Ƙungiyar Gwamnonin Nijeriya (NGF) ta bayyana baƙin ciki da alhini kan mummunan haɗarin mota da ya yi ajalin wasu ‘yan wasa daga jihar Kano, yayin da suke dawowa daga gasar wasanni ta ƙasa da aka kammala a jihar Ogun.

Shugaban NGF kuma gwamnan jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, ya fitar da wata sanarwa da ya sanya wa hannu da kansa a yau Asabar, yana mai miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan mamatan da gwamnatin jihar Kano.

Mutane 21 Sun Mutu A Tawagar Ƴan Wasannin Kano A Hatsarin Mota Ahmed Musa Ya Angwance Da Matarsa Ta 4 A Kano

“Muna miƙa ta’aziyyar ga iyalan ‘yan wasan, gwamnatin jihar Kano da kuma ɗaukacin ma’abota wasanni a faɗin kasar nan,” in ji sanarwar.

Gwamna AbdulRazaq ya ƙara da cewa: “Muna rokon Allah Maɗaukakin Sarki Ya jiƙansu da rahama, Ya kuma ba da haƙura da ƙarfin gwuiwa ga iyalansu da duk wanda abin ya shafa a wannan lokaci mai wahala.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Wasa Yan wasan Kano

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Yusuf Ya Bada Hutu A Ranar Litinin Domin Addu’o’i Ga ‘Yan Wasan Kano 22 Da Suka Rasu

 

Gwamna Yusuf wanda a halin yanzu yake kasar Saudiyya don gudanar da aikin hajjin 2025, ya bayar da umarnin ware ranar Litinin 2 ga watan Yunin 2025 a matsayin ranar hutu domin bai wa al’ummar damar yin jimami tare da yi wa wadanda suka rasu addu’a.

 

Ya kuma yi kira ga limamai da daukacin al’umma a fadin jihar, da su yi addu’o’i na musamman ga wadanda abin ya shafa da kuma karfafa wa iyalansu da suka rasu.

 

Gwamna Yusuf ya tabbatar da cewa, gwamnati na daukar matakan tallafawa wadanda suka jikkata da kuma iyalan wadanda abin ya shafa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sanatocin Arewa Sun Yi Jimamin Rasuwar ‘Yan Wasan Kano
  • Gwamnatin Kano Ta Ba Da Hutun Makaranta Domin Bukukuwan Sallah
  • Gwamna Yusuf Ya Bada Hutu A Ranar Litinin Domin Addu’o’i Ga ‘Yan Wasan Kano 22 Da Suka Rasu
  • Gwamnatin Kano Ta Ba Iyalan Mamatan Wasanni Tallafin Naira Miliyan Ɗaya Kowane
  • Gwamnonin Najeriya Sun Bayyana Alhininsu Bisa Rasuwar ‘Yan Wasan Kano
  • Mutane 20 sun rasu a hatsari motar ’yan wasan Jihar Kano
  • Ahmed Musa Ya Angwance Da Matarsa Ta 4 A Kano
  • Gwamnatin Tarayya Ta Yi Ta’aziyyar Mutanen Da Suka Rasu A Ambaliyar Garin Mokwa A Neja
  • Gwamnatin Jihar Gombe Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniya Domin Gina Mayankar Dabbobi