Rikici ya barke a taron Atiku da kungiyoyin Arewa
Published: 26th, May 2025 GMT
Daliget sun tayar da jijiyoyin a wurin taron haɗakar siyasar tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar da tsohon dan takarar shugaban kasa na Jam’iyyar LP a zaben 2023, Peter Obi domin fafatawa da shuagaban kasa Bola Tinubu na Jam’iyyar APC a zaɓen 2027.
Ana tsaka da taron Kungiyar Tuntubar Siyasa ta Kasa Reshen Arewa a Abuja ne hayaniya ta kaure bayan tsohon sakataren gwamnatin Tarayya, Babachir David Lawal ya sanar da wanda suna daliget da zai wakilci Jihar Jigawa.
Rashin gamsuwar sauran daliget din jihar dadi ba suka tayar da jijiyoyin wuya, inda suka hau kan mumbari suka dauke wanada aka ayyanan suka hana shi magana da yawunsu.
Daba bisani an yi nasarar shawo kan rikicin, inda aka zabi dan tsohon gwamnan jihar, Sule Lamido, Mustapha Lamido, da wani daliget kuma suka gabatar da jawabi a madadin wakilan jihar.
Ana zargin wani mutum da kashe ɗan maƙwabtansa a Sakkwato Ko gwamnoni duka za su koma APC ba zai hana mu kayar da Tinubu a 2027 ba — Babachir An kashe matashi yayin rikici a ƙauyukan KanoAtiku wanda ya dade yana neman takarar shugaban kasa a Najeriya yana kokarin jagorantar jam’iyyun adawa domin kayar da Tinubu a zaben na 2027, yana daga cikin fitattun ‘yan siyasar da suka shiga hadakar APC a gabanin zaben 2015.
Hadakar tasu ta kai ga dan takarar APC Muhammadu Buhari, ya yi nasarar kayar da shugaban kasa Goodluck Jonathan a lokacin. Daga bisani ya fice daga APC zuwa tsohuwar jam’iyyarsa ta PDP, inda yake hankoron cika burinsa na zama shugaban kasa.
Daga cikin wadanda ke cikin hadakar tasu Atiku har da tsohon Ministan Sufuri, Rotimi Amaechi da tsohon Sakataren Gwamnatin Tarayya a zamanin Buhari,, Babachir David Lawal.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Xi Jinping Ya Halarci Kwarya-Kwaryan Taron Shugabannin APEC Na 32 Tare Da Gabatar Da Jawabi
Shugaba Xi ya kuma bayyana cewa, cikakken zama na 4 na kwamiti na 20 na JKS ya amince da shirin raya kasa na shekaru biyar-biyar karo na 15. Sin za ta yi amfani da wannan damar don ci gaba da gyare-gyaren tattalin arzikinta, da kuma fadada bude kasuwancinta mai zurfi ga ketare, ta haka za ta ci gaba da ba da sabbin damammaki ga yankin Asiya da Pasifik da sauran kasashen duniya ta hanyar zamanantar da al’ummarta. (Amina Xu)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA