Yemen: Matukar Gaza Tana Fuskantar Yaki, To Babu Tsaro A HKI
Published: 30th, May 2025 GMT
Miliyoyin Mutanen Kasar Yemen sun yi gangamin a jihohi 14 na fadin kasar domin nuna goyon bayan Gaza.
A cikin birnin Sanaa an yi taron ne a dandalin Saba’in a yau juma’a da mahalartansa suka rika bayar da taken nuna kin amincewa da halin da mutanen Gaza suke ciki na yunuwar da aka jefa su da kuma ci gaba da yi musu kisan kiyashi.
Bugu da kari masu gangamin sun rika bayyana cewa; Taimakawa mutanen Gaza, kai wa manzon Allah cika-makin annabawa, manzon Allah ( s.a.w) dauki ne, kuma taimakon masallacin Kudus ne.
Haka nan kuma masu gangamin na birnin Sanaa sun yi tir da kutsa masallacin kudus da yahudawa ‘yan share wuri zauna su ka yi. Har ila yau, mutanen sun bayyana cewa; Fitowar da su ka yi, nau’in jihadi ne da kuma amsa umarnin Allah da yin jihadi a tafarkinsa da kuma neman yardarsa.
Baya ga birnin San’aa an kuma yi wasu gangamin a cikin birane 14 na fadin kasar ta Yemen.
Kasar Yemen dai tana ci gaba da kai wa manufofin HKI hare-hare saboda ci gaba da tafka laifukan yaki da take yi a Gaza, tare da jaddada cewa ba za su daina ba har idan an kawo karshen yakin na Gaza.
Sojojin Yemen ta bakin kakakinsu Janar Yahya Sari, sun sanar da kakaba takunkumi akan tasoshin jiragen sama da na ruwa na HKI. Daga lokaci zuwa lokaci sojojin na Yemen suna harba makamai masu linzami akan filin saukar jirgin sama na “Ben-Gorion” da kuma tashar jirgin ruwa ta “Haifa”.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
ALGON ta karrama Gwamna Buni da lambar yabo kan kawo ci gaba a Yobe
Ƙungiyar shugabannin ƙananan hukumomin Jihar Yobe (ALGON) ta karrama Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni, da lambar yabo ta karramawa bisa himmar ayyukan raya ƙasa da gwamnatinsa ke gudanarwa a faɗin jihar.
Karramawar, wacce aka bayyana a matsayin irinta ta farko a tarihin Jihar Yobe, shugabannin ƙananan hukumomi 17 na jihar suka ba da ita ga gwamna.
Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabala Sojoji sun harbe mayaƙan ISWAP 8 a BornoDa yake jawabi, shugaban ƙungiyar ALGON a Jihar Yobe, kuma shugaban ƙaramar hukumar Damaturu, Alhaji Bukar Adamu, ya yaba da yadda Gwamna Buni yake gudanar da harkokin mulki na bai ɗaya. Ya ce nasarorin da aka samu sun haɗa da fannoni na ilimi, noma, kiwon lafiya, kasuwanci, da samar da ababen more rayuwa.
“Babu wani sashe a jihar da aka bari a baya a cikin ayyukan ci gaban da Gwamna Mai Mala Buni ke aiwatarwa,” in ji Adamu.
A nasa martanin, Gwamna Buni, wanda mataimakinsa, Alhaji Idi Barde Gubana, ya wakilta, ya karɓi karramawar a matsayin “hanyar mayar da martani mai ƙarfi” da ke tabbatar da tasirin gwamnatinsa a matakin farko.
Ya kuma yi alƙawarin ci gaba da ƙoƙarin kai Yobe matsayin jiha da za ta iya gogayya da takwarorinta a fagen ci gaban ƙasa.
Wakilinmu ya ruwaito cewa taron ya samu halartar manyan jami’an gwamnati, ’yan siyasa daga ciki da wajen jihar, da kuma sarakunan gargajiya.