Aminiya:
2025-09-17@23:13:19 GMT

Kwastam ta kama Tiramol ta N150m, ta miƙa wa NAFDAC a Kano

Published: 26th, May 2025 GMT

Hukumar Kwastam reshen Kano da Jigawa, ta kama nau’in ƙwayar Tiramol katan 491,000, tare da miƙa su ga Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC).

An ƙiyasta kuɗin magungunan da aka kama sama da Naira miliyan 150, kuma an gano su a cikin wata mota ƙirar Lexus SUV, a hanyar Gumel zuwa Maigatari da ke Jihar Jigawa.

FCTA ta rufe hedikwatar PDP saboda rashin biyan haraji Ana zargin wani mutum da kashe ɗan maƙwabtansa a Sakkwato

Kwanturolan hukumar a yankin, Dalhatu Abubakar, ya ce an yi wannan nasara ne bisa sahihan bayanan sirri, kuma yana daga cikin ƙoƙarin da suke yi tun bayan shigarsa ofis a watan Fabrairun 2025.

Abubakar, ya ce an shigo da ƙwayoyin ne cikin dare, kuma sun saɓa da dokokin da aka sarrafa su.

“Wannan ƙwaya tana lalata rayuka. Ka tambayi kanka shin wata ’yar uwarka, ɗanka, ko maƙwabcinka ba sa amfani da ita?” in ji shi.

Ya ƙara da cewa amfani da Tiramol yana haifar da ƙaruwar laifuka, taɓin hankali, da rashin tsaro, musamman a Arewacin Najeriya.

Bisa ƙididdigar da Majalisar Ɗinkin Duniya da Hukumar Ƙididdiga ta Ƙasa (NBS) suka fitar, ana ƙiyasta cewa kimanin mutane miliyan uku ke amfani da miyagun ƙwayoyi a yankin Arewa maso Yamma.

A Jihar Kano kuwa, sama da mutum 670,000 ke amfani da ƙwayar Tiramol ba tare da izinin likita ba.

Ya kuma ce daga cikin masu amfani da ƙwayoyi a Najeriya huɗu mata ne, wanda hakan abin damuwa ne ganin rawar da mata ke takawa a cikin gida da al’umma.

Abubakar, ya buƙaci haɗin gwiwa daga wajen malamai, sarakunan gargajiya, ƙungiyoyin fararen hula, da hukumomin gwamnati don yaƙi da matsalar amfani da miyagun ƙwayoyi.

Taron ya ƙare ne da miƙa ƙwayoyin da aka kama zuwa hannun Hukumar NAFDAC domin ɗaukar matakin doka.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Kwastam Tiramol

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan sanda sun kama mutum 6 kan satar zinarin N109m a Kebbi

Wasu mutum shida sun shiga hannun ’yan sanda kan zargin satar zinari da kuɗinta ya haura Naira miliyan 109.5 a Jihar Kebbi.

Sashen binciken manyan laifuka na rundunar ’yan sanda a jihar Kebbi na tuhumar su da sace sarkoƙin zinare guda biyar sauran kayan zinare daga wani gida a garin Ka’oje, Ƙaramar Hukumar Bagudo.

Sauran sun haɗa da zobba huɗu da munduwar hannu tara, da nauyinsu ya kai gram 782.7 — dukkansu mallakar ’ya’ya da ’yan uwar mai gidan.

Wanda ake tuhuma ya amsa laifi

Bayan samun koken, jami’an suka kama Ibrahim Abubakar Ka’oje, jami’i a Hukumar Gyaran Hali ta Kasa, wanda a yayin bincike, ya amsa laifin.

’Yan ‘Mafiya’ na ƙoƙarin kashe matatar man fetur da na gina —Ɗangote ’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu

Ya bayyana cewa ya sayar da kayan ga wasu mutane biyu, dukkansu daga Sakkwato, tare da wasu mutum biyu a Jihar Kebbi.

An kuma gano wanda  ya taimaka masa wajen sayar da wasu daga cikin kayan, inda ya karɓi naira miliyan 2.5 a matsayin lada.

Rundunar ’yan sanda ta bayyana cewa har yanzu tana neman sauran da suka gudu, bisa zargin taimakawa wajen sayar da kayan sata.

Ana zargin an sayi filaye biyu a Birnin Kebbi da kuɗin da aka samu daga sayar da kayan.

Abubuwan da aka ƙwato

Kayan da aka ƙwato sun haɗa da munduwar hannu biyu, babur ɗin Haouje, da kuma wayoyin iPhone 16, Samsung Galaxy Ultra da Samsung Flip.

Kwamishinan ’yan sanda na Jihar Kebbi, Bello M. Sani, ya jinjina wa jajircewar jami’ansa bisa wannan nasara.

Ya kuma yi kira gare su da su ci gaba da aiki tukuru domin cafke sauran da ake nema da kuma ƙwato dukkan kayan da suka rage.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB
  • Karamar Hukumar Birnin Kano Ta Kaddamar Da Kula Da Lafiyar Ido Kyauta
  • Saudiyya ta saki ’yan Najeriya 3 da ta kama kan zargin safarar miyagun ƙwayoyi
  • Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Ta Kama Bisa Kuskuren Safarar Ƙwayoyi
  • Gwamnatin Kano ta gayyaci Mai Dubun Isa da Shehi Tajul-Izzi kan shirya muƙabala
  • NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
  • ’Yan sanda sun kama mutum 6 kan satar zinarin N109m a Kebbi
  • An kama mabaraci da kuɗaɗen ƙasar waje a Ilorin