An gano gawar direba a cikin mota a Bayelsa
Published: 30th, May 2025 GMT
An gano gawar wani direban da yake tuƙi ƙarƙashin kamfanin sufuri da har yanzu ba a tantance shi ba a yankin Samphino na Yenagoa, babban birnin Jihar Bayelsa.
Daily Trust ta ruwaito cewa, an gano gawar direban matashin mai matsakaicin shekaru da sanyin safiyar Juma’a a cikin motarsa a mahaɗar Samphino da ke unguwar Kpansia a unguwar Yenagoa.
Wasu shaidun gani da ido da mazauna wurin da suka gano mutumin a wurin, an bayyana cewa, sun sanarwa da jami’an tsaro lamarin inda suka yi gaggawar ɗaukar mataki a wajen tare da killace wurin.
Mazauna yankin sun ce mai yiwuwa wasu da ake zargin ’yan fashi da makami ne suka harbe direban, a yunƙurin ƙwace motarsa ko wasu kayayyaki masu daraja.
Kodayake har yanzu ba a samu cikakkun bayanai ba, rahotannin da ba a tabbatar da su ba sun nuna cewa, mai yiwuwa maharan sun kira direban ne ta tikitin tafiya ta hanyar amfani da manhajar wayar salula ta Bolt, dabarar da ta ƙara nuna damuwa kan tsaron lafiyar direbobin da ke aiki da manhajar na direbobi a jihar.
Lamarin ya haifar da wani sabon tashin hankali a tsakanin mazauna garin da direbobin masu ɗaukar fasinja a Yenagoa, sa’o’i 24 bayan gwamnatin Jihar Bayelsa ta ba da gudummawar motocin sufuri aiki 31 ga jami’an tsaro daban-daban domin ƙarfafa ƙoƙarin yaƙi da miyagun ayyuka a faɗin jihar.
Kakakin rundunar ’yan sandan jihar, DSP Musa Muhammad, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin, ya ce rundunar ta fara gudanar da bincike kan lamarin.
A ranar Alhamis ne Gwamna Douye Diri ya gabatar da sabbin motocin aiki guda 31 ga kwamandojin jami’an tsaro na jihar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Bayelsa
এছাড়াও পড়ুন:
Ban Tsani Buhari Ba, Ina Sukar Sa Ne Kawai Kan Matsalar Tsaro – Ortom
Ya ce ya dinga ƙorafi ne domin gwamnatin Buhari ba ta ɗauki matakin da ya dace ba game da kashe-kashen da ake yi a Benuwe.
“Ba zan iya zama na yi shiru ina ci gaba da binne mutane ba. Dole ne na faɗi gaskiya,” in ji shi.
“Amma ban tsaya a magana kawai ba, gwamnatina ta kawo hanyoyin magance matsalar da muka ga za su taimaka.”
Ortom ya ƙara da cewa da gwamnatin Buhari ta karɓi shawararsa kuma ta yi aiki da ita, da matsalar tsaro a Benuwe ta ƙare.
Ya ce ya sha kokawa a lokacin, kuma shirye-shiryen da gwamnati ta kawo kamar Ruga ba su da amfani.
Ya ce ba wai rikici ne tsakanin makiyaya da manoma kawai ba, wasu daga cikin makiyaya suna kai wa ƙauyuka hari, suna kashe mutane, lalata gonaki, yi wa mata fyaɗe da aikata wasu laifuka.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp