‘Yan Gwagwamayar Falasdinu Sun Halaka Sojojin Mamayar Isra’ila Masu Yawa A Wani Harin Kwanton Bauna
Published: 31st, May 2025 GMT
Bangarorin ‘yan gwagwarmayar Falasdinawa sun kai hari kan sojojin mamaya a wani farmakin hadin gwiwa da suka kai a Khan Yunus
Dakarun Sarayal-Quds bangaren sojin kungiyar Jihadul-Islami da kuma dakarun Izzuddeen Al-Qassam bangaren sojin kungiyar gwagwagrmayar Musulunci ta Hamas sun tabbatar da cewa: Sun yi nasarar kashe sojojin mamayar Isra’ila tare da raunata wasu a farmakin hadin gwiwa da suka kai kan yankin “Unguwar Turawa” a kudu maso gabashin Khan Yunus da ke kudancin zirin Gaza.
Dakarun Sarayal-Quds a cikin wani takaitaccen bayani da suka fitar sun bayyana cewa: Sun gudanar da wani farmakin hadin gwiwa tare da dakarun Al-Qassam kan sojojin haramtacciyar kasar Isra’ila da suka kutsa cikin yankin Unguwar Turawa a kudu maso gabashin Khan Yunus, bayan da suka yi artabu da su gaba da gaba.
A nata bangaren, rundunar Al-Qassam ta sanar a cikin wata sanarwa da ta fitar cewa: Mayakan Al-Qassam tare da mayakan Sarayal- Quds, sun samu nasarar kai hari kan sojojin yahudawan sahayoniyya da ke cikin wani gida, da makamai masu linzami na TBG.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Jami’in Shari’ar Kasa Da Kasa Ya Bayyana Cewa: Harin Da Aka kai Kan Iran Babban Laifi Ne
Jami’in harkar shari’ar kasa da kasa ya bayyana cewa: Harin da aka kai wa Iran babban laifi ne kuma jarrabawa ce ta tarihi ga kwamitin sulhu
Mataimakin ministan harkokin wajen kasar Iran kan harkokin shari’a da kasa da kasa, Kazem Gharibabadi, ya ce: Harin da aka kai wa Iran babban laifi ne, kuma jarrabawa ce ta tarihi ga kwamitin sulhun Majalisar Dinkin Duniya.
A yayin wani taron manema labarai da ya yi da wakilan kasashe mambobin Majalisar Dinkin Duniya fiye da 110 a birnin New York na kasar Amurka a jiya Litinin, Gharibabadi ya bayyana ma’auni na wuce gona da iri da gwamnatin yahudawan sahayoniyya da Amurka suka dauka kan yankin Jamhuriyar Musulunci ta Iran da kuma sakamakonsa ga zaman lafiya da tsaro a duniya.
Ya dauki gwamnatin yahudawan sahayoniya a matsayin babbar mai haifar da rashin tsaro da zaman lafiya a yankin cikin shekaru 80 da suka gabata, yana mai jaddada cewa: Wannan ita ce gwamnatin da ya zuwa yanzu ta aiwatar da ayyukan ta’addanci sama da 3,000, tare da raba Falasdinawa sama da miliyan bakwai da muhallansu, da kashe dubban daruruwan Falasdinawa, tare da kame Falasdinawa sama da miliyan guda.