Aminiya:
2025-05-31@19:00:54 GMT

Faransa ta haramta shan sigari a cikin jama’a

Published: 30th, May 2025 GMT

Kasar Faransa ta ce daga ranar daya ga watan Yuli mai zuwa ta haramta shan sigari a wuraren taruwar jama’a.

Kasar ta ce wuraren da haramcin ya shafa sun hada da makarantu da tashoshin mota ko na jirgi, wuraren shakatawa, wuraren wasanni ko kasuwanni saboda kada yara kanana su gani.

Yadda ambaliyar Neja ta ci mutum 12 ’yan gida daya NAHCON ta kammala jigilar maniyyata aikin hajjin 2025

Ministar Lafiya da Iyali na kasar, Catherine Vautrin ce ta bayyana hakan a ranar Alhamis, inda ta ce, “Dole a daina shan sigari a wuraren da yara suke.

“’Yancin shan sigari ya kare ne a inda ’yancin yara na shakar tsaftatacciyar iska ya fara,” kamar yadda ministar ta shaida wa jaridar Ouest-France ta kasar.

Kazalika, dokar za ta hana dalibai shan sigari a gaban makarantu, kuma duk wanda aka samu ya karyata zai iya fuskantar hukuncin biyan tarar da ta kai Dala 154, kusan Naira 250,000 ke nan.

A cewar alkaluman Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO), fiye da kaso 35 cikin 100 na mutanen kasar Faransa na ta’ammali da sigari.

 

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Faransa Sigari shan sigari a

এছাড়াও পড়ুন:

Za a gabatar da Huɗubar Ranar Arfa a harsunan Najeriya 3

Hukumomin ƙasar Saudiyya sun sanar cewa a bana za a gabatar wa mahajjata huɗubar Ranar a cikin harsuna uku na Najeriya.

Harsunan Najeriya guda uku da za a gabatar da Huɗubar Ranar Arfa da su sun ne Hausa da Fulatanci da kuma Yarbaci.

Harsunan huda uku na daga cikin  karin harsunan duniya guda 34 da hukumomin Saudiyya suka sanar cewa za a gabatar da Huɗubar a cikinsu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Za a gabatar da Huɗubar Ranar Arfa a harsunan Najeriya 3
  • Nukiliya : Iran ta kirayi mai kula da harkokin Ostiriya da ke birnin Tehran kan wasu kalamai na tsokana
  • Gwamnatin Kano ta haramta liƙa hotuna ko rubutu marasa ma’ana a A-Daidaita-Sahu
  • Koshin Lafiyar Yaran Kasar Sin Na Kara Inganta
  • Shugaban Kasar Iran Ya Jaddada Matsayin Iran Na Rashin Tunanin Kera Makamin Nukiliya
  • Yadda ambaliyar Neja ta ci mutum 12 ’yan gida daya
  • Duniyarmu A Yau: Wasikar Lawyoyi 800 Ga Firay Ministan Kasar Burtaniya Kan Gaza
  •  Kasar Chile Na Shirin Yanke Alakar Diplomasiyya Da “Isra’ila”
  • Yunkurin Philippines Bai Kai Gaci Ba A Tekun Kudancin Kasar Sin