HausaTv:
2025-07-24@23:43:03 GMT

 DRC: Joseph Kabila Ya Bayyana A Yakin Dake Karkashin Kungiyar M23

Published: 30th, May 2025 GMT

Rahotanni daga kasar ta DRC sun ambaci cewa an ga tsohon shugaban kasar Joseph Kabila a jiya Alhamis a garin Goma wanda yake a karkashin ikon ‘yan tawayen kungiyar M23.

Majiyar malaman addinin kirista a yankin ce ta sanar da cewa, ta gayyace shi ne domin ya shiga Tsakani a kawo karshen yakin da ake yi a yankin.

Bishop Joel Amurani ne ya sanar da cewa, su ne su ka gayyaci tsohon shugaban kasar wanda ya kasance akan karagar Mulki daga 2001 zuwa 2019.

A yayin ziyarar tashi a garin na Goma, Kabila ya gana da bangarori mabanbanta da su ka hada da malaman addinin yankin.

A can birnin Kinshasha, gwamnatin Felix Tshisekedi tana zargin Kabila da cewa yana goyon bayan kungiyar ta M23 wacce ta shimfida ikonta a gabashin kasar.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Tsohon Sakataren Gwamnatin Bauchi, Ibrahim Kashim, Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP

Ya ce ya zagaya dukkanin ƙananan hukumomin Jihar Bauchi domin goyon bayan Gwamna Bala yayin yaƙin neman zaɓe, duk da cewa yana ci gaba da aiki a matsayin Sakataren Gwamnatin Jiha.

A watan Janairu 2025, Kashim ya yi murabus daga matsayin SSG, inda ya ce gwamnan ne ya umarce shi da yin hakan.

Rahotanni na nuna cewa Kashim na da niyyar sake tsayawa takarar gwamna a nan gaba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kungiyar “Human Right Watch” Ta Yi Kira Da A Saki Tsohon Shugaban Kasar Nijar Muammad Bazoum
  • Farfesa Yilwatda Ya Zama Sabon Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa
  • Iran Tace Tawagar Kwararru Daga Hukumar IAEA Zata Ziyarci Kasar Nan Ba Da Dadewa Ba
  • Sin Ta Yi Mu’amala Da Kasashen Dake Kan Karshen Kogin Yarlung Zangbo Dangane Da Batun Gina Tashar Samar Da Wutar Lantarki Ta Karfin Ruwa A Kogin
  • Shugaban Amurka Trump Ya Bukaci Gurfanar Da Tsohon Shugaban Amurka Barack Obama A gaban Kuliya
  • Kasar Sin Tana Da Dokoki Da Ka’idoji Sama Da 180 Dake Kare Nakasassu
  •  Netanyahu: Ba Za Mu Daina Yakin Gaza Ba
  • Sin Da Masar Za Su Karfafa Dangantakarsu Karkashin Kungiyar SCO
  • Tsohon Sakataren Gwamnatin Bauchi, Ibrahim Kashim, Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP
  • Wata Kungiyar Ta Bukaci Shugaban Kasa Ya Cika Alkwarin Marigayi Shugaba Buhari Game Da Shehu Usman Aliyu Shagari