Kokarin Minista Tuggar Na Mayar Da Hijirar Masana Daga Nijeriya Zuwa Kasashen Waje Alhairi
Published: 31st, May 2025 GMT
Wannan shi ne babban abin alfahari da Ministan Harkokin Waje, Ambasada Yusuf Maitama Tuggar ke jagoranta. A yayin tattaunawar manyan jami’an biyu a Berlin tare da ministan harkokin wajen Jamus Johann Wadephul, Tuggar ya nuna bajinta. “Ba manufar Nijeriya bace ta fitar da mutane zuwa wasu kasashen waje ba, sai don nuna gwanayenta,” in ji shi, tare da sake sanya haske a manufinta.
A cikin shekarun baya-bayan nan, yawan al’ummar Nijeriya sun kasance ana sanya su a matsayin wadanda ke cikin rikici, miliyoyin matasa marasa aikin yi, masu karatun digiri, da kwararru an nuna musu halin ko-in-kula.
Amma Tuggar, gogaggen jami’in diflomasiyya kuma mai tunani na Afirka, yana ganin abin da mutane da yawa ke watsi da shi dama ce. Ana ganin sama da mutum miliyan 220 da muke da su a yau ana hasashen za su kai miliyan 400 nan da shekarar 2050, don haka Nijeriya ba kawai mai daukar nauyin al’umma bace, ita ce ma’adanin jari-hujja baki daya.
Sabanin haka, Jamus da yawancin Tarayyar Turai suna tsufa da wuri. Tattalin arzikinsu na karuwa, amma yawansu yana raguwa
Kwararrun ma’aikata suna cikin karancin wadata. Vangaren kiwon lafiya ya tabarbare. Masana’antu suna bukatar a karfafe su da kwarewar dijital.
To a nan akwa al’amari mai ban sha’awa: Nijeriya na da hazaka. Turai kuma na da bukata. Amma maimakon a yi asarar wannan wannan hadin gwiwa ta hanyar yanke kauna da yin hijira ba bisa ka’ida ba, Tuggar ya ba da shawarar yin doka, da tsarin hadin gwiwa, wacce za a rika yin hijrar akan tsari.
Wadephul, a nasa bangaren, wannan shawara ba wai ta kasance karbabbiya bace, ai bayan haka abar sha’ace a bayyane
A nasa jawabin, ya jaddada ingancin zurfafa hadin gwiwa tsakanin Nijeriya da Jamus a fannonin da suka hada da kasuwanci zuwa makamashi, da kuma yadda ake tafiyar da ayyuka na hazaka. “Akwai manyan damammaki a hadin gwiwa cikin ma’adanai masu mahimmanci, canjin makamashi, da hadin gwiwar kamfanoni masu zaman kansu,” in ji shi.
Jamus ba ta sanya Nijeriya cikin masu ba da taimako ga masu karba, ko mai taimako ga marasa galihu. Madadin haka, wannan hadin gwiwa ne da zai zama na masu daidaita kasashen da za su daidata bukatun juna da mutunta juna. Tuggar da Wadephul sun binciko hanyoyin zurfafa alaka ta hanyar koyar da sana’o’i, inganta kwarewa, da kirkirar hanyoyin kaura da ke mutunta ikon mallaka da samun dama.
Hadin gwiwar makamashi tsakanin Jamus da Nijeriya, wanda aka fara a 2008 kuma aka karfafa shi a 2021 tare da kafa ofishin hydrogen a Abuja, wani abin koyi ne na yadda kasashen biyu za su iya samar da darajar kayan. Yanzu dai, makasudin yin haka shi ne a sake dawo da irin wannan hadin gwiwa, karfafawa matasa, da sanya hannun jari na kasashen biyu.
A cikin manufofin waje na Tuggar, ba gwaninta bace a rika fita da kaya ta hanyar bazata ba, domin kadara ta kasa. Ya fahimci cewa idan kaura ba ta da tsari, to lallai kasashe sun yi hasara. Amma idan aka yi da kyakkwar niyya kuma ana yin mubaya’a, al’ummomi kasashe za su shigo ciki.
’Yan Najeriya kwararrun da ke aiki a Berlin, Hamburg, Munich, ko Frankfurt ba wai kawai suna cike gibin aiki bane, suna gina gadoji na kasashen waje, aika kudi, samun sabbin kwarewa, da fadada darajar Nijeriya a duniya.
Wannan ba maganar hijira ba ce kawai; wannan shi ne dabarun diflomasiyya.
Wannan tsarin ya kalubalanci ra’ayin da aka dade ana yi wanda Afirka ba ta da wani abin da za ta iya bayarwa. Akasin haka, Afirka, da Nijeriya musamman a shirye suke domin kerawa gami da ba wa duniya abin da ba ta da shi ko take rasawa.
Ayyukan Tuggar a Berlin sun fi ba da fifiko kan kiraye-kirayen girmamawa na bangarorin biyu, da suka kasance wani bangare na hangen nesa wajen sake mayar da Nijeriya a matsayin mai kwarin gwiwa, mai kwarewa wajen taka muhimmiyar rawa a fagen duniya. Har ila yau ya gana da ‘yan majalisar dokokin Jamus, da manyan jami’an raya kasa, da Farfesa Lanz Rolla, wanda shi ne mai hangen nesan da ya kafa taron tattaunawa na duniya na Berlin.
Dangane da jagorancinsa da kuma yadda Nijeriya ke tasowa, an gayyaci Tuggar a hukumance don yin jawabi a taron 2025 na Tattaunawar Duniya ta Berlin. Wannan gayyata kakkarfar alama ce.
Kuma hakan ya tabbatar da rawar da Nijeriya ta taka wajen tsara tattaunawar duniya game da mulki, da dorewa, da kuma yin hijira.
Shekaru da yawa, an yi magana game da Afirka a cikin da’irar duniya. Tuggar yana son Nijeriya ta kasance daya daga cikin masu fada a ji kuma masu jagoranci.
Lokaci ya yi da ‘yan Nijeriya a gida da waje za su daina kallon hijira a matsayin abin takaici. Ba koyaushe ne hijrar take zama tsrewa ake ba,. Wani lokaci, ana ficewa ne domin fadada ilimi. Wani lokaci, masu hijrar ba batu ne na watsar da kasarsu ba, a’a suna fita ne domin ciyar da ita kasar gaba.
Dole ne mu gina tsarin da zai ba matasa ‘yan Nijeriya kayan aiki ba kawai don yin gasa a duniya ba sai don yin nasara da alfahari, daukar su tare da girmamawa, da kuma danganta nasarar kansu ga ci gaban kasa.
Dan Nijeriya mazaunin kasar waje ai ba zama dan kasa ba. Kadara ce kawai ta ketare.
Don yin wannan aikin, dole ne gwamnati ta saka hannun jari a fannin ilimi, fasahar dijital, da horar da sana’o’i. Dole ne kuma ta sake fasalin ayyukan diflomasiyya don tallafa wa hanyoyin kaura na doka da kuma kare ‘yan kasa a kasashen waje daga cin zarafi da nuna wariya.
Amma bayan gwamnati, dole ne kowane dan Najeriya ya sake gyara tunaninsa. “Japa” ba shi ne abin kunya ba. A hannun shugabanni masu hangen nesa kamar Tuggar, ya zama dabara dabara ta hawa abin hawa mai mahimmanci ga kasa.
Kada mu yi la’akari da bin hanya daya. Mu horar da ingantattun tunani, mu samar da ginshikai masu karfi, domin gina Nijeriya a duniya wanda zai amfanar da kowa.
Nijeriya ba ta yi asarar mutanenta ba. Tana amfanuwa ta karkashin kasa.
Kuma yayin da wannan sabon babi ya bayyana-mai tushe cikin mutunci, da tsarin diflomasiyya – har yanzu muna iya gano cewa jiragen da a da suka kwashe mafarkinmu suna dawowa, ba kawai tare da fasinjoji ba, har ma da kyakkyawar manufa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Tuggar kasashen waje hadin gwiwa da Nijeriya
এছাড়াও পড়ুন:
Maƙabarta mai shekaru 500 da ta koma maɓoyar ’yan daba
Maƙabartar Kuka Bulukiya maƙabarta ce mai daɗaɗɗen tarihi a cikin ƙwaryar birnin Kano, wadda bayanai suka nuna an shafe sama da shekara 500 ana binne mamata a cikinta.
Wannan daɗaɗɗiyar maƙabarta tana da matuƙar muhimmanci musamman la’akari da yawan unguwannin da suka kewaye ta da yawan mutanen da aka binne a cikinta da kuma fitattun mutanen da suke kwance a cikinta.
Maƙabartar Kuka Bulkiya ta yi iyaka da unguwannin Dala da Madabo da Yalwa da Kwanar Taya da kuma Gwammaja, sa’annan akan kawo gawarwaki hatta daga unguwanni irin su Gwauron Dutse da Ƙulƙul da Dogon Nama da Madigawa da Sanka da Makafin Dala da dai sauran su.
Asali dai an sanya mata sunan Bulukiya ne saboda wata bishiyar kuka mai wannan sunan da take tsakiyarta. Tarihi ya nuna hatta Mujaddadi Shehu Usman ɗanfodiyo ya taɓa ziyartar maƙabartar inda ya yi wa mamata addu’a a ƙarƙashin bishiyar.
Sojoji sun kashe ɗan ta’adda da aka sa ladar N100m a kansa a Borno Mun haramta liƙa hotuna ko rubutu marasa ma’ana a A-Daidaita-Sahu —El-MustaphaMamallakin tsohon kamfanin sufurin jiragen sama na Kabo Air, Jarman Kano, Marigayi Alhaji Muhammadu Adamu Ɗankabo, ne ya katange ta sama da shekaru 25 da suka shuɗe, lokacin yana raye, kuma shi ma a nan aka binne shi.
To sai dai duk da wannan tarin muhimmancin, a ’yan shekarun nan, wani sashe na maƙabartar ya zama kamar wata mafaka ta ’yan daba, masu yin ƙwacen waya da ma aikata fashi ga masu wucewa ta kusa da ita.
Sun sace allunan kabari da ƙarafan katangar maƙabartaA yayin ziyarar da wakilinmu ya kai maƙabartar, ya gane wa idanunsa yadda aka ɓalle ƙarafan da suke jikin saman katangar, kuma an shaida masa cewa ɓata-garin ne suka sace ƙarafan. Bugu da ƙari, hatta allunan ƙarfe da ake rubuta sunan da kwanan watan rasuwar mamata a jikin ƙaburburansu, ɓata-garin ba su bari ba, sun yi awon gaba da su.
Ɗaya daga cikin masu haƙan ƙabari a maƙabartar, wanda bai amince a bayyana sunansa ba, ya shaida wa wakilinmu cewa, babbar matsalar da suke fuskanta ita ce ta tsaro, musamman la’akari da yadda ɓata-gari suke fakar numfashin masu wucewa ta kusa da ita suna yi musu ƙwace.
Ya ce akan ƙwace wa masu wucewa kuɗaɗe da wayoyi — har ma da ƙarafan da suka zagaye katangar maƙabartar. A cewarsa, “Lokacin da suka fi yin ƙwacen shi ne lokacin da sawu ya ɗauke, kamar wajen sallar Azahar saboda tsananin zafin rana, ko da daddare ko da sanyin safiya.
“Duk abin da suka samu a jikin mai wucewa daga kuɗi ko waya duk ƙwacewa suke yi. Har babur ɗin hawa an taɓa ƙwacewa a nan wajen. Galibi dai an fi yin ƙwacen nan ta ɓangaren katangar yamma, tsallaken Kwanar Taya, sai kuma nan kan titi.
“An sace yawancin ƙarafan katangar, kodayake ya ce sai da daddare suka fi zuwa ,saboda ai ba zai yiwu ido na ganin ido ba, kafin su cire wani zai gan su ya hana tun da ko ta ina akwai jama’a,” ” in ji ma’aikacin maƙabartar, wanda ya ce, ɓarayin sukan sace hatta allunan ƙaburbura, su sayar wa masu sana’ar gwan-gwan.
Ya ce adadin masu haƙar ƙabari a maƙabartar ya kai 31, amma mutum 16 daga cikinsu kaɗai ƙaramar Hukumar Dala take ba wa alawus. Amma su ma kusan wata huɗu ke nan ba a ba su ba.
Daga nan sai ya yi kira ga ƙaramar hukumar da ta dube su ta tallafa musu wajen biyan alawus ɗin.
Da muka tambaye shi ta yaya suke iya kula da iyalansu da abin da suke samu, sai ya ce galibi sai dai idan jama’a sun zo rufe mamaci sai su nemi taimako a wajensu, abin da aka samu na sadaka kuma sai su raba a tsakaninsu.
‘An ƙwace keken yaron da ya ziayrci ƙabarin mahaifiyarsa’Shi ma wani daga cikin masu aikin hakan da shi ma bai amince a bayyana sunansa ba, ya ce akwai yaron da ya taɓa zuwa ziyara kabarin mahaifiyarsa da keke, amma ɓata-garin suka ƙwace masa keken. “Haka suka ƙwace keken suka tafi suka bar shi yana kuka, sam ba su da imani,” in ji shi.
Ya ci gaba da cewa, “Ni ma akwai ranar da na zo ina aiki da safe, kawai sai na hango wani daga cikin ’yan daba ya laɓe a bayan wata bishiya a tsakiyar ƙaburbura da adda a hannunsa, sai ya yi min alamar in bar wajen za su yi wani aiki, dole haka na bar wajen tun da ba ni da makamin da ya fi nasa ballantana na hana shi.”
Ya ce da yake yawancin ɓata-garin ’yan unguwannin da ke maƙwabtaka da maƙabartar ne, sun san su a fuska, amma ba su cika yi wa masu haƙan kabarin ƙwacen ba, sun fi yi wa baƙi masu zuwa ziyara ko wucewa.
A zantawarsa da wakilinmu, shugaban masu haƙan kabari da kuma kula da maƙabartar, Malam Garba Sa’adu, wanda ya ce ya shafe sama da shekaru 40 yana aiki a cikinta. Malam Garba ya shaida masa cwea abin takaici ne yadda ɓata-garin ke zuwa har kusa da maƙabarta suna aikata ta’asa ba tare da jin tsoron Allah ba.
Sai dai ya ce yanzu an samu sauƙin sace-sacen a sakamakon hoɓɓasar da mutanen unguwa da kuma ƙungiyoyi masu zaman kansu suka yi.
Daga nan sai ya yi kira ga masu hannu da shuni da su taimaka wajen kai gudunmawar ƙasar ciko da birjin da za a yi amfani da su wajen cike wasu ƙaburburan da sukan rufta saboda ruwan damina.
Malam Garba ya kuma yi kira gare su da gwamnati da su taimaka wa maƙabartar da ma ma’aikatanta don su ci gaba da samun ƙwarin gwiwar gudanar da ayyukansu yadda ya kamata.
Wata 4 babu N5,000 da ake biyan mu a wata — Mai haƙan kabariYa kuma yi kira, musamman ga ƙaramar hukumar da maƙabartar take, wato Dala, da su taimaka wa masu aikin hakan domin kula da su.
“Ba a kula da mu da rayuwarmu yadda ya kamata gaskiya, ɗan abin da ake ba mu ƙalilan ne. A ce mutum da ’ya’ya da iyali yana bauta wa al’umma amma sama da shekaru 40 ba abin da gwamnati take yi mana. Wata huɗu ke nan yanzu ma ba a ba mu alawus ba. ɗubu hudu ce, kuma yanzu wata hudu ke nan ma ba a ba mu ba,” in ji Malam Garba.
Wani abokin aikinsa ya ce ko a kwanakin baya sun zauna da wakilan shugaban ƙaramar hukumar Dala, inda ya yi musu alƙawarin ƙarin alawus ɗin daga Naira 5,000 zuwa 10,000, amma har yanzu ba a fara aiwatarwa.
Aminiya ta tuntuɓi Ƙaramar Hukumar ta Dala don jin ta bakinta a kan batun alawus ɗin, sai dai duk ƙoƙarin wakilinmu na jin ta bakin Daraktan Ma’aikata da Gudanarwa na ƙaramar hukumar, Dauda Shehu Zakirai, ya ci tura.
Wakilin namu ya ziyarci je Daraktan amma bai same shi ba, ya kira shi a waya bai ɗaga ba, sa’annan bai amsa rubutaccen saƙon da wakilin namu ya tura masa ba, har zuwa lokacin haɗa wannan rahoton.
Ba mu sani ba, amma za mu bincika — Kwamitin maƙabartuA cewar mai magana da yawun kwamitin da aka ɗora wa alhakin kula da maƙabartu na jihar Kano, Aminu Yahaya Galadanci, babu wanda ya sanar da kwamitin nasu matsalolin Maƙabartar Kuka Bulukiya, don haka ba su san da su ba.
Sai dai ya yi alƙawarin kai ziyara maƙabartar da kansa don ganin halin da take ciki. A cewarsa, “Kwamitinmu ba shi da wakilci a kowacce maƙabartar da ke Kano, mutum 10 ne kawai a cikinsa. Ba zai yiwu a ce komai muna ciki ba, kullum buƙatarmu ga jama’a ita ce idan wani abu ya faru irin wannan su sanar da mu, sai mu bincika mu ɗauki mataki.
“Amma galibi sai dai mu ji ana ƙorafi a gidan rediyo amma ba a sanar da mu ba, duk da cewa mun bayar da lambobin waya da za a riƙa kawo mana ƙorafi. Amma dai wannan gaskiya ba mu sani ba, amma dai yau ɗin nan in Sha Allahu ni da kaina zan je na bincika domin ɗaukar matakin da ya dace,” in ji shi.