Bangarorin ‘yan gwagwarmayar Falasdinawa sun kai hari kan sojojin mamaya a wani farmakin hadin gwiwa da suka kai a Khan Yunus

Dakarun Sarayal-Quds bangaren sojin kungiyar Jihadul-Islami da kuma dakarun Izzuddeen Al-Qassam bangaren sojin kungiyar gwagwagrmayar Musulunci ta Hamas sun tabbatar da cewa: Sun yi nasarar kashe sojojin mamayar Isra’ila tare da raunata wasu a farmakin hadin gwiwa da suka kai kan yankin “Unguwar Turawa” a kudu maso gabashin Khan Yunus da ke kudancin zirin Gaza.

Dakarun Sarayal-Quds a cikin wani takaitaccen bayani da suka fitar sun bayyana cewa: Sun gudanar da wani farmakin hadin gwiwa tare da dakarun Al-Qassam kan sojojin haramtacciyar kasar Isra’ila da suka kutsa cikin yankin Unguwar Turawa a kudu maso gabashin Khan Yunus, bayan da suka yi artabu da su gaba da gaba.

A nata bangaren, rundunar Al-Qassam ta sanar a cikin wata sanarwa da ta fitar cewa: Mayakan Al-Qassam tare da mayakan Sarayal- Quds, sun samu nasarar kai hari kan sojojin yahudawan sahayoniyya da ke cikin wani gida, da makamai masu linzami na TBG.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Najeriya: An Bude Bincike Sojojin Da Suke Bayar Da Makamai Ga Kungiyoyi Masu Dauke Da Makamai

Mahukunta a tarayyar Najeriya sun sanar da kama wasu sojoji  da ‘yan sanda 30 bisa tuhumarsu da sace makaman gwamnati da sayar da su ga kungiyoyi masu dauke da makamai, daga cikinsu har da kungiyoyin da suke ikirarin jihadi.

Sanarwar da rudnunar sojan kasar ta Najeriya ta fitar ta kunshi cewa; Farmakin da rundunar sojan kasar ta fara kai wa a cikin watan Ogusta na 2024 tana a matsayin mayar da martani ne akan satar makamai da alabarusai na gwamanti da ake yi, kuma ya zuwa yanzu bincike ya sa an kama sojoji 18 da kuma ‘yan sandan 15 sai kuma wasu fararen hula 8 da su ka hada da sarkin gargajiya daya.

Wannan sanarwar dai ta zo ne adaidai lokacin da kasar ta Najeriya take fuskantar kalubale mai girma ta fuskar tsaro, ta yadda a bayan nan kungiyoyin Bokoharam, da Iswap su ka dawo da hare-haren da suke kai wa musamman akan rundunar sojojin kasar.

Dama a baya wata cibiyar mai nazari da bincike akan yankunan da ake rikice-rikicen makamai a duniya mai matsuguni a Birtaniya, ta bayyana cewa; Kungiyoyin da suke ikirarin jihadi a yankin Sahel, suna samun kaso 20% na makamansu ne daga cikin kasashensu.

Baya ga matsalar masu ikirarin jihadi da ake fama da su da Najeriya, da akwai kuma ta barayin daji da suke sace mutane domin karbar kudin fansa, mafi yawancinsu a yankin Arewa maso yammacin kasar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Najeriya: An Bude Bincike Sojojin Da Suke Bayar Da Makamai Ga Kungiyoyi Masu Dauke Da Makamai
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kutsa Cikin Yankunan Kasar Siriya Tare Da Kafa Wuraren Bincike
  • Kungiyar Hamas Ta Bukaci Masu Shiga Tsakani Amurkawa Su Gamsar da Ita Za’a Dakatar Da Yaki A Gaza
  • Sojojin Yemen Zasu Bullo Da Shirin Takurawa Jiragen Saman Haramtacciyar Kasar Isra’ila  
  • Macron : Faransa za ta iya sanya takunkumi ga gwamnatin Isra’ila matukar ba ta kawo karshen killace Gaza ba
  • Hana shigar da abinci da Isra’ila ta yi zuwa Gaza ‘laifi ne na yaki’: MDD
  • Sojoji sun kashe ɗan ta’adda da aka sa ladar N100m a kansa a Bor
  • Sojojin Yemen Sun Hana Jigilar Jiragen Sama A Isra’ila Tare Da Firgita ‘Yan Sahayoniyya
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Aiwatar Da Kisan Kiyashi Kan Falasdinawa A Yankin Zirin Gaza