Aminiya:
2025-05-27@18:11:39 GMT

’Yan sanda sun kama wanda ake zargi da kisan matar aure a Kano

Published: 27th, May 2025 GMT

’Yan sanda sun kama babban wanda ake zargi da kisan wata matar aure masi shekaru 22 a gidanta da ke unguwar  Tsamiyar Duhuwa da ke yankin Farawa a Jihar Kano.

A ranar 6 ga watan Afrilu ne aka tsinci gawar matar mai suna Rumaisa Haruna, ne a gidanta bayan an yi mata kisan gilla.

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kano ta sanar kama wanda ake zargin mai shekaru 35 mazaunin unguwar Madatai ne a ranar 23 ga watan Mayu ta hanyar binciken sirri.

Kakakin rundunar, Abdullahi Haruna Kiyawa, ya ce wanda ake zargin ya amsa laifin a hannun ’yan sanda, inda ya bayyana cewa ya shiga gidan wadda aka kashe ne ya shake ta, sa’annan ya soka mata wuka a wuya, lamarin da ya yi sanadin mutuwarta.

Gwamnatin Kano za ta sabunta masallacin da aka kona masallata 23 a kan N150m Amarya ta kashe uwargida da wuka a Katsina

Sanarwar ’yan sandan ta ce: “Za a gurfanar da wanda ake zargi a gaban kotu bayan kammala bincike.”

Lamarin mai ban tausayi ya bayyana ne lokacin da mijin matar mai suna Ibrahim Mohammed, ya tsinci gawarta da mummunan rauni a wuyanta. An garzaya da ita asibiti inda aka tabbatar da mutuwarta.

Rundunar ’yan sandan ta yaba wa jami’anta masu bincike saboda kwarewarsu da kuma jajircewarsu wajen cafke wanda ake zargi, inda ta kara da cewa ana ci gaba da bincike don tabbatar da an yi cikakken adalci.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Farawa matar aure Tsamiyar Duhuwa wanda ake zargi

এছাড়াও পড়ুন:

Amarya ta kashe uwargida da wuka a Katsina

’Yan sanda sun tsare wata matar aure kan zargin ta da kashe kishiyarta a Ƙaramar Hukumar Daura da ke Jihar Katsina.

Mai magana da yawun ’yan sanda a Jihar Katsina, DSP Abubakar Aliyu, ya bayyana cewa matar ta yi wa uwargidarta kisan gilla ne bayan wata hatsaniya da aka samu a tsakaninsu, wanda ya ƙazance har ya kai ga kisa.

Amaryar, mai shekara 23 a duniya, ta yi wa uwargida wannan aika-aika ne ranar Lahadi a unguwar Sabon Gari, daura da Makaranta Firamare ta Daɗi.

DSP Abubakar Aliyu, ya ce a ranar ce bayan mijinsu ya dawo daga kasuwa ya kai ƙara Babban Ofishin ’Yan Sanda da ke Daura cewa ya iske uwar gidansa kwance a cikin jini.

An yanke wa wanda ya yi wa agolarsa fyaɗe ɗaurin rai-da-rai  Jama’ar gari sun kashe DPO, sun ƙona ofishin ’yan sanda a Kano  NAJERIYA A YAU: Matsalolin Da Suke Tarnaki Ga Kananan Yara A Najeriya Da Hanyoyin Magance Su

“Ya bayyana cewa an sossoka wa matar tasa wuƙa, lamarin da ya sa DPO ya jagoranci jami’ansa suka je aka kai ta Babban Asibitin Tarayya na Daura, inda likita ya bayyana musu cewa rai ya riga ya yi halinsa,” in ji DSP Abubakar Aliyu.

Ya bayyana cewa a yayin bincike, an kama kishiyar amaryar, kuma ta amsa cewa ita ce ta kashe uwargidar bayan sun ba hamata iska saboda wani saɓani da suka samu.

Kwamishinan ’yan sanda na Jihar Katsina, Bello Shehu ya bayyana cewa za a gurfanar da wadda ake zargin a kotu bayan an kammala bincike.

Ya kuma buƙaci jama’a da su guji hawa dokin zuci ko ɗaukar doka a hannunsu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Kano za ta sabunta masallacin da aka kona masallata 23 a kan N150m
  • Yadda kotu ta yanke wa wanda ya kona mutane a cikin masallaci hukuncin rataya a Kano
  • Amarya ta kashe uwargida da wuka a Katsina
  • Jama’ar gari sun kashe DPO, sun ƙona ofishin ’yan sanda a Kano 
  • Yadda Rikici Ya Yi Sanadin Kashe DPO A Kano
  • Kwastam ta kama Tiramol ta N150m, ta miƙa wa NAFDAC a Kano
  • Kotu Ta Yanke Hukuncin Kisa Ga Wanda Ya Kona Masallata A Kano
  • An kashe matashi yayin rikici a ƙauyukan Kano
  • Afirka Ta Kudu Ta Zargi Shugaban Kasar Amurka Da  Rashin Dalili Akan Zargin Yi Wa Fararen Fatar Kasar Kisan Kiyashi