandan sojin sama, Dakta Musa Salmanu, ya ce zai ɗauki maganar kakakin hedikwatar tsaro da muhimmanci, amma ya nuna damuwa cewa idan ’yan kasashen waje ne ke kai hare-haren, hakan na nufin Najeriya na fuskantar wani nau’i na mamayewa.
Ya yi tambayoyi game da ko waɗannan mutane ne suka zo da kansu ko kuma wasu ƙasashe ne ke ɗaukar nauyinsu.
Ya jaddada cewa ko ’yan Najeriya ne ko baƙi, babban abin da ya kamata a fi mayar da hankali a kai shi ne yadda za a dakatar da barnar da suke yi.
Ya kuma yi kira da a magance tushen matsalar rikicin makiyaya da manoma da sauran matsalolin tsaro a sassan Najeriya.
Wani tsohon ɗan majalisa, Destiny Enabulele, ya zargi shugabannin Najeriya da rashin jajircewar magance matsalar rashin tsaro.
Ya yi tambaya game da yadda ake kashe kuɗaɗen da aka ware don tsaro, yana mai cewa har sai an samu jajircewar yaƙar rashin tsaro, ba za a samu mafita ba.
Ya kuma yi kira ga jami’an shige da fice da na kwastam da su koma kan iyakokin kasar don gudanar da ayyukansu yadda ya kamata.
Wani masanin tsaro, Jackson Lekan Ojo, ya musanta iƙirarin sojojin, yana mai cewa hakan ya nuna gazawar hukumomin iyaka da na leƙen asiri na ƙasar.
Ya ce ya kamata a hukunta waɗanda ke da alhakin tsaron iyakokin Najeriya, yana mai bayyana ikirarin a matsayin “uzuri maras tushe,” da ke nuna halin ko-in-kula na sojoji da sauran jami’an tsaro.
Ya yi kira da a fatattaki waɗannan mutane, a kama su ko kuma a mayar da su kasashensu.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: yan ta adda hare hare Makiyaya Tsaro
এছাড়াও পড়ুন:
Yadda Ƴan Agbero’ Ke Cin Karensu Ba Babbaka A Abuja
Abdulahi, wanda ke jigilar kaya daga Agbara a Jihar Ogun zuwa Ibadan, ya ce yana kashe har Naira 25,000 a kowace tafiya da yake yi, inda mafi yawan kuɗin ke shiga hannun ƴ an Agbero a Legas, waɗanda ke gudanar da ayyukansu sa’o’i 24 a rana, kwana 7 a mako.
Ya ce daga Berger, gefen Legas, zuwa Agbara, manyan motoci kan gamu da aƙalla tashoshi 15 na ta’annati, inda ake karɓar kuɗi tsakanin Naira 1,000 zuwa Naira 3,000 a kowane wuri.
Manajan Daraktan wani kamfani da ke aiki a cibiyar masana’antu ta Agbara a Jihar Ogun, wanda ya nemi a sakaya sunansa ba, ya shaida wa wannan jarida cewa jigilar kwantena na kayayyakin masarufi daga tashar jiragen ruwa ta Apapa a Legas zuwa Agbara na iya kaiwa har Naira 700,000, sakamakon ayyukan waɗannan ƴ an Agbero da ba su da izinin doka.
Babu shakka, waɗannan kuɗaɗen ana sauke su ne kan masu sayen kayayyakin da kamfanonin masana’antu ke samarwa.
Haka nan, fasinjoji na jayayya cewa nauyin kuɗin da aka ɗora wa direbobi a ƙarshe ana sauke shi ne a kan su ta hanyar ƙarin kuɗin haya.
“Kuɗin haya na tashi kullum, kuma wani ɓangare na matsalar waɗannan kuɗaɗen haramtattu ne,” in ji Chidinma Okafor, wata fasinja da ke zama a Legas.Ga wasu direbobi ma, cin zarafin ya wuce batun kuɗi. “Idan ka ƙi biyan kuɗi, za su fasa gilashin motarka ko kuma su cire madubin gefe,” in ji Sani Mohammed, direban Abuja. “Ya zama kamar muna yi musu aiki ne, ba wai don kanmu ba.”
A Fatakwal kuwa, fasinjoji na cewa rashin tsaro na zama babban ƙalubale. “Tashoshin motoci cunkushe suke kuma waɗannan ƴ an Agbero na tsoratar da fasinjoji ma,” in ji wata ɗaliba, Amara Nwankwo.
Ta ƙara da cewa: “Ba ka da tabbacin ko adadin kuɗin da kake biya shikena, ko kuma ana tilasta maka ka biya ƙarin kuɗi.”
A Legas kuwa, matsalar ta fi tsananta. Wani shugaban ƙungiya a Legas, da ya nemi a sakaya sunansa, ya ƙiyasta cewa ƴ an Agbero suna tara sama da Naira biliyan 100 a duk shekara daga harajin da ba na doka ba da suke ƙaƙaba wa direbobi a Legas.
Masu ruwa da tsaki na cewa waɗannan kuɗaɗe ba sa komawa wajen inganta ababen more rayuwa ko samar da ayyuka.
Masana suna gargaɗi cewa ƙara yawaitar wannan rashin gaskiya na da illa ga tattalin arziki da kuma zamantakewa.
“Ayyukan ƴ an Agbero da ba a sarrafa su ba suna hana zuba jari na doka a fannin sufuri, suna ƙara taɓarɓarewar tsaro a tashoshin motoci, sannan suna ƙara tsadar rayuwa ga talakawan ƴ an Nijeriya,” in ji tsohon ƙaramin ministan harkokin sufuri a wani taron masu ruwa da tsaki, Prince Ademola Adegoroye.
“Gwamnati dole ta matsa zuwa ga tsari na doka da kuma inganta tafiyar da harkokin tashoshin mota idan ana son wannan ɓangare ya bayar da gagarumar gudummawa ga tattalin arzikin ƙasa,” in ji Dr. Feliɗ Echekoba, masanin tattalin arziki daga Jami’ar Nnamdi Azikiwe.
Ƙungiyoyin farar hula ma sun yi kira da a yi gyara. Bisa ga Centre for Justice and Peace, wata ƙungiya mai zaman kanta (NGO), tsarin karɓar haraji ta hanyar da ba ta doka ba na rage amincewar jama’a da hana gaskiya ta bayyana a fili.
“Idan hukumomin gwamnati suka ɗauki nauyin karɓar kuɗaɗen kai tsaye, hakan zai rage satar kuɗaɗe, ya inganta gaskiya da riƙon amana, tare da kare direbobi daga cin zarafi da tsangwama a kullum,” in ji ƙungiyar a cikin wata sanarwa.
Kuma jami’an tsaro sun amince cewa tsarin yana jawo ruɗani. “A lokuta da dama muna kama direbobi saboda laifukan hanya, amma idan ka duba sosai, da yawa daga cikinsu waɗanda ne aka zalunta da haraji na ƙarya ne daga hannun ƴ an Agbero,” wani babban jami’in ƴ ansanda a Legas ya shaida wa wakilinmu cikin sirri.
Ya ce wannan shi ne dalilin da ya sa ake yawan ganin tashin hankali a kan tituna.
Ƙungiyoyin direbobi, duk da sun amince da ƙalubalen, sun dage cewa yin doka da tsari kan harkokin ne ya dace fiye da kawar da ayyukansu baki ɗaya.
“Ina buƙatar kulawa ta musamman daga gwamnati domin a tabbatar da cewa an daidaita haraji kuma ana bayar da rasit. Ta haka ne direbobi za su san ainihin abin da suke biya, kuma fasinjoji ba za su ɗauki nauyin biyan kuɗaɗen da ba su dace ba,” in ji Sunday Ogunleye, wakilin ƙungiya a Ota, Jihar Ogun.
Haka kuma, talakawa ma suna bada ra’ayinsu. “Ya kamata gwamnati ta ƙirƙiro tsarin tikitin zamani irin na e-payment a tashoshin motoci, kamar yadda ake da shi a BRT na Legas. Idan aka yi haka, direbobi da fasinjoji za su samu cikakken bayani, kuma babu wanda zai iya karkatar da kuɗi ba bisa ƙa’ida ba,” in ji Maryam Dennis, ma’aikaciyar gwamnati a Fatakwal.
Yayin da al’amarin ke ƙara ta’azzara, ƴ an Nijeriya da dama suna kira ga gwamnati ta tarayya da ta jihohi su ɗauki mataki ta hanyar samar da manufofi bayyanannu, tsarin tikitin zamani, da kuma tsauraran matakai kan karɓar kuɗaɗen haram.
A halin yanzu, direbobi da fasinjoji suna cewa wannan harajin na tilas ya zama abin da suke fuskanta kullum, wanda ke ci gaba da raunana rayuwarsu tare da tsananta matsalar tsadar rayuwa a faɗin ƙasar.
Abuja
Ko’ina ka juya, musamman a tashoshin motoci da aka fi sani a tsakiyar birni da unguwannin FCT, sawa’un direba ne kai ko fasinja, ɗaya daga cikin abubuwan da ake yawan gani shi ne ƴ an Daba, da aka fi sani da ‘Agbero’. Suna tsangwamar masu motoci da suke amfani da hanyoyi, suna karɓar kuɗaɗe Agberon-Agberon ba tare da wani tsari daga hukumomin gwamnati ba.
Ko a Gadar Mabushi, Gadar Baneɗ, shatale-talen Berger, Jabi, Gadar Area 1, Area 3 Junction ko Gwarinpa, yanayin iri ɗaya ne, yayin da ƴ an Agbero ke ci gaba cin karensu ba babbaka. A ƙasar da ke fama da laifuka da matsalolin tsaro irin su sace-sace, ƴ an bindiga, da ta’addanci, yawancin mazauna FCT suna ƙara fuskantar tashin hankali game da tsaron jama’a.
Alal misali, wani mai motar da ke ƙoƙarin ɗaukar abokin aikinsa ko ɗan uwansa a kan hanyarsa ta zuwa aiki ko dawowa daga aiki, yana cikin tsoro na tsangwamar ƴ an ‘Agbero’, waɗanda ke neman “bayanan motoci” ko wasu kuɗaɗen haram kafin a ba shi damar ɗaukar wanda yake so.
Duk abubuwan da suke yi ya saɓa doka, kuma hakan na iya haifar da barazanar da za ta bayu izuwa fashewar tayoyi ko kama mutum ba bisa ƙa’ida ba zuwa “ofishinsu.” Har ma ƴ an Agbero suna da gadarar bincikar direbobi su basu wasu takardu mallakinsu, tikitin biyan kuɗin haraji ko katin shaida kafin su yi tuƙi a kan titunan FCT.
Hatta masu motocin da ba na haya ba na ƙashin kansu ko ma’aikatan gwamnati da ke ƙoƙarin samun na cefane idan za su ɗauki fasinjoji don taimakawa kansu sayen mai ba a barsu a baya ba, saboda ƴ an Agbero na takura musu, suna neman a biya su wasu kuɗaɗe; in ba haka ba, direbobi da motocinsu ba za su bar su su wuce lafiya ba.
Abin lura a nan shi ne, yawancin mazauna na zargin wasu jami’an ƴ ansanda masu karɓar cin hanci da haɗa kai da ƴ an Agbero wajen tsangwamar direbobi yayin da suke aiki ba tare da la’akari da wanda abin ya shafa ba. Ba a cika kama su ba, yayin da duk wani Agbero da aka kama a cikin lokaci kaɗan ƴ ansanda ke sakin sa, wanda hakan ke ƙara ƙarfin gwiwar ayyukansu na miyagun laifuka.
Mummunan Al’amarin da ya afku a Mabushi
Kimanin ƙarfe 1:30 na ranar wata Laraba, 3 ga Satumba, wani mummunan lamari da ya shafi wani iyali ya faru ƙarƙashin gadar Mabushi a Abuja. Wani mutum, mai suna Emeka Ehekweme, tare da matarsa, yana tuƙa wata Toyota Highlander mai launin toka, mai lambar rajista ABJ 206 EC, lokacin da ƴ an Agbero uku da ba a tantance ba suka firgita su da wasu mutane.
Ana zargin cewa ƴ an Agberoran sun tilasta lallai sai sun shiga gaban motarsa, inda ɗaya daga cikinsu ya yi ƙoƙarin kama sitiyarin motar. Sakamakon haka, kan motar ya ƙwace motar ta tafi ta buge wata Mazda da aka ajiye a gefen hanya, ta sake dukan ginin gada sannan ta faɗa rami, hakan ya faru a kan babbar titin Nnamdi Azikiwe.
A cewar mai magana da yawun ƴ ansanda ta FCT, Josephine Adeh, lamarin ya yi sanadiyyar mutuwar mutane da dama yayin da direban Highlander, matarsa da wasu biyu daga cikin masu kai farmaki suka rasu a Asibitin ƙasa, yayin da wani wanda ake zargi na uku ke karɓar magani a halin yanzu. Direban Mazda ɗin Suleiman Mohammed, bai ji rauni mai haɗari ga rayuwa ba.
Sakamakon haka, mazauna wurin da suka fusata sun bi ƴ an Agberoran uku, suka kashe su nan take tsaye sannan suka ƙone su. Ana zargin cewa ƴ an Agberoran na daga cikin Abuja Municipal Area Council (AMAC) ne.
Lamarin ya jawo damuwa a bainar jama’a kan ayyukan ƴ an Agbero a Abuja, inda yawancin mazauna ke kiran gwamnati da ta ɗauki mataki na gaggawa don dakile tsangwama a tituna da kuma tsaurara dokokin hanya.
Koke
A yayin da take magana da wakilinmu, wata ma’aikaciyar gwamnati, Ruth Ayodele, ta ce ƴ an Agbero sun mamaye FCT kuma hukumomi ne ya kamata su ɗauki mataki a kansu. Ta yi ƙorafi cewa jami’ai ba sa aikinsu kamar yadda ya kamat.
Ta ce: “Idan aka duba abin da ya faru kwanan nan a Mabushi, inda wasu ma’aurata da wasu Agbero biyu suka rasa rayukansu, abin mamaki ne cewa har yanzu ba a bayar da sanarwar hukuma ta haramta ayyukansu a FCT ba.
“A ƙasa mai aiki haka, irin wannan lamari zai sa a ɗauki mataki cikin gaggawa. Alal misali, Jihar Anambra ta riga ta haramta ayyukan Agbero saboda yadda suke gudanar da ayyukan da suka saɓa wa al’umma.
Gwamnati ta basu damar samun ayyukan yi, matuƙar sun yi rajista da hukumomin ƙananan garuruwa. A bi hanya madaidaciya domin magance matsalar a maimakon a zuba musu ido. Wannan lamari abin takaici ne sosai.”
“Ƴan Agbero suna ko’ina, suna addabar masu motoci. Yanayin na ƙara fitowa daga iko kuma yana buƙatar kulawar gaggawa daga hukumomi domin kauce wa ƙarin asarar rayuka da dukiya, kamar abin da ya faru a Mabushi,” in ji wata ma’aikaciyar gwamnati.
Haka kuma, wani likita, Jacob Nnaemeka, ya ce sau da dama ƴ an Agbero suna tsangwamarsa yayin da yake ɗaukar ko sauke da abokan aikinsa, inda ya buƙaci hukumomin da abin ya shafa su dubi lamarin.
Ya ce: “Kowa ya san cewa ƴ an Agbero na tsangwamar fasinjoji a FCT. Ni ma na ta zama wanda abin ya shafa a lokuta da dama. A wata rana ta musamman, ina son ɗaukar abokin aikina a Area 1. Kafin na yi wata-wata, ƴ an Agbero sun shiga motata sun fara ƙoƙarin cire min makulli. Na tambaye su menene matsalar, sai suka ce ina ɗauka da ajiye da fasinjoji; kuma dole sai na biya su.”
“Bayan na nuna musu katin shaidar PCRC na, sai suka bar ni in tafi tare da neman afuwa. Amma duk haka sai da basu Naira 1,000. Tun daga wannan lokaci, na yi matuƙar taka tsantsan kuma sau da yawa ba na ɗauka ko ajiye abokan aiki, maƙwabta ko ƴ an uwa.
“A kwanakin nan, idan na yanke zan ɗauku abokin aikina sai na yi nisan daga tashar su sannan na tsaya, saboda ko’ina suna nan. Suna da ɗaurin gindi, don haka ne suke nuna halayyar rashin tarbiya.”
Nnaemeka ya ci gaba da cewa: “Ko da ka yi tunanin taimaka wa wani don ka ɗauke shi kyuata ba za ka iya ba saboda tsoron ƴ an Agbero. Yanayin ya wuce gona da iri. Haƙiƙa gaskiya ne cewa wasu jami’an ƴ ansanda na aiki tare da su; in ba haka ba, ba za su yi ƙarfin hali su riƙa takura wa mutane ko’ina a FCT ba.”
“Abin da ya faru a Mabushi bai hana su aiki ba, domin har yanzu suna gudanar da ayyukansu a sassa Agberon-Agberon na birni. Lallai abin takaici ne a FCT; hukumomi dole ne su duba wannan lamari.”
“Suna da iyayen gida”
A yayin da yake magana da Blueprint Weekend, Shugaban Police Reform Secretariat, Farfesa Olu Ogunsakin, ya ce shi ma sau da yawa ƴ an Agbero sun farmake shi a FCT. A cewarsa, suna da masu goya musu baya kuma jami’an ƴ ansanda sun san wannan matsala.
Ya ce: “Zan iya ba ku dalilai da dama kan wannan, amma abu ɗaya da ya kamata ku fahimta shi ne na yi aiki a fannin ƴ ansanda na tsawon shekaru da dama. Ni ba jami’in ƴ ansanda bane, don haka ba zan yi magana kan ayyukansu na gudanarwa ba.
Amma a matsayina na mai gudanarwa, wannan wani abu ne da zan iya gaya muku wanda ba sirri ba ne a gare su.
“Suna sane da wannan, kuma ba zan faɗa muku ko suna aiki a kai ko a’a ba, amma ina tabbatar muku cewa su ne ke da alhakin tsaron FCT kamar yadda suke da alhakin tsaro a ko’ina.”
Ya ƙara da cewa: “Idan kuka tambaye ni ra’ayi na na kaina a matsayin ɗan ƙasa, zan ce dole ne mu duba tsarin da ke cikin FCT. Wannan saboda lokaci-lokaci, ina tuƙa Hiluɗ ko I-Luɗury kamar yadda suke kiransa, kuma ina fuskantar farmaki daga mutane da dama. Suna tambayar bayanai, haƙiƙa, akwai yawan hukumomi Agberon-Agberon, da kayan aiki Agberon-Agberon, waɗanda wataƙila suna da masu goyon baya a wani wuri.”
“Al’amari game da tsaron jama’a abu ne mai matuƙar rikitarwa, musamman ganin abin da na fuskanta. Ba abu ɗaya ne zai iya bayyana ba. Akwai dubban dalilai da za su iya amsa wannan tambaya. Amma a kaina, ina da tabbacin suna aiki a kai.
“Amma ɓangaren gyaran tsari game da haƙƙin mutane, lallai a wannan fannin akwai wasu ƴ an ƙasa na musamman. Ra’ayina shi ne cewa ƴ ansanda dole ne su kasance suna ɗaukar mataki. Muna da kwamishinan FCT, muna da DCP mai kula da ayyuka, kuma muna da sashen gudanarwa, doka za ta iya ɗaukar mataki kan kowa. Idan ka yi magana da ƴ ansanda yanzu cewa za su yi akwai wani aiki na musamman da ake yi wanda ba za su iya tattauna shi ba.”
Hukumar Ƴansanda ta FCT na Kaucewa ba da Bayanai
Duk ƙoƙarin da aka yi don samun martanin Hukumar Ƴansanda ta FCT kan matsalar ƴ an Agbero a FCT ya ci tura, yayin da PRO, Josephine Adeh, ta ƙi amsa tambayoyin da ke neman ra’ayin ƴ ansanda a kai.
Bayan karanta saƙonni da dama da wakilinmu ya aika mata a ranar Talata da safe ta WhatsApp ɗinta da aka sani game da batun, ba ta amsa ba, ko da lokacin da wakilin ya kira ta lokaci-lokaci, ta ƙi amsa kiran, kuma har lokacin rubuta wannan rahoto ba ta ce komai ba.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp