Aminiya:
2025-07-12@02:42:32 GMT

Kwastam ta kama Tiramol ta N150m, ta miƙa wa NAFDAC a Kano

Published: 26th, May 2025 GMT

Hukumar Kwastam reshen Kano da Jigawa, ta kama nau’in ƙwayar Tiramol katan 491,000, tare da miƙa su ga Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC).

An ƙiyasta kuɗin magungunan da aka kama sama da Naira miliyan 150, kuma an gano su a cikin wata mota ƙirar Lexus SUV, a hanyar Gumel zuwa Maigatari da ke Jihar Jigawa.

FCTA ta rufe hedikwatar PDP saboda rashin biyan haraji Ana zargin wani mutum da kashe ɗan maƙwabtansa a Sakkwato

Kwanturolan hukumar a yankin, Dalhatu Abubakar, ya ce an yi wannan nasara ne bisa sahihan bayanan sirri, kuma yana daga cikin ƙoƙarin da suke yi tun bayan shigarsa ofis a watan Fabrairun 2025.

Abubakar, ya ce an shigo da ƙwayoyin ne cikin dare, kuma sun saɓa da dokokin da aka sarrafa su.

“Wannan ƙwaya tana lalata rayuka. Ka tambayi kanka shin wata ’yar uwarka, ɗanka, ko maƙwabcinka ba sa amfani da ita?” in ji shi.

Ya ƙara da cewa amfani da Tiramol yana haifar da ƙaruwar laifuka, taɓin hankali, da rashin tsaro, musamman a Arewacin Najeriya.

Bisa ƙididdigar da Majalisar Ɗinkin Duniya da Hukumar Ƙididdiga ta Ƙasa (NBS) suka fitar, ana ƙiyasta cewa kimanin mutane miliyan uku ke amfani da miyagun ƙwayoyi a yankin Arewa maso Yamma.

A Jihar Kano kuwa, sama da mutum 670,000 ke amfani da ƙwayar Tiramol ba tare da izinin likita ba.

Ya kuma ce daga cikin masu amfani da ƙwayoyi a Najeriya huɗu mata ne, wanda hakan abin damuwa ne ganin rawar da mata ke takawa a cikin gida da al’umma.

Abubakar, ya buƙaci haɗin gwiwa daga wajen malamai, sarakunan gargajiya, ƙungiyoyin fararen hula, da hukumomin gwamnati don yaƙi da matsalar amfani da miyagun ƙwayoyi.

Taron ya ƙare ne da miƙa ƙwayoyin da aka kama zuwa hannun Hukumar NAFDAC domin ɗaukar matakin doka.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Kwastam Tiramol

এছাড়াও পড়ুন:

HKI: Sojoji 62 Ne Su Ka Halaka A Gaza A Cikin Wannan Shekara Ta 2025

 Jaridar HKI ta “Haaretz'” ta buga labarin da yake cewa: A cikin wannan shekarar ta 2025, sojojinsu da su ka halaka sun kai 62.

A cikin watannin bayan nan an sami karuwar sojojin mamayar da ‘yan gwgawarmaya suke kashewa a Gaza.

Yankin Khan Yunus dake Arewacin Gaza da HKI take riya cewa ta nike shi, sannan kuma ta kori Falasdinawa daga cikinsa, yana daga cikin wuraren da aka yi wa sojojin mamayar kwanton bauna.

Bugu da kari, har yanzu ‘yan gwgawarmayar suna ci gaba da harba makamai masu linzami daga Gaza zuwa matsugunan ‘yan share wuri zauna da suke kusa da Gaza.

A jiya ma dakarun “Sarayal-Quds” na kungiyar Jihadul-Islami ta sanar da harba makamai masu linzami zuwa  matsugunan da suke da Gaza.

Jaridar ta “Haaratz’ ta kuma ce, Fira ministan na HKI bai yi wa iyalan ko daya daga cikin iyalan sojojin da aka kashe a Gaza ta’aziyya  ba, balle ya gana da su.

Jaridar ta kuma ce, hotunan da ake nunawa na Netanyahu yana ganawa da iyalan sojoji tsoho ne ba sabo ba ne.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa
  • An Kama Magungunan Jabu Na Fiye Da Naira Biliyan Ɗaya A Kano
  • EFCC Ta Yi Gargadi Kan Damfara Ta Hanyar Kuɗaɗen Intanet da Zuba Jari
  • Kwastam ta kama mazaƙutar jakai da aka yi yunƙurin safararsu
  • ’Yan sanda sun ƙaddamar da sabon samame, sun kama mutum 98 a Kano
  • ’Yan sanda sun ƙaddamar da samamen “Operation Kukan Kura”, sun kama mutum 98 a Kano
  • Gwamna Namadi Ya Bukaci Hadin Gwiwar Hukumar Kwastam Don Farfado Da Yankin Kasuwanci Na Maigatari
  • ‘Yansanda Sun Kama Mutum 22 Kan Zargin Kisan ‘Yan Ɗaurin Aure A Filato
  • HKI: Sojoji 62 Ne Su Ka Halaka A Gaza A Cikin Wannan Shekara Ta 2025
  • Hukumar Kiyaye Hadura Ta Kasa Za Ta Aiki Da ‘Yan Jarida A Kano