Kotu ta ci su El-Rufa’i tarar miliyan 900
Published: 28th, May 2025 GMT
Babbar kotun tarayya da ke zamanta a Kaduna a ranar Talata ta ci tsohon Gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-Rufa’i da karin wasu mutum biyar tarar Naira miliyan 900.
Kotun dai ta ci tarar tsohon Gwamnan kan laifin kamawa tare da tsare dattawan kabilar Adara da ke jihar a shekara ta 2019.
Da take zartar da hukuncin a ranar Talata, Alkalin kotun, Mai Shari’a Hauwa’u Buhari, ta amince da bukatar Awemi Dio Maisamari da Karin wasu dattawan kabilar ta Adara su takwas wadanda aka kama bayan kisan basarakensu, Dr Raphael Maiwada Galadima.
Kotun dai ta yi fatali da da’awar wadanda ake kara kan cewa ba ta da hurumin sauraron karar, inda duk da haka ta yanke hukuncin.
An dai gurfanar da El-Rufa’i ne a kashin kansa ba a matsayin Gwamna ba, inda kotun ta ce ta same shi da laifi kan bayar da umarnin yin kamen.
Lauyar masu shigar da karar, Gloria Mabeiam Ballason Esq, ta bayyana hukuncin a matsayin wani babbar nasara kan masu amfani da kujerar mulkin ta hanyar da ba ta dace ba.
An dai kama tare da tsare dattawan na kabilar Adara ne a shakara ta 2019 yayin wani taro da El-Rufa’i ya gayyace su a shekara ta 2019, jim kadan bayan sacewa da kuma kisan da aka yi wa basaraken.
A yayin taron, rahotanni sun ce El-Rufa’i y aba jami’an tsaro umarnin kama Maisamari, wanda shi ne shugaban Kungiyar Ci Gaban Adara, inda ya bayyana shi a matsayin barazanar tsaro a yankin Kajuru.
Dattawan da aka kama dai sun hada da tsohon Kwamishina kuma tsohon jami’in dan sanda, inda aka tsare su har na tsawon watanni, kafin daga bisani babban lauyan gwamnati ya bayar da umarnin sakin su tun da ba a tuhume su a kotu ba.
To sai dai lauyoyin wadanda ake kara sun ki su ce uffan a kan hukuncin kotun.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Babbar Kotu
এছাড়াও পড়ুন:
NDLEA ta kama ɗan Indiya da ƙwaya ta Naira biliyan 3 a Legas
Hukumar Hana Sha da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi ta Najeriya (NDLEA) ta kama wani ɗan ƙasar Indiya tare da wasu mutane uku bisa zargin shigo da ƙwayoyin Tramadol da aka ƙiyasta darajarsu ta kai naira biliyan uku (N3bn) zuwa cikin ƙasar.
A cewar NDLEA, wannan shi ne kamen ƙwayoyi mafi girma da hukumar ta yi a cikin shekarar nan, lamarin da ke nuna yadda safarar miyagun ƙwayoyi ke ƙaruwa a ƙasar.
Peter Obi ya kai wa Obasanjo ziyara An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a NijarCikin wata sanarwa da hukumar ta fitar, ta bayyana cewa jami’anta sun kama mutanen ne a filin jirgin sama na Murtala Muhammad da ke Legas, bayan sun samu bayanan sirri da suka taimaka wajen gano su.
NDLEA ta bayyana cewa ƙwayoyin Tramadol ɗin da aka gano an shigo da su ne cikin kwalaye a matsayin maganin multivitamins, yayin da ake ƙoƙarin fitar da su daga filin jirgin a wasu manyan motoci.
“Ƙwayoyin da aka kama ba su da wata alaƙa da amfani na lafiya, waɗanda aka shigo da su a ɓoye a matsayin maganin rage kasala da ƙara kuzari (multivitamins),” in ji sanarwar NDLEA.
Rahotanni sun nuna cewa a da likitoci na bayar da Tramadol ne don rage zafi da raɗaɗin ciwo, amma yanzu ta zamo annoba musamman a tsakanin matasa, wadda ke haddasa mummunan maye da illa ga lafiya.
Hukumar ta nuna damuwa game da yadda yawan masu amfani da Tramadol ke ƙaruwa ba wai a Najeriya kaɗai ba, har ma a wasu ƙasashen Afirka, duk da illolin da ƙwayar ke haddasawa, kamar matsalolin taɓin hankali ko ma rasa rai gaba ɗaya.