Ina Fatan Cigaba Da Taka Leda Har Zuwa Lokacin da Zan Cika Shekara 40 A Duniya – Salah
Published: 28th, May 2025 GMT
Da yake magana da tashar talabijin ta ON Sports, Salah ya ce “Zan daina wasa ne kawai idan na fara jin gajiya a jikina”, “Idan ka tambaye ni ra’ayi na, ina tsammanin zan iya taka leda har zuwa shekaru 39 zuwa 40 amma idan na ji ina so in daina, zan daina, na samu abubuwa da yawa a harkar kwallon kafa”, inji Salah wanda ya lashe kyautar gwarzon dan wasan Firimiya Lig ta bana.
Salah ya ci wa Liverpool da Chelsea kwallaye 186 a gasar firimiya kuma ya na matsayi na biyar a jerin wadanda suka fi kowa zura kwallo a raga inda kwallo daya kacal ta rage ya cimma tsohon dan wasan Newcastle da Manchester United Andrew Cole, dan wasan na Masar ya nuna cewa zai iya taka leda a Gabas ta Tsakiya bayan kwantiraginsa a Anfield ya kare a shekara ta 2027.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Makarantar ‘Ya’yan Sojoji Ta Zaria Ta Yi Bukin Cika Shekaru 70 Da Kafawa
Shugaban rundunar mayakan sama ta kasa,Air Marshal, Hassan Abubakar, ya bukaci tsoffin daliban makarantar ‘ya’yan sojoji dake Zaria watau NMS da su kasance masu kwazo da da’a a duk inda suke kamar yadda suka koya a makarantar.
Ya bayyana haka ne lokacin da ya ke jawabi a matsayin Babban bako na musamman a wurin bukin cika shekara 71 da aka gudanar a filin faretin RSM Zakari Kumasi dake harabar makarantar a zaria.
Shugaban rundunar mayakan saman ya bayyana cewa makarantar ta NMS ta yi fice wajen baiwa yara horo a fannonin karatu da kuma ilimin aikin soja wanda hakan ya sa ta samar da manyan sojoji da dama har ma da shi a ciki.
Air Marshal Abubakar ya ce bukin na da matukar muhimmanci gare shi,kasancewar sa tsohon dalibin makarantar.
A don haka sai ya yaba wa makarantar ta NMS bisa kasancewar ta akan turbar da aka santa da shi na samar da jajirtattun sojoji ga rundunar mayakan sama ta kasa tsawon shekaru 71 da kafa ta.
Shi ma a nashi jawabin, shugaban kungiyar tsoffin daliban makarantar, Laftana Kwamanda Sunday Ngegu mai ritaya, ya ce kasancewar shugaban rundunar mayakan sama tsohon dalibi a makarantar ya rinka taimaka wa kungiyar, inda ya bukaci sauran tsoffin daliban da suyi koyi da hakan.
Sunday Ngegu ya kuma yaba wa shugaban rundunar mayakan saman bisa gudunmuwar da ya baiwa kungiyar har ta samu nasarorin da ta samu.
Daliban makarantar sun gudanar da faretin ban girma ga manyan baki,yayin da kuma shugaban rundunar mayakan saman ya kaddamar da dakin shan magani na dalibin da babban dakin cin abinci tare da Kwamandan rundunar soji ta daya da sauran Kwamandodin rundunonin soja gami da mai masaukin baki na NMS.