Aminiya:
2025-11-02@19:37:55 GMT

Rikici ya barke a taron Atiku da kungiyoyin Arewa

Published: 26th, May 2025 GMT

Daliget sun tayar da jijiyoyin a wurin taron haɗakar siyasar tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar da tsohon dan takarar shugaban kasa na Jam’iyyar LP a zaben 2023, Peter Obi domin fafatawa da shuagaban kasa Bola Tinubu na Jam’iyyar APC a zaɓen 2027.

Ana tsaka da taron Kungiyar Tuntubar Siyasa ta Kasa Reshen Arewa a Abuja ne hayaniya ta kaure bayan tsohon sakataren gwamnatin Tarayya, Babachir David Lawal ya sanar da wanda suna daliget da zai wakilci Jihar Jigawa.

Rashin gamsuwar sauran daliget din jihar dadi ba suka tayar da jijiyoyin wuya, inda suka hau kan mumbari suka dauke wanada aka ayyanan suka hana shi magana da yawunsu.

Daba bisani an yi nasarar shawo kan rikicin, inda aka zabi dan tsohon gwamnan jihar, Sule Lamido, Mustapha Lamido, da wani daliget kuma suka gabatar da jawabi a madadin wakilan jihar.

Ana zargin wani mutum da kashe ɗan maƙwabtansa a Sakkwato Ko gwamnoni duka za su koma APC ba zai hana mu kayar da Tinubu a 2027 ba — Babachir An kashe matashi yayin rikici a ƙauyukan Kano

Atiku wanda ya dade yana neman takarar shugaban kasa a Najeriya yana kokarin jagorantar jam’iyyun adawa domin kayar da Tinubu a zaben na 2027, yana daga cikin fitattun ‘yan siyasar da suka shiga hadakar APC a gabanin zaben 2015.

Hadakar tasu ta kai ga dan takarar APC Muhammadu Buhari, ya yi nasarar kayar da shugaban kasa Goodluck Jonathan a lokacin. Daga bisani ya fice daga APC zuwa tsohuwar jam’iyyarsa ta PDP, inda yake hankoron cika burinsa na zama shugaban kasa.

Daga cikin wadanda ke cikin hadakar tasu Atiku har da tsohon Ministan Sufuri, Rotimi Amaechi da tsohon Sakataren Gwamnatin Tarayya a zamanin Buhari,, Babachir David Lawal.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Xi Jinping Ya Halarci Kwarya-Kwaryan Taron Shugabannin APEC Na 32 Tare Da Gabatar Da Jawabi

 

Shugaba Xi ya kuma bayyana cewa, cikakken zama na 4 na kwamiti na 20 na JKS ya amince da shirin raya kasa na shekaru biyar-biyar karo na 15. Sin za ta yi amfani da wannan damar don ci gaba da gyare-gyaren tattalin arzikinta, da kuma fadada bude kasuwancinta mai zurfi ga ketare, ta haka za ta ci gaba da ba da sabbin damammaki ga yankin Asiya da Pasifik da sauran kasashen duniya ta hanyar zamanantar da al’ummarta. (Amina Xu)

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Daga Birnin Sin An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Tattaunawa Kan Kirkire-kirkire Da Bude Kofa Da Raba Damar Samun Ci Gaba A Colombo October 30, 2025 Daga Birnin Sin Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma  October 30, 2025 Daga Birnin Sin Babban Daraktan Sakatariyar APEC: Sin Tana Ba Da Gudummawar Ba Da Jagoranci A APEC October 30, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • 2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su
  • Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori
  • Samia Suluhu Hassan ta lashe zaben shugaban kasa a Tanzaniya
  • Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC
  • Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar
  • Ya Kamata Shugaba Tinubu Ya Ƙulla Alaƙa Ta Kut-da-kut Tsakanin Hukumar Shige Da Fice Da Kwastam – Babandede
  • Xi Jinping Ya Halarci Kwarya-Kwaryan Taron Shugabannin APEC Na 32 Tare Da Gabatar Da Jawabi
  • Matsalar Talauci Da Rashin Tsawon Rai Da ‘Yan Nijeriya Ke Fuskanta
  • Matsalar Tsaro: Ko Sabbin Shugabannin Rundunar Soji Za Su Kawo Sauyi?
  • Juventus ta ɗauki tsohon kociyan Italiya, Luciano Spalleti