Aminiya:
2025-07-26@13:54:09 GMT

’Yan bindiga sun kashe makiyaya 2, sun sace shanu 320 a Kaduna

Published: 29th, May 2025 GMT

Wasu ’yan bindiga sun kashe wasu makiyaya biyu da suka haɗa da: Mudda Shannon da Suleiman Bello, yayin da suka raunata ɗaya a ƙauyen Kurmin Lemu da ke ƙaramar hukumar Kagarko ta Jihar Kaduna.

Wani ɗan unguwar Kurim Lemu mai suna Shuaibu Ibrahim ya ce, lamarin ya faru ne a ranar Alhamis da misalin ƙarfe 12:07 na tsakar dare.

Ɗalibai sun maƙale lokacin da gini ya rufta suna jarrabawa Ko kwabo ban ciyo bashi ba tun da na zama Gwamnan Kaduna – Uba Sani

Ya ce, ’yan bindigar da suka zo adadi mai yawa tare miyagun makamai sun mamaye sansanin makiyayan inda suka buɗe wuta, inda suka kashe biyu daga cikin makiyayan nan take.

Ya ce, ɗaya daga cikin makiyayan ya tsallake rijiya da baya, amma ya samu raunukan harbin bindiga, inda ya ce ’yan bindigar sun je kai tsaye inda shanun ke da sansani suka kwashe su zuwa cikin dajin.

Ibrahim, ya ce daga baya an kai makiyayin da suka jikkata zuwa asibiti a garin Kagarko, inda yake jinya, kamar yadda ya ce an sanar da sojojin da ke Kagarko.

“An sanar da wasu sojojin da ke Kagarko, tun kafin su isa sansanin ’yan fashin sun tsere da shanun,” in ji shi.

Wani shugaban unguwar yankin da ya nemi a sakaya sunansa, shi ma ya tabbatar wa wakilinmu afkuwar lamarin ta wayar tarho.

Ya ce, ya samu rahoto daga ɗaya daga cikin shugabannin makiyaya na unguwar cewa ’yan bindiga sun kai hari sansanin makiyaya tare da kashe mutum biyu.

“Da safiyar yau ma na samu rahoto daga wani basaraken Fulani daga ƙauyen Kurmin Lemu cewa, wasu ’yan bindiga sun kai hari sansanin makiyaya inda suka kashe wasu Fulani biyu sannan suka yi awon gaba da shanunsu.” In ji shi.

Shugaban Unguwar ya bayyana cewa, ya kuma sanar da sojojin game da harin, duk da cewa ya ce an binne gawarwakin makiyayan biyu da suka mutu.

Kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Kaduna, ASP Hassan Mansur ya zuwa yanzu bai tabbatar da faruwar lamarin ba, domin har zuwa lokacin da ake haɗa rahoton bai amsa kiran da aka yi masa ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Kagarko Makiyaya yan bindiga sun

এছাড়াও পড়ুন:

  New York Times: Harin A Sansanin Udaidai Ya Jaza Wa Amurka Asarar Dala Miliyan 111

Mujallar New York Times ta Amruka ta ce, harin da Iran ta kai wa sansanin sojan Amurka na Udaid, ya jazawa Amurkan asarar kudin da sun kai dala miliyan 111.

 Mujallar ta kuma ce; harin ya sa Amurka ta koyi darussan akan abinda zai iya faruwa idan har fada ya barke a  tsakaninta da China ko Korea Ta Arewa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tallafin Lafiya: Ƙungiyar Rotary Ta Raba Kayan Haihuwa kyauta Ga Mata Masu Juna Biyu  A Kaduna
  •   New York Times: Harin A Sansanin Udaidai Ya Jaza Wa Amurka Asarar Dala Miliyan 111
  • Ta’addanci: Alƙawuran sojoji 8 na kamo Bello Turji
  • Duk da kashe jagororin ’yan bindiga, Turji na ci gaba da kai hare-hare
  • An kashe mata da yara a sabon harin Filato
  • Yadda aka mayar da yaran da aka sace a Kano masu wanke-wanke a Kudu
  • Sojoji Sun Kwato Makamai Daga Hannun Ƴan Bindiga, Sun Ceto Yaro A Filato
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 95 a Neja, sun ceto mutum 138 da aka sace
  • Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutum 11 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Sakkwato
  • Al’ummar Fegin Mahe Sun Yi Zanga-zanga Kan Kisan Jama’a Da ‘Yan Bindiga Ke Yi