Sulhu da ‘Yan Bindiga Ya Fi Zubar Da Jinin Ɗan Adam A Kaduna – Uba Sani Gazawar Gwamnatin Tinubu Ce Ke Haddasa Zubar Da Jini A Filato – Ƙungiyar Dattawan Arewa

Kazalika, wasu kwararrun, sun ayyna larurar, a matsayin cieon da ke yiawa mutane, kisan mummuke, musamman duba da cewa, bata nuna wasu alamu, idan an kamu da ita, sai dai kawai, ta ci gaba da zama barzana ga lafiyar ‘yan Adam, kamar kamuwa da masu larorin da suka hada da; mutuwar barin Jiki, lalata Koda da kuma rashin iya gani.

An kiyasta cewa, a daukacin fadin duniya, sama da mutane, biliyan 1.3 ke fama da ciwon, wanda kuma rabin adadin wannan alkaluman ne kacal, aka yi masu gwaji aka kuma duba lafiyarsu, yadda ya kamata.

Ciwaon na karuwa, musamman saboda yawan shekarun wadanda suka manyanta kuma larurar, ta karade daukacin fannin tattalin arziki da shafar kudin shiga.

Wani rahoton wani bincike na kiwon lafiya na duniya, ya nuna cewa, za a iya samu karuwar ciwon daga kaso 15 zuwa 20, inda wannan adadin, zai iya kai wa zuwa biliyan 15, a 2025.

Kungiyar da ke wayar da kai kan Hawan Jini ta duniya wato, WHL, ta sanya ciwon a cikin jiren cututtukan da ba a iya yada su.

Hakazalika, Kungiyar Gudanar da Bincike da Tsare-Tsare ta duniya kan kula da kiwon lafiya ta duniya, ta sanar da cewa, ciwon na daga cikin larurorin da ke ci gaba da zama kalubale ga rayuwar wadanda suka kamu da shi wanda kuma Nijeriya na daya daga ciki.

Wani abin tausayarwa shi ne, aka shafe shekaru, kan yadda ciwon ke kara yaduwa, wanda  karuwar aka kiyasta ta kai daga kaso 22 zuwa kaso  44, wanda hakan karuwar ta sha ban ban da a yankunan da ke kasar.

Taken taron na bana, yazo ne tamkar kan gaba ga kasar nan, musamman duba irin yanayin abincin da ake ci a gidajen kasar, kusan a shekaru biyu da suka gabata zuwa yanzu.

Bugu da kari, gidaje da dama a kasar, musamman na talakawa, na ci gaba da fuskantan matsin rayuwa ciki har da aukuwar hauhawan farashin kayan abinci, wanda hakan ya kara zafafa talauci da kuma fuskantar matsalolin rashin lafiya.

An dai shafe shekaru, Nijeriya na ci gaba da fuskantar dimbin kalubale na samun kulawar kiwon lafiyar ‘yan kasar yadda ya kamata, da kuma wawagegen gibin da ya auku a tsakanin mazauna Birane da na Karkara, wajen samun ababen more rayuwa da yin inshorar kiwon lafiyar su.

Koda yake dai, an dan samu wasu nasarori, amma duk da haka, wasu kalubalen, na nan kamar yadda suke a wasu guraren, kamar na wahalar samun magunguna kan farashi mai sauki.

Duba da irin halin fatara a kasar, musamman a tsakanin talakawa, magungunan kula da ciwon, na da matukar tsada, hatta magunnan kula da wasu larorin kamar dai,  ciwon Suga, ba kasafai, masu wannan larurar za su iya sayen magungunan ba, har da, kanannan ma’aikatan a kasar, da ke karbar  sabon mafi karancin Albashin ma’aikatan kasar na Naira 70.

Kazalika, tsadar magungunan, wani babban nauyi ne, akasari ga masu larurar wanda hakan ke tilasata su, dai bin ka’idojin da aka gindaya masu, na ci gaba da kula da lafiyarsu.

Wani rahoto ya bayyana cewa, tsadar magungunan ciwon a kasar nan, ya sha ban ban a wasu sassan kasar, misali, ma’aunin da ke yin gwaji ciwon Suga, ya karu, inda farashinta a yanzu, ya kai kimanin daga Naira 30,000 zuwa Naira 6,000.

Hakazalika, Hukumar Inshorar Kiwon Lafiya ta Kasa, na fuskantar karancin masu shiga cikin tsarin Inshora, duba da cewa, kusan kashi biyar a cikin dari na ‘yan kasar ne, kacal, suka shiga cikin tsarin.

Bugu da kari, ana ci gaba da samun karancin wayar da kan alumma kan ciwon, duba da cewa wasu alkaluma a 2021 sun bayyana cewa, kaso 29 na mutanen da aka yiwa gwajin ciwon, inda kuma kaso 12, aka dora su, kan shan magani wanda kuma kaso uku ne kawai, aka ci nasara na dakile ciwon.

Muna goyon bayan tunawa da ranar ciwon na duniya wadda kuma aka mayar da hankali, mai-makon ayi mata magani kawai, hatta da yadda za a kare aukuwarta da kuma karfafawa jama’a Guiwa kan yadda za su kula da lafiyarsu da kuma zuwa yin gwaji, kan lokaci, domin a gano, ko sun kamu da ciwo tare da kuma yin dubi, ga irin nau’in abincin da suke ci.

Ya zama wajibi, a mayar da hankali, wajen wayar da kan alumma, musaman ta hanyar zuwa yin gwajin  kiwon lafiya game da larurar wanda ta hanak ne, kawai za a iya dakile yaduwarta.

Wasu kwararu, sun bayar da shawarar cewa, ya zama wajbi, mutane sun rinka sanin irin abincin da ya kamata su ci, rage yin amfani da Gishiri, motsa jiki rage shan Barasa da kuma daina shan Taba Sigari.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Hawan jini kiwon lafiya

এছাড়াও পড়ুন:

 DRC: Joseph Kabila Ya Bayyana A Yakin Dake Karkashin Kungiyar M23

Rahotanni daga kasar ta DRC sun ambaci cewa an ga tsohon shugaban kasar Joseph Kabila a jiya Alhamis a garin Goma wanda yake a karkashin ikon ‘yan tawayen kungiyar M23.

Majiyar malaman addinin kirista a yankin ce ta sanar da cewa, ta gayyace shi ne domin ya shiga Tsakani a kawo karshen yakin da ake yi a yankin.

Bishop Joel Amurani ne ya sanar da cewa, su ne su ka gayyaci tsohon shugaban kasar wanda ya kasance akan karagar Mulki daga 2001 zuwa 2019.

A yayin ziyarar tashi a garin na Goma, Kabila ya gana da bangarori mabanbanta da su ka hada da malaman addinin yankin.

A can birnin Kinshasha, gwamnatin Felix Tshisekedi tana zargin Kabila da cewa yana goyon bayan kungiyar ta M23 wacce ta shimfida ikonta a gabashin kasar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Limamin Sallar Juma’ar Tehran Ya Jaddada Cewa: Babu Wanda Zai Dakatar Da Iran Tace Sinadarin  Uranium
  • Za a ɗauke ruwan famfo na tsawon mako 2 a Abuja 
  • Cutar Kwalara Ta Yadu A Sudan Baya Ga Matsalar Tashe-Tashen Hankulan Da Suke Ci Gaba Da Yuduwa A Kasar
  • Hana shigar da abinci da Isra’ila ta yi zuwa Gaza ‘laifi ne na yaki’: MDD
  • Burkina Faso ta musanta zargin kisan kiyashi da ake yi a arewacin kasar
  • Koshin Lafiyar Yaran Kasar Sin Na Kara Inganta
  •  DRC: Joseph Kabila Ya Bayyana A Yakin Dake Karkashin Kungiyar M23
  • Mutanen da suka mutu a ambaliyar Neja sun ƙaru zuwa 88 —NSEMA
  • Masu Bincike Na Sin Sun Cimma Sabon Sakamako A Fannin Saurin Sadarwa Tsakanin Tauraron Dan Adam Da Doron Duniya