Nukiliya : Iran ta kirayi mai kula da harkokin Ostiriya da ke birnin Tehran kan wasu kalamai na tsokana
Published: 31st, May 2025 GMT
Ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ta kirayi babbar mai kula da harkokin kasar Ostiriya da ke birnin Tehran domin nuna rashin amincewa da zarge-zargen data danganta da na ‘’tsokana” da hukumar leken asirin cikin gidan kasar ta Turai ta yi dangane da shirin nukiliyar Iran na zaman lafiya.
Shugaban ofishin sashen yammacin Turai na ma’aikatar harkokin wajen Iran Alireza Molaqadimi ya gayyaci Michaela Pacher a ranar Juma’a, inda ya nuna bacin ran kasar iran game da zarge-zargen.
A cikin rahotonta na shekara-shekara kan barazanar da duniya ke fuskanta, hukumar leken asiri ta kasar Ostiriya (DSN) ta yi ikirari a ranar Litinin cewa Iran na ci gaba da aiwatar da shirin kera makaman nukiliya tare da fadada karfinta na makamai masu linzami.
M. Molaqadimi ya yi watsi da wannan zargi mara tushe, yana mai jaddada cewa ya sabawa rahotanni da dama da hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya IAEA ta fitar.
Ya ce shirin nukiliyar kasar Iran ya yi daidai da alkawurran da kasar ta doka karkashin yarjejeniyar hana yaduwar makaman nukiliya ta NPT, ya kuma yi kira ga gwamnatin Ostiriya da ta yi bayani a hukumance kan wannan batu.
Tun da farko dama a ranar Juma’a, kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran, Esmail Baghai, ya yi watsi da rahoton da ya ce na “karya ne kuma marar tushe” da hukumar leken asirin ta Austria ta fitar.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Aragchi: Shirin Nukliyar Kasar Iran Na Tafiya Kan Fahintar Rashin Amincewa Da Babakere
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya bayyana cewa JMI ta gina shirinta na makamashin nukliya ne kan fahinta da kuma kundin tsarin mulkin kasar wanda yayi tir da mamaya da kuma babakere.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto ministan yana fadar haka a safiyar yau Asabar a hubbaren Imam Ruhullah Al-khomaini (q) wanda ya kafa JMI. Ministan da sauran manya-manyan ma’aikata a ma’aikatar harkokin wajen kasar sun je hubbaren Imam ne don jadda bai’a ko alkawali da shi kan tafiya a kan tafarkin da ya barsu a kai.
A cikin wani wuri a Jawabinsa Ministan ya kara da cewa a cikin kundin tsarin mulkin JMI ya zo kan cewa Iran ba zata danne wata kasa ba kuma ba zata amince da danniyaba, hakama ba zata zalunci wata kasa ba kuma ba zata yarda a zalunceta ba.
Ya ce abinda gwamnatin kasar Amurka take son tayiwa JMI shi ne danniya da zalunci, Kalmar kada ku ce makamacin Uranium kanta danniya ce. Su sun amincewa kansu su mallaki makaman nukliya amma ba zasu amincewa wata kasa ta ma tashe makamashin uranium wanda yarjeniyar NPT ta amince masu su tace ba. Don haka wannan baa bin amincewa ne ga JMI ba.