An gano gawar direba a cikin mota a Bayelsa
Published: 30th, May 2025 GMT
An gano gawar wani direban da yake tuƙi ƙarƙashin kamfanin sufuri da har yanzu ba a tantance shi ba a yankin Samphino na Yenagoa, babban birnin Jihar Bayelsa.
Daily Trust ta ruwaito cewa, an gano gawar direban matashin mai matsakaicin shekaru da sanyin safiyar Juma’a a cikin motarsa a mahaɗar Samphino da ke unguwar Kpansia a unguwar Yenagoa.
Wasu shaidun gani da ido da mazauna wurin da suka gano mutumin a wurin, an bayyana cewa, sun sanarwa da jami’an tsaro lamarin inda suka yi gaggawar ɗaukar mataki a wajen tare da killace wurin.
Mazauna yankin sun ce mai yiwuwa wasu da ake zargin ’yan fashi da makami ne suka harbe direban, a yunƙurin ƙwace motarsa ko wasu kayayyaki masu daraja.
Kodayake har yanzu ba a samu cikakkun bayanai ba, rahotannin da ba a tabbatar da su ba sun nuna cewa, mai yiwuwa maharan sun kira direban ne ta tikitin tafiya ta hanyar amfani da manhajar wayar salula ta Bolt, dabarar da ta ƙara nuna damuwa kan tsaron lafiyar direbobin da ke aiki da manhajar na direbobi a jihar.
Lamarin ya haifar da wani sabon tashin hankali a tsakanin mazauna garin da direbobin masu ɗaukar fasinja a Yenagoa, sa’o’i 24 bayan gwamnatin Jihar Bayelsa ta ba da gudummawar motocin sufuri aiki 31 ga jami’an tsaro daban-daban domin ƙarfafa ƙoƙarin yaƙi da miyagun ayyuka a faɗin jihar.
Kakakin rundunar ’yan sandan jihar, DSP Musa Muhammad, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin, ya ce rundunar ta fara gudanar da bincike kan lamarin.
A ranar Alhamis ne Gwamna Douye Diri ya gabatar da sabbin motocin aiki guda 31 ga kwamandojin jami’an tsaro na jihar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Bayelsa
এছাড়াও পড়ুন:
Dalilin Da Ya Sa Hukumar NIWA Ta Fara Gyaran Hanyoyin Ruwa A Jihar Legsa
Manajar ofishin na NIWA, da ke a jihar ta Legas Injiniya Sarat Braimah ta bayyana cewa, tura ma’ikatan hukumar domin yin aikin, zai taimaka wajen gudanar da aikin a cikin inganci.
Kazalika, ya sanar da cewa, hakan zai kuma bayar da damar yin safarar kaya a cikin sauki da kuma safarar matafiya da ke bin hanyar ruwa ta yankin na Ikorodu.
“Mun yi nazari a cikin kwanciyar hankali kan yadda za a tabbatar da an cire fulawar da ke a cikin kasan ruwan ba tare da wata miskila ba tare da kuma bai wa jiragen ruwan damar yin zirga-zirgarsu a hanyoyin ruwan, ba tare da wata matsala ba, “ Inji Injiya Braimah.
“ Aikin ya wuce batun fannin samar da saukin yin sufurin jiragen ruwan har da tabbatar da an kiyaye janyo matsala ga ayyukan kamun Kifi a hanyoyin na ruwan, “ A cewar Inji Manajar.
Ta kara da cewa, babban shugabanmu na hukumar ta NIWA, Bola Oyebamiji, ne tuni ya riga ya bayar da kwangilar yin aikin, ba wai a jihar Legas kawai ba, har da a sauran hanyoyin ruwa da ke a sassan kasar.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA