Mutum 2 sun shiga hannu zargin yi wa ƙananan yara fyaɗe a Gombe
Published: 14th, May 2025 GMT
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Gombe, ta cafke wasu maza biyu bisa zargin yi wa ƙananan yara mata fyaɗe a lokuta daban-daban a jihar.
Kakakin rundunar, DSP Buhari Abdullahi ne, ya bayyana hakan cikin wata sanarwa, inda ya ce sun kama wani mutum mai shekara 47, da zargin yi wa ‘yar matarsa mai shekara biyu fyaɗe a Tudun Wada, Shamaki a ranar 5 ga watan Mayu.
Bayan samun rahoton daga matarsa, rundunar ’yan sandan ta garzaya gidansu inda ta kama wanda ake zargin, sannan suka kai yarinyar Asibitin Ƙwararru na Gombe domin duba lafiyarts.
Ya ce za a yi amfani da rahoton binciken asibitin a kotu.
Hakazalika, an kama wani mutum mai shekara 35 da ke unguwar Golkos a Ƙaramar Hukumar Billiri, bisa zargin yi wa wata yarinya ’yar shekara shida fyaɗe a unguwar Awai.
Mahaifiyar yarinyar ce ta rahoton faruwar lamarin, inda ’yan sanda suka kama wanda ake zargin, sannan suka garzaya da da yarinyar Asibitin Kaltungo domin duba lafiyarta.
DSP Abdullahi ya ƙara da cewa rundunar ta kama wasu mutane 18 daban da ake zargi da aikata laifuka daban-daban a faɗin jihar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda fyaɗe yara zargi zargin yi wa
এছাড়াও পড়ুন:
NAJERIYA A YAU: Yadda Damina Ke Shafar Masu Ƙananan Sana’o’i
More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba
Damina lokaci ne da ɗan Adam yake matuƙar bukata. Da za ta yi jinkiri, sai a ga hankalin kowa ya tashi.
A lokaci guda kuma, yadda damina kan hana wasu harkoki gudana kan jefa wasu mutane cikin wani irin yanayi.
NAJERIYA A YAU: Shekara nawa shugabanni ke bukata don cika alkawuran zabe? DAGA LARABA: Me Ke Sa Matasa Zama Karnukan Farautar ‘Yan Siyasa A Kafafen Sadarwa Na Zamani?Shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne a kan yadda damina kan shafi rayuwar ƙananan ’yan kasuwa da masu ƙananan sana’oi.
Domin sauke shirin, latsa nan