Kasar Najeriya ta sanar da Shirin fara aiki a wasu sabbin masana’antu domin sarrafa sanadarin Lithium

Ministan ma’adanai na kasar ta Najeriya Daili Alaki ne ya sanar a ranar Lahadin da ta wuce cewa, a wannan shekarar da ake ciki ta 2025, da hakan zai samar da gagarumin sauyi a fagen kayan da kasar za ta rika fitarwa zuwa kasashen waje.

Kamfanin dillancin “Reuters” ya ambato ministan ma’adanai na kasar yana ci gaba da cewa; ‘yan kasar China ne za su zuba hannun jari mafi grima a cikin wannan Shirin da hakan zai samar da ayyukan yi a cikin kasar da kuma bunkasar harkokin kere-kere.

Haka nan kuma Alaki ya yi ishara da cewa; Msana’antar sarrafa Lithium din da za a kafa akan iyakar jihohin Kaduna da Niger, za ta ci kudin da sun kai dalar Amurka miliyan 600, yayin da za a kafa wata matatar sanadarin na Lithium a  bayan birnin Abuja da kudin da sun kai dala miliyan 200.

Wata masana’antar ta sarrafa sanadarin Lithium da za kafa a tsakiyar wannan shekarar, za ta kasance ne a Jahar Nasarawa wacce ke iyaka da birnin Abuja.

  Majiyar ta kuma ambaci cewa kamfanin kasar China na ” Geoling’ da kuma “Kankakas Tecnalogy” ne su ka samar da kaso 80% na jarin  tafiyar da kamfanonin,yayin da za a samar da sauran kaso 20% daga cikin gida.

Tun a 2022 ne aka gudanar da wani bincike na karkashin kasa wanda ya tabbatar da cewa da akwai sanadarin “Lithium” a jahohi 6 na kasar, kuma yana da kyau sosai da kuma yawa,lamarin da ya ja hankalin kasashen duniya.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sheikh Na’im Kassim: Gwagwarmaya Tana Da Wata Hanyar Ta Korar ‘Yan Mamaya

Babban magatakardar kungiyar Hizbullah ta kasar Lebanon Sheikn Na’im Kassim ya bayyana cewa; Idan har gwamnatin kasar ta gajiya wajen yin abinda ya rataya a wuyanta na aiki da tsagaita wutar yaki, to gwgawarmaya tana da wata hanyar da za ta yi aiki da ita akan ‘yan mamaya.

Sheikh Na’im Kassim wanda ya gabatar da jawabi a jiya danage da zagayowar cikar shekaru 25 daga korar ‘yan sahayoniya daga kasar Lebanon da gwgawarmaya ta yi, ya jaddada cewa; “Gwagwarmaya ba za ta yi shiru ba, ba kuma za ta mika wuya ba, tana yin hakuri ne saboda ta bayar da Karin lokacin,don haka ya zama wajibi a yunkura.”

Sheikh Na’im Kassim ya kuma ce; Gwamnati ce mai hakkin ganin an yi aiki da tsagaita wutar yaki a Lebanon, amma idan gwamnatin ta kasa, to da akwai mafita a hannun gwgawarmaya.”

Babban magatakardar kungiyar ta Hizbullah ya kuma ce; Aikin gwgawarmaya shi ne kare kai, da kuma kin mika kai ga ‘yan mamaya, wani lokaci tana yaki, wani lokacin kuma tana takawa ‘yan mamaya birki, ko ta yi hakuri tana jira amma tana cikin shiri.”

Sheikh Na’im Kassim ya kuma ce, makami ana yin amfani da shi ne bisa dacewar maslaha.”

Wani sashen na jawabin sheikh Na’im Kassim ya kunshi cewa; A wurin gwagwarmaya har yanzu yaki bai kare ba, kuma abinda Isra’ila take yi, yana karawa gwgawarmaya karfi ne da tsayin daka.”

Haka nan kuma ya ce; Kamar yadda babu wanda ya isa ya kawar da Lebanon, babu wanda kuma zai iya kawar da gwagwarmaya daga Lebanon.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kofin Duniya: Kasar Saudiyya Za Ta Sassauta Dokar Hana Shan Giya A Wuraren Yawon Bude Ido 600
  • Shugaban Kasar Kenya: FOCAC Ya Samar Da Damammaki Ga Sin Da Afirka Wajen Inganta Hadin Kansu Da Samun Moriya Tare
  • Shugaban Jam’iyyar Adawa A Burtaniya Ya Ce HKI Tana Yaki A Gaza Ne A Madadin Gwamnatin Kasar
  • Sheikh Na’im Kassim: Gwagwarmaya Tana Da Wata Hanyar Ta Korar ‘Yan Mamaya
  • Ruhin Yuan Longping Ya Ba Da Tabbaci Ga Samar Da Isashen Hatsi a Nahiyar Afirka
  • An Gudanar da Zabukan Larduna A Kudancin Kasar Lebanin A Cikin Barazanar HKI
  • An Gargadi Shugaban Amurka Dangane Da Fadawa Iran Da Yaki
  • Tawagar MDD Da Majalisar Shugabancin Libya Sun Kafa Kwamitin Tsagaita Bude Wuta
  • Firaministan Sin Ya Shugabanci Taro Kan Masana’antu Masu Amfani Da Makamashi Mai Tsafta Da Kare Muhalli