Mutum 2 sun shiga hannu zargin yi wa ƙananan yara fyaɗe a Gombe
Published: 14th, May 2025 GMT
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Gombe, ta cafke wasu maza biyu bisa zargin yi wa ƙananan yara mata fyaɗe a lokuta daban-daban a jihar.
Kakakin rundunar, DSP Buhari Abdullahi ne, ya bayyana hakan cikin wata sanarwa, inda ya ce sun kama wani mutum mai shekara 47, da zargin yi wa ‘yar matarsa mai shekara biyu fyaɗe a Tudun Wada, Shamaki a ranar 5 ga watan Mayu.
Bayan samun rahoton daga matarsa, rundunar ’yan sandan ta garzaya gidansu inda ta kama wanda ake zargin, sannan suka kai yarinyar Asibitin Ƙwararru na Gombe domin duba lafiyarts.
Ya ce za a yi amfani da rahoton binciken asibitin a kotu.
Hakazalika, an kama wani mutum mai shekara 35 da ke unguwar Golkos a Ƙaramar Hukumar Billiri, bisa zargin yi wa wata yarinya ’yar shekara shida fyaɗe a unguwar Awai.
Mahaifiyar yarinyar ce ta rahoton faruwar lamarin, inda ’yan sanda suka kama wanda ake zargin, sannan suka garzaya da da yarinyar Asibitin Kaltungo domin duba lafiyarta.
DSP Abdullahi ya ƙara da cewa rundunar ta kama wasu mutane 18 daban da ake zargi da aikata laifuka daban-daban a faɗin jihar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda fyaɗe yara zargi zargin yi wa
এছাড়াও পড়ুন:
Tirela ta afka cikin kasuwa ta kashe mutum da raunata 5 a Taraba
Aƙalla mutum ɗaya ne aka tabbatar da mutuwarsa tare da wasu biyar suna jinya bayan da wata babbar mota ƙirar tirela ta ƙwace ta kutsa cikin kasuwar Mile Six da ke Jalingo babban birnin Jihar Taraba.
Shaidun gani da ido a wurin sun bayyana cewa, duk ƙoƙarin da direban motar ya yi na hana afkuwar lamarin ya ci tura.
Ƙudan zuma ya tarwatsa ɗaliban da ke jarrabawar NECO ’Yan sanda sun kama ɓarayi 5, sun ƙwato kuɗi da makamai a GombeAƙalla motoci biyu ne suka yi mummunan lalacewa a lamarin.
Jami’an Hukumar kiyaye haɗurra ta ƙasa (FRSC) da hukumar tsaro ta farin kaya sibil defens (NSCDC) da kuma rundunar ’yan sandan Najeriya (NPF) sun halarci wurin da jajantawa yankin tare da kawar da ababen hawa don kaucewa sake aukuwar lamarin.
Ɗaya daga cikin manyan motocin da suka tunkari wurin domin wucewa ta hanyar an yi ta jifan su da duwatsu.
Wannan dai shi ne ibtila’i na biyu da ya shafi manyan motocin dakon kaya a yankin inda na farko wata tankar dizal ce wanda ya zube bayan ta faɗi.
An dai ga wasu mutanen da ke wurin suna kuka yayin da wasu kuma suka ɗora alhakin faruwar lamarin a kan rashin ingantattun birki na motoci da ke kan hanyar zuwa kasuwar.