Aminiya:
2025-05-27@19:26:17 GMT

Kwastam ta kama Tiramol ta N150m, ta miƙa wa NAFDAC a Kano

Published: 26th, May 2025 GMT

Hukumar Kwastam reshen Kano da Jigawa, ta kama nau’in ƙwayar Tiramol katan 491,000, tare da miƙa su ga Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC).

An ƙiyasta kuɗin magungunan da aka kama sama da Naira miliyan 150, kuma an gano su a cikin wata mota ƙirar Lexus SUV, a hanyar Gumel zuwa Maigatari da ke Jihar Jigawa.

FCTA ta rufe hedikwatar PDP saboda rashin biyan haraji Ana zargin wani mutum da kashe ɗan maƙwabtansa a Sakkwato

Kwanturolan hukumar a yankin, Dalhatu Abubakar, ya ce an yi wannan nasara ne bisa sahihan bayanan sirri, kuma yana daga cikin ƙoƙarin da suke yi tun bayan shigarsa ofis a watan Fabrairun 2025.

Abubakar, ya ce an shigo da ƙwayoyin ne cikin dare, kuma sun saɓa da dokokin da aka sarrafa su.

“Wannan ƙwaya tana lalata rayuka. Ka tambayi kanka shin wata ’yar uwarka, ɗanka, ko maƙwabcinka ba sa amfani da ita?” in ji shi.

Ya ƙara da cewa amfani da Tiramol yana haifar da ƙaruwar laifuka, taɓin hankali, da rashin tsaro, musamman a Arewacin Najeriya.

Bisa ƙididdigar da Majalisar Ɗinkin Duniya da Hukumar Ƙididdiga ta Ƙasa (NBS) suka fitar, ana ƙiyasta cewa kimanin mutane miliyan uku ke amfani da miyagun ƙwayoyi a yankin Arewa maso Yamma.

A Jihar Kano kuwa, sama da mutum 670,000 ke amfani da ƙwayar Tiramol ba tare da izinin likita ba.

Ya kuma ce daga cikin masu amfani da ƙwayoyi a Najeriya huɗu mata ne, wanda hakan abin damuwa ne ganin rawar da mata ke takawa a cikin gida da al’umma.

Abubakar, ya buƙaci haɗin gwiwa daga wajen malamai, sarakunan gargajiya, ƙungiyoyin fararen hula, da hukumomin gwamnati don yaƙi da matsalar amfani da miyagun ƙwayoyi.

Taron ya ƙare ne da miƙa ƙwayoyin da aka kama zuwa hannun Hukumar NAFDAC domin ɗaukar matakin doka.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Kwastam Tiramol

এছাড়াও পড়ুন:

Yadda kotu ta yanke wa wanda ya kona mutane a cikin masallaci hukuncin rataya a Kano

Babbar Kotun Musulunci a Jihar Kano ta yanke wa Shafiu Abubakar hukuncin kisa ta hanyar rataya saboda cinna wuta a wani masallaci a kauyen Gadan, Karamar Hukumar Gezawa, yayin da jama’a ke tsaka da jam’in sallar asuba a ranar 15 ga Mayu, 2024. Harin ya yi sanadiyar mutuwar mutane 23 tare da raunana wasu.

An samu Shafi’u da laifuka hudu, ciki har da kisan kai da kuma barna ta hanyar gobara. Baya ga hukuncin kisa, alkali ya ba da umarnin a yi masa bulala 150, tare da biya tarar N1,500, sannan kuma a kwace babur dinsa mai kafa uku, inda za a sayar, a yi amfani da kudin da aka samu wajen gyaran masallacin da ya lalace.

Yayin shari’ar, masu gabatar da kara sun gabatar da shaidu bakwai, ciki har da hakimin kauye da kuma wani jami’in ’yan sanda.

Daya daga cikin shaidun, wanda dan uwan Shafi’u ne, ya bayyana cewa wanda ake tuhumar yana da tarihin kokarin cutar da ’yan uwa, kuma an bayyana shi a matsayin mai cikakken hankali bayan binciken tabin hankali.

An yanke wa wanda ya yi wa agolarsa fyaɗe ɗaurin rai-da-rai  Jama’ar gari sun kashe DPO, sun ƙona ofishin ’yan sanda a Kano 

Wani shaida kuma ya bayyana yadda ya tsira a lokacin da masallacin da ke ci da wuta tare da munanan raunuka kuma ya ga Shafi’u yana gudu.

Shafiu ya shaida wa kotun cewa ya sayi man fetur a ranar 14 ga Mayu, 2024, don yayyafa wa masallacin sannan ya cinna masa wuta, ya rufe kofofinsa kuma ya samu konewa a lokacin da yake aikata laifin. Furucinsa, tare da konewar da ke bayyane a hannayensa yayin bayyanarsa a kotu, sun tabbatar da shari’ar masu gabatar da kara.

Daraktan gabatar da kara na Jihar Kano ya bayyana gamsuwarsa da hukuncin, inda ya bayyana cewa ya nuna girman laifin.

Sai dai lauyan Shafi’u ya nuna yiwuwar daukaka kara tare da nuna damuwa game da yanayin da yake tsare.

An ruwaito cewa lamarin ya samo asali ne daga rikicin gado, inda Shafi’u ya yi niyyar kai hari ga ’yan uwansa da ya yi imanin sun zalunce shi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yansanda Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Kisan Wata Matar Aure, ‘Yar shekara 22 A Kano
  • Sojojin Sudan Sun Fatattaki Dakarun Kai Daukin Gaggawa Daga Sansaninsu Da Ke Birnin Omdurman
  • ’Yan sanda sun kama wanda ake zargi da kisan matar aure a Kano
  • Gwamnatin Kano za ta sabunta masallacin da aka kona masallata 23 a kan N150m
  • Yadda kotu ta yanke wa wanda ya kona mutane a cikin masallaci hukuncin rataya a Kano
  • Hukumar Kare Hakkin Bil’adam Ta MDD Ta Bukaci A Kawo Karshen Kissan Kiyashi A Gaza
  • Wike ya rufe ofishin FIRS da Bankin Access kan rashin biyan haraji
  • An kama Hakimi kan zargin taimaka wa ’yan bindiga a Neja
  • Firaministan Sin Ya Shugabanci Taro Kan Masana’antu Masu Amfani Da Makamashi Mai Tsafta Da Kare Muhalli