Red Crescent ta Iran da Red Cross ta Saliyo sun cimma yarjejeniyoyi da dama a tsakaninsu
Published: 28th, May 2025 GMT
Kungiyar agaji ta red crescent ta iran da kuma kungiyar red cross ta kasar Saliyo sun cimma yarjeniyoyi da dama a tsakaninsu.
An cimma wannan ne a yayin ziyarar da babban daraktan kula da lafiya na kungiyar agaji ta Red Crescent na Jamhuriyar Musulunci ta Iran ya kai Saliyo tare da gudanar da tarurruka da dama da shugaban kungiyar agaji ta Red Cross ta kasar.
Bayan taron, an rattaba hannu kan yarjejeniyar hadin gwiwa tsakanin kungiyar agaji ta Red Crescent ta Jamhuriyar Musulunci ta Iran da kungiyar agaji ta Red Cross ta Saliyo a ofishin jakadancin Jamhuriyar Musulunci ta Iran da ke Saliyo.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kungiyar agaji ta Red
এছাড়াও পড়ুন:
Kungiyar Amnesty Tana Zargin : Gwamantin DRC Da Kungiyar M23 Da Yiyuwar Aikata Lafukan Yaki
Kungiyar kare hakkin bil’aama ta “Amnesty International” ta bayyana cewa; mai yiyuwa ne kungiyar ‘yan tawaye ta m23 da kuma sojojin gwamnatin DRC sun aikata laifukan yaki.
A wani rahoto da aka buga a jiya Talata, kungiyar kare hakkin bil’adam ta ce; Kungiyar M23 wacce take samun goyon bayan kasar Rwanda ta kashe mutane da dama, da kuma azabtar da su bayan da ta tsare su.
Kungiyar ta M23 ta kwace iko da yankin gabashin kasar mai cike da albarkatun karkashin kasa da su ka hada Bukavu da Goma.
Tare da cewa an kulla yarjejeniya a tsakanin M23 da gwamnatin DRC sai dai kuma har yanzu suna ci gaba da fada.