Gwamnatin Jihar Kano ta cika alƙawarin da ta ɗauka ga al’ummar ƙauyen Gadan, ƙaramar hukumar Gezawa, inda aka kona masallata a lokacin Sallar Asuba.

Kwamishinan yaɗa labarai da harkokin cikin gida, Kwamared Ibrahim Abdullahi Waiya, ya bayyana hakan cikin wata sanarwa a daren Litinin, yana mai cewa gwamnati ta amince da kashe Naira miliyan 151,863,895.

97 domin gudanar da muhimman ayyukan ci gaba a garin.

Kotu Ta Yanke Hukuncin Kisa Ga Wanda Ya Kona Masallata A Kano Yadda Rikici Ya Yi Sanadin Kashe DPO A Kano

Ayyukan sun haɗa da gyara da faɗaɗan masallacin da aka ƙona masallatan a ciki, da ginin sabuwar makarantar Islamiyya da ofishin malamai, da gyaran banɗakuna guda shida, da kuma aikin famfon tuka-tuka mai amfani da hasken rana tare da ƙarin tanki a sama.

Al’ummar ƙauyen Gadan sun bayyana matuƙar farin cikinsu da wannan ci gaba, inda suka bayyana cewa irin wannan cika alƙawarin na nuna shugabanci nagari da kishin jama’a.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Sharrin son auren Mai Wushirya aka yi min — Mansura Isa

Tsohuwar jarumar Kannywood, Mansurah Isa, ta ƙaryata labarin da wata jaridar intanet ta yaɗa cewa wai tana son ta auri shahararren dan TikTok, Ashiru Mai Wushirya, wanda ya yi tashe a kafafen sada zumunta a ’yan kwanakin nan.

A wani saƙo da ta wallafa, Mansurah ta ce labarin ƙarya ne kuma ya jefa ta da iyalinta cikin ruɗani da damuwa.

Ta ce, “Na shiga firgici bayan na ga wannan labarin. Ba ni da wata alaka da Mai Wushirya. Wannan sharri ne tsagwaron karya.”

Rahoton da aka yada a jaridar AMC Hausa ya yi iƙirarin cewa wai Mansurah ta ce ta shirya auren Mai Wushirya idan har yana son ta da gaske.

Kofin kofi mafi tsada a duniya ya shiga kasuwa a kan Naira miliyan 1.5m An yi garkuwa da Mataimakin Shugaban Majalisar Dokokin Kebbi

Amma jarumar ta yi watsi da wannan iƙirarin, tana mai cewa jaridar ta ɓata mata suna kuma ta karya ƙa’idojin aikin jarida.

Ta ce, “Na kira su, na ba su awa 24 su sauke labarin, amma har yanzu ba su yi hakan ba. Sun kira ni sun ba ni hakuri a waya, amma labarin har yanzu yana nan. Wannan abu ya zubar min da mutunci kuma ya saka iyalina cikin tashin hankali,” ina ji ta.

Mansurah ta bayyana cewa yanzu tana cikin shirin ‘WalkAwayCancer’, wani gagarumin shiri na wayar da kan jama’a kan mcutar daji, amma wannan labarin karya ya yi ƙoƙarin karkatar da hankalin mutane daga ainihin aikinta.

“Kun hana ni barci da kwanciyar hankali saboda labarin da babu gaskiya a cikinsa. Amma in sha Allahu, za ku ji daga gare mu,” in ji ta cikin fushi.

Har zuwa lokacin da muka kammala wannan labarin dai, kamfanin AMC Hausa bai fitar da wata sanarwa ba dangane da ƙarar da Mansurah ke shirin kai musu bisa zargin yaɗa labarin ƙarya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Taron APEC Na 2026 Da Za A Shirya A Kasar Sin Zai Bude Sabon Babin Na Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik
  • Gwamnatin Isra’ila Tana Ci Gaba Da Hana Masu Jinya Zuwa Kasashen Waje Neman Magani Daga Gaza
  • Muna shirin kai farmaki a Nijeriya — Ma’aikatar Yaƙin Amurka
  • Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik
  • Iran ta damu da halin da ake ciki a yankin El Fasher na Sudan
  • Sharrin son auren Mai Wushirya aka yi min — Mansura Isa
  • Kofin kofi mafi tsada a duniya ya shiga kasuwa a kan Naira miliyan 1.5m
  • Barcelona ta shiga zarwacin Victor Osimhen
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • Real Madrid zata nemi diyyar Dala bilyan 4 daga UEFA