Shugaban kasar Amurka Donald Trump ya bayyana cewa: Suna gudanar da kyakkyawar tattaunawa da Iran

Shugaban Amurka Donald Trump ya bayyana cewa: Amurka na tattaunawa da Iran sosai kan Shirin makamashin nukiliyarta.

Donald Trump ya fada a ranar Laraba cewa:  “Ya damu da abin da ke faruwa a Ukraine, kuma bai sani ba ko Putin na son kawo karshen yakin,” a cewar gidan talabijin na Al Jazeera.

Dangane da tattaunawar da aka yi da Iran, Trump ya ce: “Suna tattaunawa mai kyau da Iran.”

Trump ya ce: Dole ne bangarorin Gaza su amince da takardar da Steve Witkoff wakilin Amurka na musamman a yankin Gabas ta Tsakiya ya gabatar.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Ministan Harkokin Wajen Iran Yayi Tir Da Jakadan Burtaniya A Amurka Dangane Da Tashe Uranim A Kasar

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Arachi ya tir da kalaman jakadan Burtaniya a Washington,  Peter Mandelson, wanda yayi kira ga Amurka kada ta taba barin Iran ta tashe makamashin Uranium a cikin kasar. Ministan ya kara da cewa Mandelson yana son ya karkatar da tattaunawan da Iran take da Amurka.

Ya kuma kara da  cewa Iran ce take sanar da kasashen turai yadda tattaunawa tsakanin Amurka da ita ke tafiya, tun Amurka ta waresu daga tattaunawar. Yace, idan har haka ne tunanin kasar Burtaniya wacce take cikin kasashen da suka sanyawa yarjeniyar JCPOA hannu, yana ganin mai yuwa Iran ta dakatar da sanar da su abubuwan da ke tafiya a tattaunawar.

Ya zuwa zagaye har 5 wadanda Amurka da Iran suka tattaunawa dangane da shirin Nukliya na Iran dai, Iran ta nuna mata cewa hanata tace uranium a cikin gida, jan layi ne wanda ba zata amince da shi ba, kuma ya sabawa yarjeniyar NPT wacce ta bawa Iran wannan damar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mai Ba Da Shawara Ga Jagora Ya Mayar Da Martani Ga Barazanar Trump Kan Cibiyoyin Nukiliyar Iran
  • Shugaban Amurka Ya Ce: Kasarsa Da Iran Suna Kyakkyawar Tattaunnawa A Tsakaninsu                                                                                                                       
  • Red Crescent ta Iran da Red Cross ta Saliyo sun cimma yarjejeniyoyi da dama a tsakaninsu
  • Araghchi: “Ba ma wasa game da batun inganta uranium, wanda hakkin al’ummar Iran ne”
  • Trump Ya Gargadi Natanyahu Kan Kokarin Hana Tattaunawa Da Iran Tafiya
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Yayi Tir Da Jakadan Burtaniya A Amurka Dangane Da Tashe Uranim A Kasar
  •  Arakci: Idan Birtaniya Ta Ci Gaba Da Batun Dakatar Da Tace Uranium A Iran, Za A Dakatar Da Tattaunawa Da Ita
  • Shugaban Kasar Iran Ya Kai Ziyara Zuwa Kasar Oman don Karfafa Kyakkyawar Alakar Kasashen Biyu
  • Ko Mene Ne Dalilin Da Ya Sa Trump Ya Gujewa Yaki Da Yemen Har Ya Kai Ga Fusata Kawayen Amurka