Aminiya:
2025-06-01@23:12:19 GMT

Za a ɗauke ruwan famfo na tsawon mako 2 a Abuja 

Published: 31st, May 2025 GMT

Mazauna Babban Birnin Tarayya za su fuskanci katsewar ruwan sha na tsawon makonni biyu, kamar yadda Hukumar Kula da Ruwa ta yankin ta sanar.

Rashin ruwan, wanda ya fara ranar Juma’a, 30 ga Mayu, ana sa ran za ta ci gaba har zuwa ranar Juma’a, 13 ga Yuni.

Matsalar ta samo asali ne daga ayyukan gyare-gyare da ake yi a tashoshin tace ruwa na madatsar ruwa ta Lower Usuma Dam.

A cewar sanarwar da hukumar ta fitar, gyare-gyaren sun shafi muhimmin aikin haɗa kayan aikin lantarki da injiniya, wanda babban bangare ne na aikin inganta matatar.

Maƙabarta mai shekaru 500 da ta koma maɓoyar ’yan daba Sojoji sun kashe ɗan ta’adda da aka sa ladar N100m a kansa a Borno

Wannan aiki ya tilasta dakatar da rarraba ruwa na ɗan lokaci zuwa tsakiyar birnin da kuma yankunan wajenta.

Hukumar ta shawarci jama’a da su tanadi isasshen ruwa da zai ishe su tsawon lokacin, sa’annan su nemi wasu hanyoyin samun ruwa don biyan bukatunsu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: katse ruwa ruwa

এছাড়াও পড়ুন:

Nukiliya : Iran ta kirayi mai kula da harkokin Ostiriya da ke birnin Tehran kan wasu kalamai na tsokana

Ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ta kirayi babbar mai kula da harkokin kasar Ostiriya da ke birnin Tehran domin nuna rashin amincewa da zarge-zargen data danganta da na ‘’tsokana” da hukumar leken asirin cikin gidan kasar ta Turai ta yi dangane da shirin nukiliyar Iran na zaman lafiya.

Shugaban ofishin sashen yammacin Turai na ma’aikatar harkokin wajen Iran Alireza Molaqadimi ya gayyaci Michaela Pacher a ranar Juma’a, inda ya nuna bacin ran kasar iran game da zarge-zargen.

A cikin rahotonta na shekara-shekara kan barazanar da duniya ke fuskanta, hukumar leken asiri ta kasar Ostiriya (DSN) ta yi ikirari a ranar Litinin cewa Iran na ci gaba da aiwatar da shirin kera makaman nukiliya tare da fadada karfinta na makamai masu linzami.

M. Molaqadimi ya yi watsi da wannan zargi mara tushe, yana mai jaddada cewa ya sabawa rahotanni da dama da hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya IAEA ta fitar.

Ya ce shirin nukiliyar kasar Iran ya yi daidai da alkawurran da kasar ta doka karkashin yarjejeniyar hana yaduwar makaman nukiliya ta NPT, ya kuma yi kira ga gwamnatin Ostiriya da ta yi bayani a hukumance kan wannan batu.

Tun da farko dama a ranar Juma’a, kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran, Esmail Baghai, ya yi watsi da rahoton da ya ce na “karya ne kuma marar tushe” da hukumar leken asirin ta Austria ta fitar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Makami Mai Linzami Daga Yemen Ya Tashi Jiniyar Gargadi A Garuruwa 300 Na HKI
  • Shugaba Tinubu Ya Aika Tawaga Zuwa Jihar Neja Kan Ambaliya Ruwa
  • Mutanen da suka rasu a ambaliyar ruwa a Neja sun ƙaru zuwa 151
  • Mutanen da suka rasu a ambaliyyar ruwa a Neja sun ƙaru zuwa 151
  • Limamin Sallar Juma’ar Tehran Ya Jaddada Cewa: Babu Wanda Zai Dakatar Da Iran Tace Sinadarin  Uranium
  • Nukiliya : Iran ta kirayi mai kula da harkokin Ostiriya da ke birnin Tehran kan wasu kalamai na tsokana
  • Dantsoho Ya Kaddamar Da Aikin Tsaftace Tashar Jirgi Ta Tin-Can Island
  • Mutanen da suka mutu a ambaliyar Neja sun ƙaru zuwa 88 —NSEMA
  • GORON JUMA’A 30-03-2025