Aminiya:
2025-05-30@06:57:37 GMT

Ɗalibai sun maƙale lokacin da gini ya rufta suna jarrabawa

Published: 29th, May 2025 GMT

Ɗaruruwan ɗalibai ne suka suka tsallake rijiya da baya a lokacin da ajujuwan da suke rubuta jarabawar kammala sakandare (SSCE) a ranar Laraba.

Lamarin ya faru ne a makarantar sakandiren gwamnati da ke Namne a Ƙaramar hukumar Gassol a Jihar Taraba.

Ko kwabo ban ciyo bashi ba tun da na zama Gwamnan Kaduna – Uba Sani Ambaliyar ruwa ta kashe sama da mutum 50 a Neja

Ajujuwan sun rufta musu a lokacin da aka yi ruwan sama kamar da baƙin ƙwarya da iska.

Ɗaliban da masu kula da jarrabawar sun maƙale a cikin ajujuwan da suka rufta na tsawon sa’o’i kafin wasu mazauna garin su kuɓutar da su.

Wani mazaunin garin Alhaji DanAzumi Lauris ya shaida wa Daily Trust cewa, ajujuwan sun ruguje karo na biyu da ɗalibai, lokacin da rukunin farko ya gama jarabawa ya bar harabar makarantar.

Ya ce, lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 6 na yammacin Laraba.

DanAzumi, ya bayyana cewa, an kai ɗalibai da malaman da suka jikkata zuwa cibiyar kiwon lafiya a matakin farko da ke kusa da makarantar inda yanzu haka suke samun kulawa.

Ya ce, baya ga makarantar, guguwar ta lalata gidaje da dama a cikin unguwar .

DanAzumi ya bayyana cewa, an kai ɗaliban da Malamai da kuma masu yi wa ƙasa hidima da suka jikkata zuwa cibiyar kiwon lafiya a matakin farko da ke kusa daga makarantar inda yanzu haka suke samun kulawa.

Ya ce baya ga makarantar da guguwar ta lalata gidaje da dama a garin.

 

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Taraba a makarantar

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Amurka Ya Ce: Kasarsa Da Iran Suna Kyakkyawar Tattaunnawa A Tsakaninsu                                                                                                                       

Shugaban kasar Amurka Donald Trump ya bayyana cewa: Suna gudanar da kyakkyawar tattaunawa da Iran

Shugaban Amurka Donald Trump ya bayyana cewa: Amurka na tattaunawa da Iran sosai kan Shirin makamashin nukiliyarta.

Donald Trump ya fada a ranar Laraba cewa:  “Ya damu da abin da ke faruwa a Ukraine, kuma bai sani ba ko Putin na son kawo karshen yakin,” a cewar gidan talabijin na Al Jazeera.

Dangane da tattaunawar da aka yi da Iran, Trump ya ce: “Suna tattaunawa mai kyau da Iran.”

Trump ya ce: Dole ne bangarorin Gaza su amince da takardar da Steve Witkoff wakilin Amurka na musamman a yankin Gabas ta Tsakiya ya gabatar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Amurka Ya Ce: Kasarsa Da Iran Suna Kyakkyawar Tattaunnawa A Tsakaninsu                                                                                                                       
  • Ko kwabo ban ciyo bashi ba tun da na zama Gwamnan Kaduna – Uba Sani
  • Ɗalibai Sun Rubuta Jarrabawar WAEC Cikin Dare A Duhu
  • Makarantar ‘Ya’yan Sojoji Ta Zaria Ta Yi Bukin Cika Shekaru 70 Da Kafawa
  • Amurka za ta hana ‘’visa’’ ga daliban dake sukanta a shafukan sada zumunta
  • An Kama Sojoji 18 Da ‘Yansanda 15 Da Suke Siyar Da Makamai Ga ‘Yan Ta’adda
  • Ina Fatan Cigaba Da Taka Leda Har Zuwa Lokacin da Zan Cika Shekara 40 A Duniya – Salah
  • Hukumar Kare Hakkin Bil’adam Ta MDD Ta Bukaci A Kawo Karshen Kissan Kiyashi A Gaza
  • NAJERIYA A YAU: Matsalolin Da Suke Tarnaki Ga Kananan Yara A Najeriya Da Hanyoyin Magance Su