HausaTv:
2025-07-27@04:12:53 GMT

Iran Da Iraki Sun Jaddada muhimmancin Tsaron Kan Iyakokin Kasashensu

Published: 16th, February 2025 GMT

Mataimakin ministan harkokin wajen Iran ya ce: Tuntubar juna tsakanin Iran da Iraki ya zama wajibi don inganta matakan tsaro tsakanin kasashen biyu

Mataimakin ministan harkokin wajen Iran kan harkokin siyasa Majid Takht Rawanji ya jaddada da cewa: Ziyarar da ya kai zuwa Iraki ta zo ne bisa tsarin tuntubar juna ta fuskar siyasa da aka saba yi tsakanin kasashen biyu.

Rawanji ya kara da cewa: Iran da Iraki sun tattauna kan batutuwan da suka shafi tsaro tsakaninsu a matsayinsu na kasashen ‘yan’uwa da musulmi, tare da jaddada muhimmancin hadin kai da hadin gwiwa don tabbatar da zaman lafiya a yankin.

Ya kara da cewa, tsaron yankin shi ne babban fifiko ga kasashen Iran da Iraki, wanda ya bukaci ci gaba da tuntubar juna da kuma yin aiki tare a matakai daban daban na kasashen biyu.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Iran da Iraki

এছাড়াও পড়ুন:

Jagora: Za’a Gaggauta Ci Gaba A Ilmi Da Fasahar Tsaron Sojojin Kasar

Jagoran juyin juya halin musulunci Imam Sayyid Aliyul Khaminae ya bayyana cewa JMI zata gaggauta ci gaba a fasahar tsaron kasa da kuma fasahar zamani a dukkan fagage bayan yakin kwanaki 12 da HKI da Amurka.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Jagoran yana fadar haka a cikar kwanaki 40 da shahadar manya-manyan kwamandojin sojojin kasar da kuma masana fasahar Nukliya a kasar. Jagoran ya kara da cewa dukkan ilmomi tsaron kasa da kuma fasaha za su cilla da saura don samun ci  gaba.  A sakon da jagoran ya aikawa mutanen kasar ya yi tir da hare-haren da HKI da kuma Amurka suka kaiwa kasar Iran, sannan yay aba da sojojin kasar Iran kan duka mai karfin da suka yiwa makiya.

Yace: Babu shakka an yi rashin manya-manyan kwamandojin sojojin kasar Kamar Bakiri salami, Rashid Hajizadeh shadmani da sauransu, abun yayi mana nauyi, hakama mun rasa masana fasahar Nukliya Tehranchi da Abbasi, amma kuma muna godiyar All..makiya basu cimma mummunan manufofinsu a kan Iran ba.  Yace: Manufar HKI na maida kasar Iran baya ya kasa kaiwa ga nasara,.  A ranar Jumma’a 13 ga watan yunin da ya gabata ne jiragen yakin HKI suka kai hare-hare a wurare da dama a cikin nan birnin Tehran. Inda suka kai wadannan manya-manyan mutane ga shahada. Sannan kafin kasar Yakin wanda suka nemi a tsaida shi sun dauki darasi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jagora: Za’a Gaggauta Ci Gaba A Ilmi Da Fasahar Tsaron Sojojin Kasar
  • Tallafin Lafiya: Ƙungiyar Rotary Ta Raba Kayan Haihuwa kyauta Ga Mata Masu Juna Biyu  A Kaduna
  • Araqchi Ya Jaddada Cewa; Karfin Kariya Da Makamai Masu Linzamin Iran Ne Suka Tilastawa Makiya Neman Tsagaita Wuta
  • An Watse A Taron EU Da China Saboda Ricikin Kasuwanci Da Siyasa  Tsakaninsu
  • Iran Ta Jaddada Wajabcin Daukan Matakin Kawo Karshen Dakatar Da Laifukan Kisan Kare Dangi A Gaza
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Jaddada Aniyar Iran Ta Ci Gaba Da Inganta Sinadarin Uranium
  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Kasar Iran Ta Ce: Taro Tsakanin Iran Da Tawagar Kasashen Turai Dama Ce Ta Gyarar Tunanin Tarai
  • Firaministan Sin Ya Jagoranci Taron Tattaunawa Tsakanin Shugabannin Sin Da EU Karo Na 25 Tare Da Shugaban Majalisar EU Da Shugabar Hukumar EU
  • Kwamitin Tsaron Majalisar Dinkin Duniya Ya Fara Tattaunawa kan Masifar Zirin Gaza Na Falasdinu
  • Yan Majalisar Dokokin Kasashen Iran Da Iraki Sun Amince Da Ra’yin Ficewar Sojojin Amurka Daga Iraki