Shugaba Tinubu Ya Aika Tawaga Zuwa Jihar Neja Kan Ambaliya Ruwa
Published: 31st, May 2025 GMT
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp.কীওয়ার্ড: Ambaliya
এছাড়াও পড়ুন:
Makami Mai Linzami Daga Yemen Ya Tashi Jiniyar Gargadi A Garuruwa 300 Na HKI
Sa’oi kadai da su ka gabata jiniyar gargadi ta kada a cikin garuruwa da sansanonin ‘yan share wuri zauna 300 a HKI saboda makami mai linzami da mutane Yemen su ka harba.
Kafafen watsa labarun ‘yan sahayoniya sun ambaci cewa; an rufe filin saukar jiragen saman a “Ben Gorion” da kuma dakatar da kai da komowar jiragen sama.
Kafafen watsa labarun na HKI sun ambaci cewa; Miliyoyin mutane ne su ka gudu zuwa Mabuya.
Wannan sabon harin dai na sojojin Yemen yana zuwa ne a karkashin abinda sojojin na Yemen su ka kira, kakaba takunkumi na sama da ruwa akan HKI, tare da yin kira ga kamfanonin jiragen sama da na ruwa da su kauracewa zuwa wannan haramtacciyar kasa.
Filin saukar jiragen sama na Ben Gorion’ da tashoshin jiragen ruwa ta Haifa da Eiliat su ne wadanda takunkumin na sojojin Yamen ya fi shafa.
Kwanaki kadan da su ka gabata jagoran kungiyar Ansarullah ta kasar Yemen, Sayyid Abdulmalik al-Husi ya sanar da cewa, ba za su daina kai wa HKI hare-hare, har sai idan sun kawo karshen yakin Gaza da kuma killace yankin da aka yi.