Aminiya:
2025-05-30@09:23:57 GMT

’Yan bindiga sun kashe makiyaya 2, sun sace shanu 320 a Kaduna

Published: 29th, May 2025 GMT

Wasu ’yan bindiga sun kashe wasu makiyaya biyu da suka haɗa da: Mudda Shannon da Suleiman Bello, yayin da suka raunata ɗaya a ƙauyen Kurmin Lemu da ke ƙaramar hukumar Kagarko ta Jihar Kaduna.

Wani ɗan unguwar Kurim Lemu mai suna Shuaibu Ibrahim ya ce, lamarin ya faru ne a ranar Alhamis da misalin ƙarfe 12:07 na tsakar dare.

Ɗalibai sun maƙale lokacin da gini ya rufta suna jarrabawa Ko kwabo ban ciyo bashi ba tun da na zama Gwamnan Kaduna – Uba Sani

Ya ce, ’yan bindigar da suka zo adadi mai yawa tare miyagun makamai sun mamaye sansanin makiyayan inda suka buɗe wuta, inda suka kashe biyu daga cikin makiyayan nan take.

Ya ce, ɗaya daga cikin makiyayan ya tsallake rijiya da baya, amma ya samu raunukan harbin bindiga, inda ya ce ’yan bindigar sun je kai tsaye inda shanun ke da sansani suka kwashe su zuwa cikin dajin.

Ibrahim, ya ce daga baya an kai makiyayin da suka jikkata zuwa asibiti a garin Kagarko, inda yake jinya, kamar yadda ya ce an sanar da sojojin da ke Kagarko.

“An sanar da wasu sojojin da ke Kagarko, tun kafin su isa sansanin ’yan fashin sun tsere da shanun,” in ji shi.

Wani shugaban unguwar yankin da ya nemi a sakaya sunansa, shi ma ya tabbatar wa wakilinmu afkuwar lamarin ta wayar tarho.

Ya ce, ya samu rahoto daga ɗaya daga cikin shugabannin makiyaya na unguwar cewa ’yan bindiga sun kai hari sansanin makiyaya tare da kashe mutum biyu.

“Da safiyar yau ma na samu rahoto daga wani basaraken Fulani daga ƙauyen Kurmin Lemu cewa, wasu ’yan bindiga sun kai hari sansanin makiyaya inda suka kashe wasu Fulani biyu sannan suka yi awon gaba da shanunsu.” In ji shi.

Shugaban Unguwar ya bayyana cewa, ya kuma sanar da sojojin game da harin, duk da cewa ya ce an binne gawarwakin makiyayan biyu da suka mutu.

Kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Kaduna, ASP Hassan Mansur ya zuwa yanzu bai tabbatar da faruwar lamarin ba, domin har zuwa lokacin da ake haɗa rahoton bai amsa kiran da aka yi masa ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Kagarko Makiyaya yan bindiga sun

এছাড়াও পড়ুন:

 Nigeria: Mutane Da Yawa Sun  Rasa Rayukansu Sanadiyyar Harin Makiyaya A Jihar Benue

 Rhotanni daga jihar ta Beneu sun ce a wani hari da makiyaya su ka kai a yankin Gwe ya yi sanadiyyar mutuwar mutane 42.

Mahukunta a yankin sun sanar da cewa; an gano gawawwakin mutane 32 da aka kashe sanadiyyar harin da aka kai kauyukan Ahume da Aodona, yayin da aka gano wasu gawawwakin mutane 10 a kauyukan Tyolaha, Tse-Ubiam, kamar yadda shugaban karamar hukuma   Gwer ta yamma Victor Omnin ya bayyana.

Shugaban karamar hukumar ya bayyana wa ‘yan jarida abinda ya faru da cewa; na takaici ne, domin a wannan lokacin da muke Magana ana ci gaba da gano gawawwaki.”

Jahar Benue tana tsakiyar kasar Nigeria ne a yankin da ake kira : Middle-Belt”. An kuma dauki shekaru masu tsawo ana riciki a tsakanin makiyaya da manoma akan kasa saboda rushewar tsarin burtali.

Ofishin Gwamnan jihar ta Benue Hyacinth Lormem Alia, ya kuma sanar da cewa daga cikin wadanda aka  kai wa hari da akwai malamin addinin kirista,amma yana a raye.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisar Dokokin Jihar Kaduna Ta Amince Da Sabbin Kwamishinoni Biyu
  • Falasdinawa 23 Suka Yi Shahada A Farmakin Da Sojojin Mamayar Isra’ila Suka Kai Kan Sansanin Al-Bureij
  • ‘Yan Tawayen Sudan Sun Kashe Fararen Hula 10 A Hare-Haren Da Suka Kai Kan Birnin Kordofan
  • NDLEA ta kama maniyyata aikin hajji ɗauke da hodar iblis
  • ‘Yan Bindiga Sun Sace Basarake A Nasarawa
  • Babu Wata Sauran Mafaka Ga ‘Yan Ta’adda, In Ji Shugaban Rundunar Sojin Sama
  • Falasdinwan Akalla 16 Sojojin HKI Suka Kashe A Gaza Ya Zuwa Yanzu A Yau Laraba
  •  Nigeria: Mutane Da Yawa Sun  Rasa Rayukansu Sanadiyyar Harin Makiyaya A Jihar Benue
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama A Wani Sabon Hari Da Suka Kai Sansanin Sojoji A Borno