’Yan bindiga sun kashe makiyaya 2, sun sace shanu 320 a Kaduna
Published: 29th, May 2025 GMT
Wasu ’yan bindiga sun kashe wasu makiyaya biyu da suka haɗa da: Mudda Shannon da Suleiman Bello, yayin da suka raunata ɗaya a ƙauyen Kurmin Lemu da ke ƙaramar hukumar Kagarko ta Jihar Kaduna.
Wani ɗan unguwar Kurim Lemu mai suna Shuaibu Ibrahim ya ce, lamarin ya faru ne a ranar Alhamis da misalin ƙarfe 12:07 na tsakar dare.
Ya ce, ’yan bindigar da suka zo adadi mai yawa tare miyagun makamai sun mamaye sansanin makiyayan inda suka buɗe wuta, inda suka kashe biyu daga cikin makiyayan nan take.
Ya ce, ɗaya daga cikin makiyayan ya tsallake rijiya da baya, amma ya samu raunukan harbin bindiga, inda ya ce ’yan bindigar sun je kai tsaye inda shanun ke da sansani suka kwashe su zuwa cikin dajin.
Ibrahim, ya ce daga baya an kai makiyayin da suka jikkata zuwa asibiti a garin Kagarko, inda yake jinya, kamar yadda ya ce an sanar da sojojin da ke Kagarko.
“An sanar da wasu sojojin da ke Kagarko, tun kafin su isa sansanin ’yan fashin sun tsere da shanun,” in ji shi.
Wani shugaban unguwar yankin da ya nemi a sakaya sunansa, shi ma ya tabbatar wa wakilinmu afkuwar lamarin ta wayar tarho.
Ya ce, ya samu rahoto daga ɗaya daga cikin shugabannin makiyaya na unguwar cewa ’yan bindiga sun kai hari sansanin makiyaya tare da kashe mutum biyu.
“Da safiyar yau ma na samu rahoto daga wani basaraken Fulani daga ƙauyen Kurmin Lemu cewa, wasu ’yan bindiga sun kai hari sansanin makiyaya inda suka kashe wasu Fulani biyu sannan suka yi awon gaba da shanunsu.” In ji shi.
Shugaban Unguwar ya bayyana cewa, ya kuma sanar da sojojin game da harin, duk da cewa ya ce an binne gawarwakin makiyayan biyu da suka mutu.
Kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Kaduna, ASP Hassan Mansur ya zuwa yanzu bai tabbatar da faruwar lamarin ba, domin har zuwa lokacin da ake haɗa rahoton bai amsa kiran da aka yi masa ba.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Kagarko Makiyaya yan bindiga sun
এছাড়াও পড়ুন:
Real Madrid zata nemi diyyar Dala bilyan 4 daga UEFA
Wata kotu da ke birnin Madrid ta yi watsi da ƙarar da Hukumar ƙwallon ƙafa ta Nahiyyar Turai UEFA, LaLiga da Hukumar Kwallon Kafa ta Sipaniya suka shigar kan ƙin amincewa da gasar Super League.
Wannan yana nufin yanzu Real Madrid da sauran ƙungiyyoyin za su iya neman diyyar kudi Euro Milyan 4.
Kotu ta tsige dan majalisar da ya sauya sheka zuwa APC Shugabannin Kudancin Kaduna za su karrama Janar Christopher MusaReal Madrid ta ce, wannan hukuncin ya tabbatar da cewa UEFA ta karya dokokin gasa, kuma ƙungiyyoyi sun rasa maƙuden kuɗaɗe tun daga lokacin da aka dakatar da gasar.
Gasar wacce aka shirya farawa a shekarar 2021 tare da manyan ƙungiyoyin Turai, an yi hasashen zata samar da kusan Yuro miliyan 200 ga ƙungiyoyin da suka shiga.
A nata martanin hukumar UEFA ta dage cewa wannan sabon hukuncin ba ya nufin an dawo ko an amince da a buga gasar Super League ba ne.