HausaTv:
2025-06-01@02:01:36 GMT

Yemen: Matukar Gaza Tana Fuskantar Yaki, To Babu Tsaro A HKI

Published: 30th, May 2025 GMT

Miliyoyin Mutanen Kasar Yemen sun yi gangamin a jihohi 14 na fadin kasar domin nuna goyon bayan Gaza.

A cikin birnin Sanaa an yi taron ne a dandalin Saba’in a yau juma’a da mahalartansa suka rika bayar da taken nuna kin amincewa da halin da mutanen Gaza suke ciki na yunuwar da aka jefa su da kuma ci gaba da yi musu kisan kiyashi.

Bugu da kari masu gangamin sun rika bayyana cewa; Taimakawa mutanen Gaza, kai wa manzon Allah cika-makin annabawa, manzon Allah ( s.a.w) dauki ne, kuma taimakon masallacin Kudus ne.

Haka nan kuma masu gangamin na birnin Sanaa sun yi tir da kutsa masallacin kudus da yahudawa ‘yan share wuri zauna su ka yi. Har ila yau, mutanen sun bayyana cewa; Fitowar da su ka yi, nau’in jihadi ne da kuma amsa umarnin Allah da yin jihadi a tafarkinsa da kuma neman yardarsa.

Baya ga birnin San’aa an kuma yi wasu gangamin a cikin birane 14 na fadin kasar ta Yemen.

Kasar Yemen dai tana ci gaba da kai wa manufofin HKI hare-hare saboda ci gaba da tafka laifukan yaki da take yi a Gaza, tare da jaddada cewa ba za su daina ba har idan an kawo karshen yakin na Gaza.

Sojojin Yemen ta bakin kakakinsu Janar Yahya Sari, sun sanar da kakaba takunkumi akan tasoshin jiragen sama da na ruwa na HKI. Daga lokaci zuwa lokaci sojojin na Yemen suna harba makamai masu linzami akan filin saukar jirgin sama na “Ben-Gorion” da kuma tashar jirgin ruwa ta “Haifa”.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sojojin Yemen Sun Hana Jigilar Jiragen Sama A Isra’ila Tare Da Firgita ‘Yan Sahayoniyya

Sojojin Yemen sun kai hari kan filin jirgin saman Ben Gurion da makami mai linzami lamarin da ya tarwatsa cinkoson jama’a a filin jirgin

Sojojin Yemen sun sanar da kai farmakin soji kan filin tashi da saukan  jiragen saman Ben Gurion tare da yin barazanar ci gaba da toshe hanyoyin zirga-zirgar jiragen sama da na ruwa na haramtacciyar kasar Isra’ila muddin bata kawo karshen killace Zirin Gaza da ta yi ba.

Kakakin rundunar sojin kasar Yemen Birgediya Janar Yahya Sari’e ya tabbatar da cewa: Wannan farmakin ya samu nasarar cimma burin da aka sanya a gaba, wanda ya tilastawa miliyoyin ‘yan sahayoniyya ‘yan mamaya tserewa zuwa maboyar karkashin rami tare da dakatar da zirga-zirgar jiragen sama a filin jirgin.

Sari’e ya kara da cewa: Wannan farmakin yana tabbatar da ci gaba da gudanar da ayyukan sojojin Yemen na wajibin addini, kyakkyawar dabi’a da jin kai da kuma dan Adamtaka ga ‘yan uwansu na Falastinu har sai an daina kai hare-haren wuce gona da iri kan Falasdinawa da killace su.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hadin Gwiwar Sin Da Kasashe Masu Tasowa Ya Dade Da Zama Kan Gaba A Bangaren Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Waje
  • Kungiyar Hamas Ta Bukaci Masu Shiga Tsakani Amurkawa Su Gamsar da Ita Za’a Dakatar Da Yaki A Gaza
  • Limamin Sallar Juma’ar Tehran Ya Jaddada Cewa: Babu Wanda Zai Dakatar Da Iran Tace Sinadarin  Uranium
  • Cutar Kwalara Ta Yadu A Sudan Baya Ga Matsalar Tashe-Tashen Hankulan Da Suke Ci Gaba Da Yuduwa A Kasar
  • Macron : Faransa za ta iya sanya takunkumi ga gwamnatin Isra’ila matukar ba ta kawo karshen killace Gaza ba
  • Hana shigar da abinci da Isra’ila ta yi zuwa Gaza ‘laifi ne na yaki’: MDD
  • Mutanen da suka mutu a ambaliyar Neja sun ƙaru zuwa 88 —NSEMA
  • Sojojin Yemen Sun Hana Jigilar Jiragen Sama A Isra’ila Tare Da Firgita ‘Yan Sahayoniyya
  •  Yemen: Wuce Gona Da Irin HKI Ba Zai Sauya Mana Ra’ayi Akan Ci Gaba Da Taimaka Wa Gaza Ba