Shugaban Jam’iyyar Adawa A Burtaniya Ya Ce HKI Tana Yaki A Gaza Ne A Madadin Gwamnatin Kasar
Published: 26th, May 2025 GMT
Shugaban wata jam’iyyar adawa a kasar Burtaniya ya bayyana cewa HKI tana yakar Falasdinawa a Gaza ne a madadin gwamnatin kasar tunda har yanzun gwamnatin kasar Burtaniya tana ganin gwamnatin HKI tana kare kanta daga mayakan Hamas, kuma bata daukar abinda HKI take yi a Gaza, kissan kiyashi ne.
Badenoch shugaban jam’iyyar ‘ Conservative’ ya bayyana haka ne a lokacinda yake hira da tashar talabijin ta Sky News dake birnin London a jiya Lahadi.
A lokacinda aka tambaye shi idan ya yarda da maganar Banyamin natanyaho kan cewa hamas yan ta’adda ce, kuma yana kokarin kwace gaza da shafi yan ta’adda ne, sai shugaban Conservative ya ce banzo nan don binciken kalmomin Natanyahu ba. Abinda nake son bada sanarwansa shi ne HKI tana yaki ne a madadin gwamnatin kasar Burtaniya, kamar yadda kasar Ukraine take yakar kasar Rasha a madadin kasashen turai.
Banda haka gwamnatin ta ki ta aibata HKI sannan bata yarda cewa cewa tana aikata kissan kiyashe ne a gaza ba.
Shugaban conservative yana fadar haka ne bayanda shugabannin kasashen Faransa, Burtaniya da kuma Canada suka bukaci HKI ta dakatar da kissan kiyashi na gaza ta kuma bar kayakin agaji su shiga yankin idan ba haka ba suna iya daukar matakai masu tsauri a kanta. Badenoch Shugaban jam’iyyar Conservative ya ce wannan bai wadatar ba.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: gwamnatin kasar
এছাড়াও পড়ুন:
Jamhuriyar Nijar Da China Sun Kusa Warware Sabanin Dake Tsakaninsu Akan Batun Man Fetur
Tashar talabijin din ‘almayadin’ ta ce, wata majiya mai karfi a jamhuriyar Nijar ta ce; An kusa kusa kawo karshen sabanin dake tsakanin gwamnatin jamhuriyar Nijar da kamfanonin kasar China da suke aiki a fagen hako da tace man fetur, bayan da bangarorin biyu su ka yi nisa a tattaunawar da suke yi.
Sauyin da aka sami shi ne amincewar kamfanin man fetur na kasar China ( CNPC) da sauya tsohon manajan dake tafiyar da ayyuka a Nijar, da wani sabo kamar yadda gwamnatin Yamai ta bukata.
Su ma kamfanonin WAPCO da SORAZ za su dauki sabbin matakai na samar da sauye-sauye a cikin harkokin tafiyar da su.
Ana sa ran cewa, sabbin matakan da kamfanoni na China da Nijar suke dauka zai bude sabon shafi a alakar kasashen biyu da za ta kare manufofin kowane bangare.