Ministan harkokin wajen kasar Iran yayi tsokaci kan hasashe game da kusancin cimma yarjejeniyar nukiliyar da ke gudanarwa tsakanin Amurka da Iran

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya jaddada cewa: Hanyar diflomasiyya tana bukatar a dage dukkan takunkumai da aka kakabawa Iran da kuma mutunta hakkin mallakar makamashin nukiliyar Iran, yana mai cewa: Hanyar cimma yarjejeniya ta ta’allaka ne ta kan teburin tattaunawa, ba ta hanyar kafafen yada labarai ba.

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya fada a jiya Alhamis cewa: Kafafen yada labarai na yada jita-jita game da yarjejeniyar da ake shirin kullawa tsakanin Iran da Amurka.

Araqchi ya ci gaba da yin tsokaci a shafinsa na Twitter a dandalin Twitter, inda ya ce: “Muna shakkar cewa an kai wannan matakin.”

Ya kara da cewa: “Hanyar yarjejeniya tana bi ta kan teburin tattaunawa ne, ba ta hanyar kafafen yada labarai ba.”

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Shekaru 6: Don amfanin matasa mun inganta ilimi da noma — Gwamna Buni 

A bikin cikarsa shekaru 6 cur yana mulkin Jihar Yobe, Gwamnan jihar Mai Mala Buni da aka gudanar a ranar Alhamis ɗin da ta gabata ya bayyana irin gagarumin ci gaban da aka samu akan harkokin ilimi da noma, inda ya ce akasarin waɗanda suka amfana a waɗannan fannoni guda biyu matasa ne.

Da yake jawabi a yayin wannan taro na bikin cikarsa shekaru 6 akan mulki da aka gudanar a babban ɗakin taro na Banquet da ke gidan gwamnatin Jihar a garin Damaturu tare da ma su ruwa da tsaki na Jihar.

An gano gawar direba a cikin mota a Bayelsa Mutanen da suka mutu a ambaliyar Neja sun ƙaru zuwa 88 —NSEMA

Gwamnan ya bayyana ƙudirinsa na ci gaba da inganta harkokin da suka shafi matasa da kuma sauran fannonin da tuni gwamnatinsa ta yi nisa cikinsu kamar fannonin noma, kiwon lafiya, kasuwanci, tsaro da makamantansu.

Taron wanda ofishin mai baiwa Gwamna shawara na musamman kan harkokin talabijin, Rediyo da kafafen yaɗa labarai na zamani, Dakta Ibrahim Yabani, ya shirya yadda gwamnan ya amsa tambayoyin da wasu al’ummomin Jihar haɗe da ‘yan jaridu da ƙungiyoyin farar hula daga ƙananan hukumomin Jihar 17 suka yi wanda nan take Gwamnan ke amsa musu tambayoyin da suka masa kai tsaye.

A nasa jawabin, Gwamna Buni ya jaddada cewa taimakawa matasa na da matuƙar muhimmanci wanda kamar yadda ya ambata hakan ne ya ba shi ƙarfin gwiwar ƙara inganta harkokin ilimi wanda matuƙar matasa sun samu Ilimi to kuwa batun zaman banza zai kau kasancewar da sun samu Ilimi mai amfani gwamnatin nada ƙarfin gwiwar samar musu da aikin yi ta kowace irin fuska.

Gwamnan ya ce, aƙalla gwamnatin Jihar a duk wata takan kashe zunzurutun kuɗi sama da Naira miliyan 600 wajen ciyar da ɗaliban makarantun kwana waɗanda dukkansu matasa ne kuma gwamnatinsa ta tura matasa sama da 100 zuwa ƙasar Indiya don samun horo akan karantun likita wanda a yanzu haka matasan sun kammala sun dawo Jihar har an samar musu aikin yi a asibitocin Jihar.

Kan ɓangaren noma ma haka lamarin yake domin gwamnatinsa ta samarwa matasan kayayyakin gudanar da noman zamani, wadda kuma kwalliya tuni ta biya kuɗin sabulu.

Haka nan ta ɓangare tsaro nan ma haka lamarin yake domin gwamnatin ta a kullum takan yi abin da ya dace dangane da harkokin na tsaro musamman ta wajen samarwa jami’an tsaron Jihar haɗe da na Sibilyan JTF kayan aikin da suka haɗa da motocin sintiri da sauransu don ganin an daƙile barazanar da masu tada ƙayar baya ke yi ga al’ummar Jihar.

Ta fuskar gina titunan karkara ma gwamnatinsa ba ta yi ƙasa a gwiwa ba kasancewar yana da matuƙar muhimmanci wajen harkokin inganta kasuwanci, aikin noma haɗa kan al’umma musamman a ƙananan hukumomin Potiskum da Damaturu da Nguru da Gashua da Geidam da aka gina musu hanyoyin mota don ƙara alatu a garuruwan da kuma gina hanyoyin karkara a ƙananan hukumomin Jihar.

Da yake amsa tambayoyi daga mahalarta taron, Buni ya bayyana cewa, yawan gina hanyoyin mota ba wai rage tsadar sufuri ba ne, har ma yana ƙara haɓaka tattalin arzikin yankunan gaba ɗaya ta hanyar sauƙaƙawa manoman kawo amfanin gonakinsu zuwa kasuwannin Jihar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Likitocin Iran Suna Ci Gaba Da Samun Nasara Wajen Magance Matsalar Kurmanta Da Na Bebantaka
  • Nukiliya : Iran ta kirayi mai kula da harkokin Ostiriya da ke birnin Tehran kan wasu kalamai na tsokana
  • Shekaru 6: Don amfanin matasa mun inganta ilimi da noma — Gwamna Buni 
  • Mai Ba Da Shawara Ga Jagora Ya Mayar Da Martani Ga Barazanar Trump Kan Cibiyoyin Nukiliyar Iran
  • Brazil Ta Goyi Bayan Iran Kan Hakkinta Na Mallakar Makamashin Nukiliya
  • Sin Da Kasashen Yankin Pasifik Sun Yi Nasarar Gudanar Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Karo Na Uku
  • Kasar Iran, Da Kasashen Kungiyar BRICS Sun Gudanar Da Taro Kan Harkokin Tsaro A Mosco
  •  Iran Ta Yi Watsi Da Jita-Jitar Cewa Za Ta Dakatar Da Tace Sanadarin Uranium
  • Araghchi: “Ba ma wasa game da batun inganta uranium, wanda hakkin al’ummar Iran ne”