Sojojin Yemen sun kai hari kan filin jirgin saman Ben Gurion da makami mai linzami lamarin da ya tarwatsa cinkoson jama’a a filin jirgin

Sojojin Yemen sun sanar da kai farmakin soji kan filin tashi da saukan  jiragen saman Ben Gurion tare da yin barazanar ci gaba da toshe hanyoyin zirga-zirgar jiragen sama da na ruwa na haramtacciyar kasar Isra’ila muddin bata kawo karshen killace Zirin Gaza da ta yi ba.

Kakakin rundunar sojin kasar Yemen Birgediya Janar Yahya Sari’e ya tabbatar da cewa: Wannan farmakin ya samu nasarar cimma burin da aka sanya a gaba, wanda ya tilastawa miliyoyin ‘yan sahayoniyya ‘yan mamaya tserewa zuwa maboyar karkashin rami tare da dakatar da zirga-zirgar jiragen sama a filin jirgin.

Sari’e ya kara da cewa: Wannan farmakin yana tabbatar da ci gaba da gudanar da ayyukan sojojin Yemen na wajibin addini, kyakkyawar dabi’a da jin kai da kuma dan Adamtaka ga ‘yan uwansu na Falastinu har sai an daina kai hare-haren wuce gona da iri kan Falasdinawa da killace su.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Kasar Sin Na Fatan EU Za Ta Yi Aiki Da Ita Bisa Alkibla Guda Da Tsara Hadin Gwiwa Na Shekaru 50 Masu Zuwa

Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Guo Jiakun, ya bayyana a yayin gudanar da taron manema labaru na yau da kullum da aka yi yau Litinin cewa, bana shekara ce ta cika shekaru 50 da kulla huldar diflomasiyya tsakanin Sin da Tarayyar Turai EU. Kuma taron kolin kasar Sin da EU karo na 25 na karatowa. Kasar ta Sin tana fatan kungiyar EU za ta yi aiki tare da ita bisa alkibla guda, da cimma matsaya, da kawar da bambance-bambance, da kuma tsara shirin hadin gwiwa tare cikin shekaru 50 masu zuwa.

Bayan cimma yarjejeniya tsakanin Sin da kungiyar EU, shugaban majalisar Tarayyar Turai António Costa da shugabar hukumar Tarayyar Turai Ursula von der Leyen, za su ziyarci kasar Sin a ranar 24 ga watan Yuli. Shugaban kasar Sin Xi Jinping zai gana da shugabannin na EU guda biyu. Kazalika, firaministan kasar Sin Li Qiang, zai jagoranci taron koli na Sin da EU karo na 25 tare da shugabannin kungiyar ta EU guda biyu.

Bugu da kari, wasu jami’an diflomasiyyar Turai sun bayyana cewa, kasar Sin na kokarin yin amfani da damar sake fasalin hukumomi don bikin cika shekaru 80 da kafuwar MDD wajen fadada tasirinta a MDD. A yayin da yake mayar da martani kan wannan batu, Guo Jiakun ya ce, kasar Sin na son yin hadin gwiwa tare da kasashen Turai wajen daukar bikin cika shekaru 80 da kafuwar MDD a matsayin wata dama ta kara karfafa muhimmin matsayin da MDD take da shi, da taka rawar da ta dace a matsayinta na MDD yadda ya kamata, da sanya kwarin gwiwa da karfafa damawa da bangarori daban daban. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran: Sojojin Ruwan Iran Sun Kori Jirigin Yakin Amurka Daga Tekun Oman
  • Aikin Zirga-Zirgar Jiragen Sama Ta Fasinja Ta Sin Ya Bunkasa Zuwa Sabon Matsayi
  • Sojojin Yemen Sun Kai Hari Kan Filin Jirgin Lod Na Isra’ila Da Makami Mai Linzami Nau’in Flasdinu
  • Yahudawan Sahayoniyya Sun Bullo Da Dabarar Kisa Kan Falasdinawa Musamman ‘Yan Gudun Hijira
  • Eritrea ta gargadi Habasha game da yunkurin kafa tashar jiragen ruwa a cikin yankinta
  • Natasha za ta sake komawa kotu kan hana ta shiga harabar majalisa
  • Mutum 16 sun mutu a haɗarin jirgin sama a Bangladesh
  • Kasar Sin Na Fatan EU Za Ta Yi Aiki Da Ita Bisa Alkibla Guda Da Tsara Hadin Gwiwa Na Shekaru 50 Masu Zuwa
  • WHO Ta Buƙaci Isra’ila Ta Saki Ma’aikacinta Da Aka Kama A Gaza
  • Jaridar Washington Post Ta Ce; Yeman Ta Gurguta Ayyukan Tashoshin Jiragen Ruwan Isra’ila