A cewar jami’ai, za’a tsara yadda tsarin fitar da barasar zai kasance ta hanyar tabbatar da cewar an ba da horo ga masu sayar da ita da kuma basu takardar lasisin sayar da barasar. Hakazalika, za a tsaurara ka’idoji akan sayar da barasa a kasar, gwamnati ta jaddada cewa ana gabatar da sauye-sauyen ne cikin taka-tsantsan tare da kula da al’adun al’ummar kasar.

 

“Manufar ita ce, maraba da duniya ba tare da rasa asalin al’adu ba, sanya Saudiyya a matsayin mai ci gaba, duk da haka mai mutunta taswirar yawon shakatawa na duniya,” in ji hukumomin Saudiyya a cikin wata sanarwa.

 

Matakin ya zo ne a daidai lokacin da Saudiyya ke neman yin gogayya da kasashe makwabta kamar Hadaddiyar Daular Larabawa da Bahrain, inda a bisa ka’ida ake samun barasa a wuraren yawon bude ido.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Mene Ne Dalilin Amurka Na Cewa Zata Harba Makamamin Nukiliya Kan Yankin Zirin Gaza?

Mene ne dalilin da ya sa Amurka da Isra’ila suke barazanar jefa bama-baman nukiliya a Gaza?

Masanin siyasa kuma mai sharhi Abdel Bari Atwan ya rubuta labarin game da barazanar da Amurka ta yi na kai wa Gaza hari da makamin nukiliya, yana mai cewa; “Domin dan majalisar wakilai na jam’iyyar Republican Randy Fein ya yi kira da a kai hari kan Zirin Gaza da bama-baman nukiliya, kwatankwacin abin da kasarsa ta yi a Hiroshima da Nagasaki na Japan, a karshen yakin duniya na biyu, da kuma samun wanda ya yaba masa a gwamnatin Shugaba Donald Trump, wannan shi ne kololuwar ta’addanci, rashin mutuntaka, da kishir ruwan zubar da jini a duniya daga jagororin da ke da’awar kare hakkin bil’adama a duniya kuma daga kasar da ta fi kowace kasa da’awar kare hakkin bil’adama da neman wanzar da adalci a fadin duniya.

Wani abin mamaki shi ne, wannan kira ya fito ne daga wani dan majalisar wakilai na jam’iyyar Republican wanda shugaba Trump ke goyon bayan yakin neman zabensa, da kuma abin takaici, har ma da wasu Larabawa masu kada kuri’a. Wannan kiran na kai harin makamashin Nukiliya ya zo ne a daidai lokacin da Trump ya dawo daga rangadin da ya kai wasu kasashen Larabawa uku, inda ya yi nasarar karbar dala tiriliyan 5, ciki har da wani jirgin sama na shugaban kasa a matsayin kyauta, wanda ya kai kusan rabin dala biliyan daya bayan da aka cika masa kayan aiki.

Wannan dan majalisar mai dauke da akidar ‘yan sahayoniyya ta nuna wariyar al’umma, da bai san adadin mutanen da Benjamin Netanyahu ya zubar da jininsu a yakin kisan kiyashin da ya jagoranta kan Gaza ba, wanda abin koyi ne a cikin kungiyar ‘yan Nazin zamani kuma wadanda ya kashe ya ninka adadin wadanda harin bam din nukiliya guda biyu da aka jefa kan biranen kasar Japan biyu. Kwatanta wannan da yawan al’ummar Zirin Gaza, wadanda ba su wuce miliyan biyu ba, da kuma al’ummar Japan, wadanda aka kiyasta kusan miliyan 124.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • CMG Ta Cimma Nasarar Gudanar Da Gasar Mutum-Mutumin Inji Ta Kasa Da Kasa
  • Raya Al’adu Wani Sirri Ne Na Ci Gaban Kasar Sin
  • Akwai Ma’ana Mai Zurfi A Bayan Da’a
  • Tare Da Taimakon Kasar China Za A Bude Masana’antun  Sarrafa Sanadarin Lithium A Nigerria
  • Gaza : Spain ta bukaci kasashen duniya su kakabawa Isra’ila takunkumi
  • Shugaban Kasar Kenya: FOCAC Ya Samar Da Damammaki Ga Sin Da Afirka Wajen Inganta Hadin Kansu Da Samun Moriya Tare
  • Mene Ne Dalilin Amurka Na Cewa Zata Harba Makamamin Nukiliya Kan Yankin Zirin Gaza?
  • An Gano Kofin Gasar Zakarun Turai Na Mata Bayan Sace Shi Da Aka Yi
  • Tawagar MDD Da Majalisar Shugabancin Libya Sun Kafa Kwamitin Tsagaita Bude Wuta