Iran Tana Gudanar Da Ayyukan Cibiyoyin Makamashin Nukiliyarta Bisa Maslahar Kasarta Ne
Published: 25th, May 2025 GMT
Shugaban Hukumar Makamashin Nukiliya ta Iran ya bayyana cewa: Suna yin aiki ne bisa maslahar kasa, kuma ba su yarda da karbar umarni daga waje ba
Shugaban Hukumar Makamashin Nukiliya ta Iran, Mohammad Islami, ya ce Iran tana dogara ne kan manufofinta na kasa da kuma manufofinta na koli, kuma ba zata yarda wasu kasashen waje su tsara mata ko bata umurnin abin da zata yi ba.
Kalaman na Islami sun zo ne a lokacin da yake halartar wani taron juyayin tunawa da shahadar marigayi tsohon ministan harkokin wajen kasar Iran Hossein Amir-Abdollahian a jiya Asabar, wanda ya samu halartar manyan jami’an siyasa da na diflomasiyya.
A cikin jawabin nasa, Islami ya jaddada cewa asalin kasa da dabi’unta sune abubuwan da zasu tsara tafarkin al’umman Iran, kuma ta hanyar su ne suke neman samun hadin kai don gudanar da hidimar kasa da biyan bukatun al’ummar Iran.
Ya jaddada cewa: Jamhuriyar Musulunci ta Iran tana neman ci gaba da rike matsayinta a duniya ta hanyar da ta dace da ta samo asali daga manufofinta na kasa.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Ta Tabbatar Da Cewa Tana Iya Yakar Amurka Da HKI A Lokaci Guda
Tsohon babban kwamandan dakarun kare juyin juya halin musulunci wato IRGC ya bayyana cewa a yakin da JMI ta fafata a cikin watan da ya gabata , ya tabbata cewa JMI tana iya yaki da Amurka da HKI a lokaci guda.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Manjo Janar Mohsen Rezaei, yana fadar haka a lokacinda wata talabijin ta cikin gida take hira da shi a jiya Talata .
Labarin ya kara da cewa Janar Rezaei ya taba rike mukamin babban kwamandar rundunar IRGC jim kadan bayan nasarar juyin juya halin musulunci a shekara 1979.
Yace: Shahid Janar Qasem Sulaimani, Babban kwamandan rundunar Qudus ne ya fara furta zancen cewa , Iran tana da karfin fuskantar Amurka. Wannan kuma ya tabbata a yankin kwanaki 12 da aka dorawa kasar.
A halin yanzu dai Janar Rezaei yana cikin wadanda suke bawa Jagoran juyin juya halin musulunci shawara a kan al’amuran tsaro da siyasa.