Ɗalibai sun maƙale lokacin da gini ya rufta suna jarrabawa
Published: 29th, May 2025 GMT
Ɗaruruwan ɗalibai ne suka suka tsallake rijiya da baya a lokacin da ajujuwan da suke rubuta jarabawar kammala sakandare (SSCE) a ranar Laraba.
Lamarin ya faru ne a makarantar sakandiren gwamnati da ke Namne a Ƙaramar hukumar Gassol a Jihar Taraba.
Ko kwabo ban ciyo bashi ba tun da na zama Gwamnan Kaduna – Uba Sani Ambaliyar ruwa ta kashe sama da mutum 50 a NejaAjujuwan sun rufta musu a lokacin da aka yi ruwan sama kamar da baƙin ƙwarya da iska.
Ɗaliban da masu kula da jarrabawar sun maƙale a cikin ajujuwan da suka rufta na tsawon sa’o’i kafin wasu mazauna garin su kuɓutar da su.
Wani mazaunin garin Alhaji DanAzumi Lauris ya shaida wa Daily Trust cewa, ajujuwan sun ruguje karo na biyu da ɗalibai, lokacin da rukunin farko ya gama jarabawa ya bar harabar makarantar.
Ya ce, lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 6 na yammacin Laraba.
DanAzumi, ya bayyana cewa, an kai ɗalibai da malaman da suka jikkata zuwa cibiyar kiwon lafiya a matakin farko da ke kusa da makarantar inda yanzu haka suke samun kulawa.
Ya ce, baya ga makarantar, guguwar ta lalata gidaje da dama a cikin unguwar .
DanAzumi ya bayyana cewa, an kai ɗaliban da Malamai da kuma masu yi wa ƙasa hidima da suka jikkata zuwa cibiyar kiwon lafiya a matakin farko da ke kusa daga makarantar inda yanzu haka suke samun kulawa.
Ya ce baya ga makarantar da guguwar ta lalata gidaje da dama a garin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Taraba a makarantar
এছাড়াও পড়ুন:
A Kalla Falasdinawa 10 Yunwa Ta Kashe A Gaza A Cikin Sa’o’i 24
Ma’aikatar kiwon lafiya ta Gaza ta sanar da cewa a cikin sa’o’i 24 da su ka gabata adadin falasdinawan da su ka yi shahada saboda yunwa sun kai 10.
Daga lokacin da HKI ta fara amfani da yunwa a matsayin makamin yaki,adadin falasdinawan da su ka yi shahada sun kai 111.
Wannan adadin yana nuni da yadda rashin abinci ya tsananta a cikin yankin na Gaza saboda yadda Isra’ila ta killace yankin ta hana a shigar da abinci a ciki.
A gefe daya, HKI tana ci gaba da kashe Falasdinawa ta hanyar yi musu kisan kiyashi, da a yau kadai fiye da mutane 80 ne su ka yi shahada. Mafi yawancin wadanda su ka yi shahada a cikin sa’oin nan na baya suna a unguwannin Tallul-Hawa, da Deir-Balah. Haka nan kuma ‘yan sahayoniyar sun kai wasu hare-haren a sansanin ‘yan hijira dake Mukhayyam-Shadhi.
Kungiyoyin kasa da kasa suna ta ci gaba da yin kira da a bude iyakokin Gaza domin a shigar da kayan abinci, sai dai babu faruwar hakan.
A cikin zirin Gaza dai, mutane suna faduwa suna somewa, wani lokaci mutuwa saboda yunwa, ba kuma babba babu yaro.
Mafi yawancin mutanen da suke mutuwa dai kananan yara ne, jarirai da matasa.