Aminiya:
2025-05-31@22:39:40 GMT

An gano gawar direba a cikin mota a Bayelsa

Published: 30th, May 2025 GMT

An gano gawar wani direban da yake tuƙi ƙarƙashin kamfanin sufuri  da har yanzu ba a tantance shi ba a yankin Samphino na Yenagoa, babban birnin Jihar Bayelsa.

Daily Trust ta ruwaito cewa, an gano gawar direban matashin mai matsakaicin shekaru da sanyin safiyar Juma’a a cikin motarsa ​​a mahaɗar Samphino da ke unguwar Kpansia a unguwar Yenagoa.

Mutanen da suka mutu a ambaliyar Neja sun ƙaru zuwa 88 —NSEMA Faransa ta haramta shan sigari a cikin jama’a

Wasu shaidun gani da ido da mazauna wurin da suka gano mutumin a wurin, an bayyana cewa, sun sanarwa da jami’an tsaro lamarin inda suka yi gaggawar ɗaukar mataki a wajen tare da killace wurin.

Mazauna yankin sun ce mai yiwuwa wasu da ake zargin ’yan fashi da makami ne suka harbe direban, a yunƙurin ƙwace motarsa ​​ko wasu kayayyaki masu daraja.

Kodayake har yanzu ba a samu cikakkun bayanai ba, rahotannin da ba a tabbatar da su ba sun nuna cewa, mai yiwuwa maharan sun kira direban ne ta tikitin tafiya ta hanyar amfani da manhajar wayar salula ta Bolt, dabarar da ta ƙara nuna damuwa kan tsaron lafiyar direbobin da ke aiki da manhajar na direbobi a jihar.

Lamarin ya haifar da wani sabon tashin hankali a tsakanin mazauna garin da direbobin masu ɗaukar fasinja a Yenagoa, sa’o’i 24 bayan gwamnatin Jihar Bayelsa ta ba da gudummawar motocin sufuri aiki 31 ga jami’an tsaro daban-daban domin ƙarfafa ƙoƙarin yaƙi da miyagun ayyuka a faɗin jihar.

Kakakin rundunar ’yan sandan jihar, DSP Musa Muhammad, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin, ya ce rundunar ta fara gudanar da bincike kan lamarin.

A ranar Alhamis ne Gwamna Douye Diri ya gabatar da sabbin motocin aiki guda 31 ga kwamandojin jami’an tsaro na jihar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Bayelsa

এছাড়াও পড়ুন:

Zulum Ya Ba Da Tallafin Karatu Ga Mata ‘Yan Asalin Jihar Da Suka Samu Maki 250 A JAMB

Gwaman ya umarci mai rikon mukamin Shugaban ma’aikata, Hukumar bada tallafin karatu ta Jihar, ma’aikatar ilimi,da kuma kungiyar APWEN reshen Maiduguri cewar wadanda suka cika sharuddan da ake bukata ya dace a basu tallafin na karatu.

Lokacin taron ya taya Shugabnnin kungiyar amsu barin gado da kuma wadanda za su gaje su kan jajircewar da suka nuna wajen daukakalamarin da ya shafi kwararru ta bangaren Injiniya.

Da take gabatar da kasida mai taken, “Muhimmancin daukar nauyin da jawo hankalin’ ya’ya mata su yi karatun Injiniya da daukar abin a matsayin aiki a Nijeriya, ”Uwargidan gwamnan Borno,Dakta Habiba Babagana Zulum, ta lura da cewar daukar nauti wani lamari ne na yadda ake bunkasa ci gaban kwararru,inda ta yi nunu da cewa mata a Nijeriya sun samar da kashi 14 ne cikin 100 na ma’aikatan da suke da alaka da STEM, tace barin fiye da kashi 50 na yawan mutanen da basu da alaka da STEM wajen gina kasa wani abinda bai dace bane.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Zulum Ya Ba Da Tallafin Karatu Ga Mata ‘Yan Asalin Jihar Da Suka Samu Maki 250 A JAMB
  • Yawan Mutanen Da Suka Rasa Rayukansu A Ambaliyan Ruwa A Jihar Niger Na Najeriya Ya Kai 151
  • ‘Yan Wasan Kano Sun Rasu Sanadiyar Hadarin Mota Yayin Dawowa Daga Gasar Wasanni Ta Kasa
  • Jami’ar Jos Ta Samu Lambobin Zinare 14 A Gasar NUSSA, Yayin Da FUT Daura Ta Lashe Kofin Kwallon Kafa
  • Tsaro Ya Inganta A Zamfara, In Ji Gwamna Lawal Yayin Tattakin Zaman Lafiya Na Tarihi A Jihar
  • NAJERIYA A YAU: Yaya Girman Matsalar Rashin Tsaro A Shekaru Biyun Tinubu?
  • Ambaliyar ruwa ta kashe sama da mutum 50 a Neja
  • Kasar Iran, Da Kasashen Kungiyar BRICS Sun Gudanar Da Taro Kan Harkokin Tsaro A Mosco
  •  Kasar Chile Na Shirin Yanke Alakar Diplomasiyya Da “Isra’ila”