Sojojin Sudan Sun Fatattaki Dakarun Kai Daukin Gaggawa Daga Sansaninsu Da Ke Birnin Omdurman
Published: 27th, May 2025 GMT
Sojojin Sudan sun yi nasarar fatattakan ‘yan tawayen kasar na kungiyar Rapid Support Force daga sansanoninsu da ke kudancin Omdurman
Hukumomin sojin Sudan a birnin Omdurman na jihar Khartoum, sun sanar da cewa: Dakarun kai daukin gaggawa na Rapid Support Forces sun tsare sun bar makamai da alburusai da dama da suka hada da haramtattun makamai da aka hana amfani da su a dokokin kasa da kasa, bayan da suka sha kashi a yankin Al-Saliha da ke kudancin birnin.
Yakin baya- bayan nan da sojojin Sudan suka yi da dakarun kai daukin gaggawa na Rapid Support Forces a yankin Al-Saliha da ke kudancin Omdurman ba abu ne mai sauki ba. An kwashe sama da wata guda ana gwabza fada. Babban dalilin shi ne mallakar manyan makamai da Dakarun kai daukin gaggawa suka yi, wanda ya janyo bullar tambayoyi da dama kan yadda dakarun da ba su da isasshen horo don amfani da irin wadannan makaman za su iya mallakar su, sai dai idan suna samu goyon baya daga waje.
Suleiman Abdo Ali, kwamandan rundunar soja ta Takht Omdurman, ya ce: “Alhamdu lillahi, an fatattaki makiya sun bar kayan aikin soja, da a ce sun kasance sojoji ne na yau da kullun ko kuma sojoji ne masu manufa ko wata akida da su tsaya a fafata da su.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Dakarun kai daukin
এছাড়াও পড়ুন:
Dakarun Juyin Juya Halin Musulunci Sun Kama ‘Yan Leken Asirin Isra’ila A Lardin Mazandaran Na Kasar Iran
Dakarun juyin jaya halin Musulunci ta Iran sun kama wani wakilin hukumar leken asirin Isra’ila Mossad a arewacin kasar Iran
Dakarun kare juyin juya halin Musulunci sun sanar da kame wani jami’in hukumar leken asirin haramtacciyar kasar Isra’ila “Mossad” a lardin Mazandaran (arewacin kasar Iran), wanda ke shirin kai harin ta’addanci a cikin kasar.
Sanarwar da dakarun kare juyin juya halin suka fitar ta bayyana cewa: wani ma’aikacin fage na makiya da ke shirin aiwatar da ayyukan ta’addanci ta hanya kai tsaye wajen jagorantar masu adawa da Iran a kasashen waje, an kama shi ne a wani gagarumin samame da jami’an leken asirin na Karbala suka kai, kafin ya aiwatar da duk wani aikin ta’addanci.
Sanarwar ta kara da cewa: Bincike ya kai ga gano tare da kama wasu da dama daga cikin ‘yan kungiyar leken asirin da lamarin ya shafa.
Tawagar masu leken asiri ta dakarun kare juyin juya halin Musulunci a lardin Mazandaran ta tabbatar da cewa tana cikin shiri da kuma taka tsantsan, kuma ta yi gargadin cewa “duk wani mataki na nuna adawa da tsaron kasar, zai fuskanci dauki mai tsauri da raɗaɗi.”