Mataimakin ministan ma’aikatar cinikayya ta kasar Sin Ling Ji, ya ce gwamnatin kasar Sin za ta ci gaba da zurfafa dunkule rawar da yankunan raya tattalin arziki da fasahohi mallakin gwamnati ke takawa, a fannin janyo jarin waje, a gabar da kasar ke kara fadada matakanta na bude kofa ga kasashen waje.

Ling Ji, wanda ya bayyana hakan a Talatar nan yayin wani taron manema labarai da ya gudana, ya ce a halin yanzu yanayin hada-hadar tattalin arziki da cinikayyar kasa da kasa na cikin wani halin ha’ula’i, kuma sakamakon haka, matsayar yankunan raya tattalin arziki da fasahohi na muhimmin jigon daidaita hada-hadar cinikayyar waje, da zuba jari na kara bayyana a fili.

Ya zuwa shekarar 2024, adadin irin wadannan yankuna ya kai 232 a sassan kasar Sin, inda suka samar da darajar GDPn da ya kai kudin Sin tiriliyan 16.9, kwatankwacin dalar Amurka tiriliyan 2.35. (Mai fassara: Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

NPA Ta Yi Wa Ma’aikatanta 1,500 Karin Girma

Dantsoho ya kara da cewa, nuna kwarewar ma’aikata na kara taimaka wa, wajen cimma burin da aka sanya a gaba, musamman a bangaren nuna yin gasa, a tafiyar da Tashohin Jiragen Ruwa.

“Ta irin wannan hanyar ce, za mu iya cimma bukatar da muke da ita da kuma cika muradin masu ruwa da tsaki, da ke a fannin, musamman domin mu kara karfafa karsashin ma’aikatan mu,” Inji Dantsoho.

Dantsoho ya kuma jinjinawa Minsitan ma’aikatar bunsa hada –hadar kasuwanci na kan Teku Adegboyega Oyetola, kan sahalewar Hukumar ta NPA, na yin karin girman ga ma’aikatan da suka amfana, wanda Hukumar ta jima, tana da bukatar yin hakan.

“Dole ne kuma in yabawa Ministanmu Adegboyega Oyetola, kan amincewar da ya yi, na kawo karshen batun yiwa ma’aikatan karin matsayin, ta hanyar gudanar masu da jarrabawar yin gwaji,” A cewar Shugaban.

A na sa jawabin madadin gamayyar kungiyoyin na Tashoshin Jiragen Ruwan kasar SSASCGOC, Kwamarade Bodunde, ya nuna jin dadinsa kan wannan karin matsayin da aka yiwa ma’aikatan.

“Muna kuma godiya, kan inganta walwalar ma’aikatan Hukumar ta NPA da kara inganta ayyukan ‘ya’yan kungiyar, musamman duba da irin yanayin matsin tattalin arzikin da ake fama da ita a kasar, Inji Bodunde.”

Shi kuwa, Janar Manaja a sashen tsare-tsare da samar da bayanai na Hukumar ta NPA Ikechukwu Onyemekara, ya bayyana cewa, zamanantar da kayan aikin Tashoshin Jiragen Ruwan kasar, hakan zai kara taimaka wa wajen kara inganta ayyukan ma’aikatan.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani
  • Dakarun Juyin Juya Halin Musulunci Sun Kama ‘Yan Leken Asirin Isra’ila A Lardin Mazandaran Na Kasar Iran
  • Kyautar ‘Jakadan Abota’ Na Kasar China Ya Shiga hannun Iran
  • Iran Ta Yi Tir Da Takunkuman Tattalin Arzikin Da Amurka Ta Dorawa Ma’aikaciyar MDD
  • Kasar Sin Na Da Muradin Zurfafa Hadin Gwiwar BRI Da Masar 
  • Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci Ta Iran Ya Ce: Jagora Da Kansa Ya Shiga Dakin Ba Da Umarnin Sojin Lokacin Yaki
  • NPA Ta Yi Wa Ma’aikatanta 1,500 Karin Girma
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Wasu Matasa Ba Sa Aiki Tukuru Wajen Neman Arziki
  • Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita
  • Sauye-sauyen Tinubu Suna Taimaka Wa Farfaɗowar Tattalin Arzikin Nijeriya — Minista