Kasar Najeriya ta sanar da Shirin fara aiki a wasu sabbin masana’antu domin sarrafa sanadarin Lithium

Ministan ma’adanai na kasar ta Najeriya Daili Alaki ne ya sanar a ranar Lahadin da ta wuce cewa, a wannan shekarar da ake ciki ta 2025, da hakan zai samar da gagarumin sauyi a fagen kayan da kasar za ta rika fitarwa zuwa kasashen waje.

Kamfanin dillancin “Reuters” ya ambato ministan ma’adanai na kasar yana ci gaba da cewa; ‘yan kasar China ne za su zuba hannun jari mafi grima a cikin wannan Shirin da hakan zai samar da ayyukan yi a cikin kasar da kuma bunkasar harkokin kere-kere.

Haka nan kuma Alaki ya yi ishara da cewa; Msana’antar sarrafa Lithium din da za a kafa akan iyakar jihohin Kaduna da Niger, za ta ci kudin da sun kai dalar Amurka miliyan 600, yayin da za a kafa wata matatar sanadarin na Lithium a  bayan birnin Abuja da kudin da sun kai dala miliyan 200.

Wata masana’antar ta sarrafa sanadarin Lithium da za kafa a tsakiyar wannan shekarar, za ta kasance ne a Jahar Nasarawa wacce ke iyaka da birnin Abuja.

  Majiyar ta kuma ambaci cewa kamfanin kasar China na ” Geoling’ da kuma “Kankakas Tecnalogy” ne su ka samar da kaso 80% na jarin  tafiyar da kamfanonin,yayin da za a samar da sauran kaso 20% daga cikin gida.

Tun a 2022 ne aka gudanar da wani bincike na karkashin kasa wanda ya tabbatar da cewa da akwai sanadarin “Lithium” a jahohi 6 na kasar, kuma yana da kyau sosai da kuma yawa,lamarin da ya ja hankalin kasashen duniya.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Magance Matsalar Yara Da Ba Sa Zuwa Makaranta: Gwamnan Zamfara Ya Ƙaddamar Da Shirin Ciyarwa A Makarantun Jihar

A nasa jawabin, Gwamna Lawal ya bayyana cewa, ƙaddama da shirin na nuni da ƙwazon gwamnatinsa na yin aiki tare da masu ruwa da tsaki domin aiwatar da dabaru daban-daban na ƙara yawan ɗalibai a makarantun jihar Zamfara.

 

Ya ci gaba da cewa, “Alƙawarinmu na yin garambawul ya haɗa da tsare-tsare na yaƙi da rugujewar sassan ilimi da samar da haɗin gwiwa, kamar Bankin Duniya ta hanyar shirin AGILE da kuma UNICEF. A kwanakin baya Ma’aikatar Ilimi, Kimiya da Fasaha tare da haɗin gwiwar UNICEF, sun kafa wani kwamitin fasaha na shugabannin hukumomin da masu ruwa da tsaki domin ziyartar mananan hukumomi 14, da tantance yaran da ba su zuwa makaranta, da kuma tabbatar da shigar su makarantu.

 

“Shirin ciyar da ɗalibai a makarantu da muke ƙaddamarwa a yau, wani bangare ne na shirye-shiryen bayar da agajin gaggawa na inganta rajista da kuma riƙe ɗalibai a makarantu tare da yaƙi da yunwa da rashin abinci mai gina jiki. Wannan baya ga ƙoƙarin mu da wasu ƙungiyoyi masu zaman kansu guda biyu, Cibiyar Ci Gaban Tattalin Arziki ta Ƙasa da Ƙasa da Gidauniyar FINPACT, waɗanda suka amince da tallafa wa gwamnati wajen aiwatar da shirin domin yin aiki a matsayin tushen ilimi.

 

“A cikin sharuɗɗan, gidauniyar FINPACT za ta ɗauki nauyin ciyar da ɗalibai 1000 a Gusau, Maru, Anka, da Talatar Mafara, yayin da Cibiyar Raya Tattalin Arziki ta Duniya ke ɗaukar nauyin ciyar da ɗalibai 3300 a faɗin Gusau, Talatar Mafara, da Shinkafi.

 

“Ina kira ga duk masu ruwa da tsaki da sauran hukumomin bayar da agaji da su ƙara binciko hanyoyin samar da ƙarin ayyuka da shirye-shirye, wanda ba wai kawai hakan zai ƙara ƙaimi wajen samar da ilimi mai inganci ba ne, amma zai rage adadin yaran da ba su zuwa makaranta, ta yadda tare za mu mai da jiharmu ta zama abin koyi.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jamhuriyar Nijar Da China Sun Kusa Warware Sabanin Dake Tsakaninsu Akan Batun Man Fetur
  • FRCN Ya Kaddamar Da Shirin Koyar Da Sinanci Mai Taken “Hello China”
  • Magance Matsalar Yara Da Ba Sa Zuwa Makaranta: Gwamnan Zamfara Ya Ƙaddamar Da Shirin Ciyarwa A Makarantun Jihar
  • Aragchi: Kofar Iran Ta Tattaunawa A Bude Take, Amma Amurka Sai Ta Biya Kudade Kan Kura-Kuranta
  • Shugaban Kasar Iran Yace Huldar kasar Iran Da IAEA Zai Ci Gaba Ne Idan Ta Daina Fuska Biyu
  • Muna so a kafa doka ta bincikar yadda ’yan Nijeriya ke tara dukiya — EFCC
  • An kashe mutum ɗaya da ƙona gidaje sama da 100 a Taraba
  • Manazaecin Kasar Amurka Ya Ce; Isra’ila Ta Sha Kashi A  Yakinta Da Jamhuriyar Musulunci Ta Iran
  • Zagaye na 5 A Tattaunawar Gaza da HKI  Ya tashi ba tare da Sun Dai-daita ba A Doha
  • Za A Horas Da Jami’an Tsaron Sakkwato, Kaduna Da Benue Sabbin Dabarun Aiki