Aminiya:
2025-09-18@06:59:42 GMT

’Yan sanda sun kama wanda ake zargi da kisan matar aure a Kano

Published: 27th, May 2025 GMT

’Yan sanda sun kama babban wanda ake zargi da kisan wata matar aure masi shekaru 22 a gidanta da ke unguwar  Tsamiyar Duhuwa da ke yankin Farawa a Jihar Kano.

A ranar 6 ga watan Afrilu ne aka tsinci gawar matar mai suna Rumaisa Haruna, ne a gidanta bayan an yi mata kisan gilla.

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kano ta sanar kama wanda ake zargin mai shekaru 35 mazaunin unguwar Madatai ne a ranar 23 ga watan Mayu ta hanyar binciken sirri.

Kakakin rundunar, Abdullahi Haruna Kiyawa, ya ce wanda ake zargin ya amsa laifin a hannun ’yan sanda, inda ya bayyana cewa ya shiga gidan wadda aka kashe ne ya shake ta, sa’annan ya soka mata wuka a wuya, lamarin da ya yi sanadin mutuwarta.

Gwamnatin Kano za ta sabunta masallacin da aka kona masallata 23 a kan N150m Amarya ta kashe uwargida da wuka a Katsina

Sanarwar ’yan sandan ta ce: “Za a gurfanar da wanda ake zargi a gaban kotu bayan kammala bincike.”

Lamarin mai ban tausayi ya bayyana ne lokacin da mijin matar mai suna Ibrahim Mohammed, ya tsinci gawarta da mummunan rauni a wuyanta. An garzaya da ita asibiti inda aka tabbatar da mutuwarta.

Rundunar ’yan sandan ta yaba wa jami’anta masu bincike saboda kwarewarsu da kuma jajircewarsu wajen cafke wanda ake zargi, inda ta kara da cewa ana ci gaba da bincike don tabbatar da an yi cikakken adalci.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Farawa matar aure Tsamiyar Duhuwa wanda ake zargi

এছাড়াও পড়ুন:

 Gaza: HKI Tana Ci Gaba Da Yi Wa Falasdinawa  Kisan Kiyashi A Gaza

Rahotannin da suke fitowa daga Gaza sun ce, fiye da Falasdinawa 35 ne su ka yi shahada daga Safiyar yau Laraba zuwa  tsakiyar rana,sanadiyyar hare-haren da HKI take kai wa.

Hakan tana faruwa ne a daidai lokacin da ma’aikatar  kiwon lafiya a Gaza ta yi gargadi akan cewa asibitocin yankin sun kusa daina aiki baki daya.

Tashar talabijin din ‘aljazira’ ta kasar Qatar ta ce,adadin wadanda su ka yi shahada har zuwa marecen yau sun kai 51,38 daga cikinsu a cikin birnin Gaza kadai.

A gefe daya rahoton tashar talbijin din ta ‘aljazira’ ya  bayyana cewa; HKI ta yanke hanyoyin sadarrwa na “Internet’ a fadin Gaza, haka nan kuma ta hana hukumar lafiya ta duniya ( w.h.o) shigar da makamashi cikin asibitocin yankin.

Ma’aikatar kiwon lafiya a Gazan ta kuma ce, matukar ba a bari aka shigar da makamashi cikin asibitocin yankin ba, to komai zai tsaya.

A can yankin yammacin kogin Jordan kuwa, sojojin HKI sun rushe gidajen Falasdinawa 40 a garin ‘Assir” a yau Laraba kadai.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Ma’aikatar Shari’ar Iran Ta Sanar Da Rataye Dan Leken Asirin Hukumar Mossad Ta Isra’ila September 17, 2025 Hamas Ta Karyata Gwamnatin Mamayar Isra’ila Kan Shirga Karya Don Kare Muggan Manufofinta September 17, 2025 Iran Ta Bayyana Abubuwan Da Bata Amince Da Su Ba A Jawabin Bayan Taro Na Kungiyar OIC A Birnin Doha September 17, 2025 Chadi:  Majalisa ta amince a baiwa shugaban kasa  damar ci gaba da Mulki har karshen rayuwa September 17, 2025 Iran Ta Bukaci Musulmi Su Goyi Bayan Yunkurin Kasa da Ka Na Kauracewa Isra’ila September 17, 2025 Kwamitin bincike na MDD ya zargi Isra’ila da aikata “kisan kare dangi” a Gaza September 17, 2025 Iran da Saudiyya sun bukaci hadin kan Musulmi game da halin da ake a yankin September 17, 2025 Duniya na tir da sabon farmakin Isra’ila kan Gaza September 17, 2025 Akalla Falasdinawa 78 ne sukayi shahada a hare-haren Isra’ila a Gaza September 17, 2025 Akalla Falsdinawa 78 Ne Suka Yi Shahada A Yau A Gaza. September 16, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Gaza: HKI Tana Ci Gaba Da Yi Wa Falasdinawa  Kisan Kiyashi A Gaza
  • ‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja
  • Kwamitin bincike na MDD ya zargi Isra’ila da aikata “kisan kare dangi” a Gaza
  • ’Yan sanda sun kama mutum 6 kan satar zinarin N109m a Kebbi
  • Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne
  • Sin Ta Gano Wani Dutse Mai Sassaka Na Daular Qin A Kan Tsaunin Qinghai-Tibet
  • ‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Kan Masallata Tare Da Garkuwa Da Mutane A Zamfara
  • ’Yan sanda sun sasanta rikicin asibitin AKTH da KEDCO
  • Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ya Fara Shan Ƙasa, Sun Yi Garkuwa Da Masallata A Zamfara 
  • An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar