Shugaban Jam’iyyar Adawa A Burtaniya Ya Ce HKI Tana Yaki A Gaza Ne A Madadin Gwamnatin Kasar
Published: 26th, May 2025 GMT
Shugaban wata jam’iyyar adawa a kasar Burtaniya ya bayyana cewa HKI tana yakar Falasdinawa a Gaza ne a madadin gwamnatin kasar tunda har yanzun gwamnatin kasar Burtaniya tana ganin gwamnatin HKI tana kare kanta daga mayakan Hamas, kuma bata daukar abinda HKI take yi a Gaza, kissan kiyashi ne.
Badenoch shugaban jam’iyyar ‘ Conservative’ ya bayyana haka ne a lokacinda yake hira da tashar talabijin ta Sky News dake birnin London a jiya Lahadi.
A lokacinda aka tambaye shi idan ya yarda da maganar Banyamin natanyaho kan cewa hamas yan ta’adda ce, kuma yana kokarin kwace gaza da shafi yan ta’adda ne, sai shugaban Conservative ya ce banzo nan don binciken kalmomin Natanyahu ba. Abinda nake son bada sanarwansa shi ne HKI tana yaki ne a madadin gwamnatin kasar Burtaniya, kamar yadda kasar Ukraine take yakar kasar Rasha a madadin kasashen turai.
Banda haka gwamnatin ta ki ta aibata HKI sannan bata yarda cewa cewa tana aikata kissan kiyashe ne a gaza ba.
Shugaban conservative yana fadar haka ne bayanda shugabannin kasashen Faransa, Burtaniya da kuma Canada suka bukaci HKI ta dakatar da kissan kiyashi na gaza ta kuma bar kayakin agaji su shiga yankin idan ba haka ba suna iya daukar matakai masu tsauri a kanta. Badenoch Shugaban jam’iyyar Conservative ya ce wannan bai wadatar ba.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: gwamnatin kasar
এছাড়াও পড়ুন:
Afirka Ta Kudu Ta Zargi Shugaban Kasar Amurka Da Rashin Dalili Akan Zargin Yi Wa Fararen Fatar Kasar Kisan Kiyashi
Ministan ‘yan sandan kasar Afirka ta kudu, ya ce, shugaban kasar Amurka Donald Trump ya yi na cewa an yi wa fararen fatar kasar kisan kiyashi a yayin ziyarar da shugaban kasar Afirka ta kudu Cyril Ramaphosa ya kai.
A yayin ganawar da ya yi da shugaban kasar Afirka ta kudu, shugaban kasar Amurka ya kunna wani faifen bidiyo da a ciki aka nuna gicciye a gefen hanya domin tunawa da fararen fata manoma da aka yi wa ksian gilla.
Ministan ‘yan sandan kasar ta Afirka ta kuku Senzo Mchunu ta cewa; Wadannan gicciyen ba su nuni da cewa suna akan kabarurruka ne, ko wani wuri na tunawa da matatu, an Sanya su ne a 2020 domin tunawa da dukkanin manoman da aka kashe a fadin kasar ta Afirka ta kudu.
Har ila yau, ministan ‘yan sandan na kasar Afirka ta kudun ya kuma kara da cewa; ‘yan fashi da makami sun kashe wasu ma’aurata manoma a cikin gonarsu, yana mai kara da cewa; Abinda Trump ya yi shi ne murguda wancan labarin da kirkirar abinda ya kira; “Kisan Kiyashi.”
Mchunu ya kara da cewa; kasar Afirka ta kudu tana girmama mutanen Amurka da shugaban kasarta, amma ko kadan ba ta girmama kirkirarren labarin; Kisan Kiyashi.”
Amurka ta dauki wannan matakin ne dai a kan Afirka Ta Kudu saboda ta kai karar HKI akan kisan kiyashin da take yi wa al’ummar Falasdinu.