NAFDAC ta gano wajen da ake sabunta magungunan da suka lalalce a Abiya
Published: 16th, February 2025 GMT
Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta gano wani waje a Jihar Abiya da ake sake gyara da sabunta magungunan da suka lalace domin sayar wa jama’a.
A cikin wata sanarwa da ta wallafa a shafinta na Facebook.
Gwamnatin Zamfara ta haramta tarukan siyasa saboda tsaro Gwamnatin Yobe Ta Ɗauki Jami’an Kiwon Lafiya 42 AikiHukumar ta ce an gano waɗannan magunguna a wasu gine-gine da ke garin Umumeje, a Ƙaramar Hukumar Osisioma Ngwa.
NAFDAC, ta ce wannan waje yana kusa da kasuwar Ariaria a Aba, cibiyar kasuwanci a jihar.
Hukumar ta bayyana cewa ta kai samame wajen ne tare da haɗin gwiwar jami’an tsaro domin daƙile safarar jabun magunguna.
Wannan yana ɗaya daga cikin ƙoƙarin Gwamnatin Tarayya na kare lafiyar al’umma.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Abiya
এছাড়াও পড়ুন:
Ɗan Majalisar Tarayya Ya Nuna Damuwa Kan Ƙaruwar Hare-haren Ta’addanci A Sakkwato
Mataimakinsa kan harkokin majalisa Honarabul Attahiru Danmadi ne ya wakilci dan majalisar ya kuma tabbatarwa wadanda lamarin ya shafa kokarinsa kan daukar matakan da suka kamata domin tabbatar da tsaron rayukan su da dawowa da zaman lafiya a yankunan.
Garuruwan da ‘yan bindigar suka tarwatsa a gundumar Kuchi sun hada da Fakku, sha’alwashi, tulluwa da Rafin- gora a inda mutane bakwai suka rasa rai. A gundumar Jabo kuwa kauyukan da lamarin ya shafa su ne; Gesolodi, Hilya, Guraye, Guma, Chakai, Modo, Badariya, Tafki, Balera, Gudumawa da Rafin shinka.
“Mun girgiza kwarai da wannan halin da kuke ciki. A matsayina na wakilin ku, zan ci-gaba da kokarin da ya kamata a majalisa domin ganin jami’an tsaro sun kawo karshen wannan ta’addancin.”
Dan Majalisar ya ce ya gabatar da bukata ga Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Kasa domin tallafawa wadanda lamarin ya shafa kuma zai ci- gaba da bibiya domin ganin tallafin ya samu cikin lokaci.
Ya ce yana kokarin ganin rundunar sojoji ta kara tura wadatattun jami’ai tare da tallafa masu domin yakar ‘yan ta’addan da wanzar da zaman lafiya a yankunan.
Tallafin kayan abinci na gaggawa da dan majalisar ya bayar sun hada da buhuhuwan masara, gero, garin kwaki da kuma kuli- kuli.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp