Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci Ya Gana Da Ministan Cikin Gida Da Gwamnonim Lardunan Iran
Published: 29th, May 2025 GMT
Jagoran juyin juya halin musulunci a nan kasar Iran ya gana da ministan harkokin cikin gida da kuma gwamnonin Larduna, inda ya basu shawarar amfanin da kekyawar yanayin da kasar take ciki don ciyar da kasar Gaba.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Jagoran yana cewa, a halin yanzu kasar Iran bata fuskantan watai annoba kamar CoviD19, ko matsalar tsaro a cikin gida da sauran wanda zai hanasu aiki.
Imam Sayyid Aliyul Khaminae ya bayyana cewa kasar Iran a halin yanzu bata fuskantar wata matsala, don haka ya bukaci Gwamnonin lardun su yi amfani da wannan damar don amfani da matasan kasar wadanda suka yi karatu don bukasa tattalin arzikin kasar tare da amfani da dimbin arzikin da All..ya horewa kasar.
Kafin haka dai ministan harkokin cikin gida Eskandar Mumini ya gabatar da jawabi inda yake halin da ake cikin a ayyukan ci gaban da gwamnonin suke yi a duk fadin kasar ya kuma bayyana ire-iren ci gaban da aka samu.
Jagoran a wani wuri ya fadawa gwamnonin kan cewa suna iya amfani da kungiyoyin raya kasashen wadanda Iran take da su don kalla yarjeniyoyi da wadannan kasashen saboda ci gaban kasar Iran. Yace kungiyoyi kamar shanhai, da ECO da sauran su zasu iya taimakawa don kawo ci gaban tattalin arzikin kasar.
Sannan daga karshe jagoran ya bukaci gwamnanin su rika ciga mutane suka tambayansu matsaloli duk da cewa wani lokacin sukan hadu da wadanda zasu fada masu maganganu marasa dadi.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Jaddada Cewa: Ba Zata Taba Amincewa Da Batun Dakatar Da Sarrafa Uranium Ba
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran ya jaddada cewa: Iran ba za ta daina sarrafa sinadarin Uranium a kowane hali ba
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran Isma’il Baqa’i ya tabbatar a wata hira da tashar CNN ta Amurka cewa: Iran ba za ta taba yin watsi da hakkinta na tace sinadarin Uranium a kowane hali ba.
A yayin da yake mayar da martani game da kyakkyawan fata na shugaban Amurka Donald Trump game da shawarwarin nukiliyar da aka yi tsakanin gwamnatinsa da Iran da kuma yadda yake kallon ci gaban da aka cimma, Baqa’i ya ce: Idan manufar Amurka ita ce tabbatar da cewa shirin makamashin nukiliyar Iran ba zata yi amfani da shi wajen karfin soji ba, to yana ganin za a iya cimma hakan cikin sauki. To amma idan har Amurka tana son tauye wa Iraniyawa ‘yancinsu na samun cikakken fasahar makamashin nukiliya na zaman lafiya da lumana ne, to yana ganin hakan zai zama babbar matsala, ta yadda Iran za ta kalubalanci dukkan tsarin.
A lokacin da wakilin tashar CNN ya tambaye shi: Shin ko suna tsammanin gwamnatin Trump da mai shiga tsakaninta, Witkoff, sun gane kuma sun fahimci hakan? Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran ya mayar da martani da cewa: Kasancewar Iran tana ci gaba da tattaunawa ya zuwa yanzu tana nufin cewa ta san akwai wani matakin fahimtar da Iran ba za ta iya ba a kowane irin yanayi ta yi watsi da haƙƙinta na mallakar fasahar makamashin nukiliya na zaman lafiya da lumana da suka haɗa da inganta sinadarin Uranium.
Amurka