Shugaban Hukumar Makamashin Nukiliya ta Iran ya bayyana cewa: Suna yin aiki ne bisa maslahar kasa, kuma ba su yarda da karbar umarni daga waje ba

Shugaban Hukumar Makamashin Nukiliya ta Iran, Mohammad Islami, ya ce Iran tana dogara ne kan manufofinta na kasa da kuma manufofinta na koli, kuma ba zata yarda wasu kasashen waje su tsara mata ko bata umurnin abin da zata yi ba.

Kalaman na Islami sun zo ne a lokacin da yake halartar wani taron juyayin tunawa da shahadar marigayi tsohon ministan harkokin wajen kasar Iran Hossein Amir-Abdollahian a jiya Asabar, wanda ya samu halartar manyan jami’an siyasa da na diflomasiyya.

A cikin jawabin nasa, Islami ya jaddada cewa asalin kasa da dabi’unta sune abubuwan da zasu tsara tafarkin al’umman Iran, kuma ta hanyar su ne suke neman samun hadin kai don gudanar da hidimar kasa da biyan bukatun al’ummar Iran.

Ya jaddada cewa: Jamhuriyar Musulunci ta Iran tana neman ci gaba da rike matsayinta a duniya ta hanyar da ta dace da ta samo asali daga manufofinta na kasa.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

An Gargadi Shugaban Amurka Dangane Da Fadawa Iran Da Yaki

Jaridar ;The HIL’ ta kasar Amurka wacce take bada labaran majalisa da siyasar gwamnatin Amurka ta gargadi gwamnatin shugaba Donal Trump kada ta sake irin kuskuren da shugaban kasar Iran Sadam Hussain yaki na fadawa kasar Iran da yaki, tare da tsammanin cewa a cikin yan kwanaki zai ga faduwar jaririyar gwamnatin kasar Iran a lokacin. Amma sai wankin hula ya kai masa dare, inda ya share shekaru 8 yana fafatawa da mutanen kasar Iran ba kuma tare da samun nasarar ba.

Jaridar ta kara da cewa Iran ba kasace wacce tana dab da faduwa ne sai aje a karasa faduwarta ba. Kasashen wacce kan mutanen kasar a hade yake a duk lokacinda na waje yayi kokarin mamayar kasar.

Labarin ya kara da cewa, jaridar ta bukaci gwamnatin Trump kada ta sake kuskuren da sadan Hussain yayi kuma ta kasar ta laluma ta hanyar diblomasiyya, don warware dukkan matsalolin da ke tsakaninsu da ita.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Gargadi Shugaban Amurka Dangane Da Fadawa Iran Da Yaki
  • Eslami : duk wani mataki da Iran ta dauka ya dogara ne kan manufofi da muradun kasar
  • Jonh Kerry Ya Ce HKI Ba Zata Iya Wargaza Cibiyoyin Nukliyar Kasar Iran ba
  • Arakci Ya Jaddada Muhimmanci Kawo Karshen Yakin Gaza Da Kuma Shigar Da Kayan Agaji
  • Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Gwamnatin Jamus Friedrich Merz
  • ‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu
  • Majiyoyin Iran Sun Musanta Da’awar Karya Kan Neman Ziyarar Amurka Zuwa Cibiyoyin Sojojinta
  • Iran Ta Ce: Amurka Ba Ta Fadan Hakikanin Abubuwan Da Aka Tattauna A Zamanta Iran 
  • Amurka Tana Takurawa JMI Don Biyan Bukatun HKI Na Ta Dakatar Da Shirinta Na Nukliya