Aminiya:
2025-05-30@15:15:28 GMT

NAHCON ta kammala jigilar maniyyata aikin hajjin 2025

Published: 29th, May 2025 GMT

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta kammala jigilar maniyyatan Najeriya zuwa ƙasar Saudiyya domin gudanar da aikin hajjin shekarar 2025.

Da yake jawabi ga manema labarai a filin jirgin sama na Nnamdi Azikiwe da ke Abuja kafin jirgin maniyyatan ya tashi zuwa Saudiyya, Shugaban Hukumar NAHCON, Farfesa Abdullahi Saleh Usman, ya ce aikin Hajjin bana ya samu nasarori da dama da suka nuna ci gaba da inganta aikin hajjin Nijeriya.

NDLEA ta kama maniyyata aikin hajji ɗauke da hodar iblis ’Yan bindiga sun kashe makiyaya 2, sun sace shanu 320 a Kaduna

Ya ce, an yi jigilar maniyyata 41,568 ta jiragen sama 105.

Hakan na zuwa ne a daidai lokacin da ya nuna matuƙar godiya ga shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu da mataimakin shugaban ƙasa, Sanata Kashim Shettima bisa gagarumin goyon bayan da suka bayar wajen ganin an gudanar da aikin Hajjin 2025 cikin nasara.

A cewarsa, duk da cewa aikin jigilar jirage ba abu ne mai sauƙi ba, tare da haɗin gwiwar masu ruwa da tsaki, hukumar ta samu nasarar kammala aikin.

Shugaban Hukumar NAHCON ya bayyana cewa, akwai ƙalubale a yayin aikin jigilar jiragen amma tare da haɗin gwiwar hukumar ta samu nasarar cimma burinta na ganin duk wani mahajjatan Najeriya ya tafi ƙasa mai tsarki tare da kula da su yadda ya kamata.

“Yayin da muke rufe shirin jigilar jirage zuwa aikin Hajjin 2025 na bana daga kason jihar, wannan lokaci ne mai matuƙar muhimmanci a gare mu baki ɗaya domin hakan na nufin mun samu nasarar kwashe dubban maniyyatanmu cikin ‘yan makonni.

“Ba abu ne mai sauƙi ba, amma da kyakkyawan tsari, bayan taimakon Allah Maɗaukakin Sarki da haɗin gwiwar da muka yi, mun kammala aiki cikin nasara, Alhamdulillah.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Nasarawa Ta Bukaci A Cire Malamai 1000 Daga Aikin Tantancewar Da Ake Yiwa Malamai

Majalisar dokokin jihar Nasarawa, ta umurci gwamnatin jihar da ta cire sabbin malamai 1000 wadanda ke karbar albashinsu daga aikin tantance malaman da ake yi a jihar.

 

Mataimakin kakakin majalisar Muhammad Adamu Oyanki, ya yi wannan kiran ne a lokacin da yake karanta kudurin majalisar bayan Daniel Ogazi ya kawo lamarin cikin gaggawa ga al’umma yayin zaman majalisar a lafiya.

 

Mohammed Adamu Oyanki ya ce malamai 1000 da ke karbar albashin na aiki ne bisa ka’idojin aikin gwamnati don haka ya kamata a cire su daga aikin tantancewar da ake yi a jihar domin samar da zaman lafiya, hadin kai da adalci.

 

Ya kuma umurci mashawarcin da ke gudanar da aikin tantancewar da ya mayar da wasikun daykar aiki da aka karbo ga malamai 1000 da ke kan lissafin albashin gwamnati nan take.

 

A cewarsa, wannan abin bakin ciki ne kuma abin takaici ne, wadannan malamai 1000 sun samu aikin yi yadda ya kamata kuma suna karbar albashin watanni 9.

 

“Kudirin da majalisar ta yi shi ne, muna godiya ga mai girma Gwamna Abdullahi Sule bisa yadda ya dauki malamai aikin yi domin kara inganta harkar ilimi da kuma rage rashin aikin yi a jihar.

 

 

“Muna kuma umurtar mai ba da shawara da ya mayar wa malamai 1000 wasikun daukar da aka karbo nan take sannan su ci gaba da koyarwa, a biya su albashi” Inji shi.

 

“Kada wata hukuma ta dauki laifin wani, malamai 1000, kowa ya san ba su da laifi domin sun bi duk hanyoyin da suka dace don haka kada a ci zarafinsu, abin da muke yi shi ne kare gwamnati da doka.” Ya kara da cewa.

 

Mataimakin shugaban majalisar ya kuma kafa kwamiti na mutum shida wanda Daniel Ogazi zai jagoranta tare da shugaban kwamitin ilimi Abel Yakubu Bala tare da Luka Iliya Zhekaba a matsayin Sakatare da Barr. Esson Mairiga, Solomon Akwashiki da Muhammed Garba Isimbabi a matsayin membobi don kawo duk masu laifin da suka sayar da wasikun daukar aiki ga ’yan asalin jihar domin su samu.

 

“Wannan kwamiti zai kasance karkashin jagorancin Hon Daniel Ogazi tare da Hon. Luka Iliya Zhekaba, shugaban marasa rinjaye a matsayin sakataren kwamitin.

 

“Sauran mambobin sun hada da Hon. Solomon Yakubu Akwashiki, Hon. Mohammed Garba Isimbabi da Hon. Barr. Esson Mairiga” inji shi.

 

Mataimakin shugaban majalisar ya yi kira ga gwamna Abdullahi Sule da ya yi adalci tare da tausaya wa sauran malamai sama da 2000 da ba a biya su albashi ba.

COV/Aliyu Muraki/Lafia.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mutanen da suka mutu a ambaliyar Neja sun ƙaru zuwa 88 —NSEMA
  • NAJERIYA A YAU: Yaya Girman Matsalar Rashin Tsaro A Shekaru Biyun Tinubu?
  • NDLEA ta kama maniyyata aikin hajji ɗauke da hodar iblis
  • MDD Ta Gudanar Da Bikin Ranar Tunawa Da Dakarun Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Duniya Ta 2025
  • Majalisar Nasarawa Ta Bukaci A Cire Malamai 1000 Daga Aikin Tantancewar Da Ake Yiwa Malamai
  • ’Yar Najeriya ta tsinci miliyan 8.2 a Saudiyya ta mayar wa da mai su
  • Kamfanoni Mallakin Gwamnatin Sin Sun Samu Bunkasa Bisa Daidaito Cikin Watanni Hudu Na Farkon Bana
  • Gwamna Uba Sani Ya Kammala Titin Unguwar Su El-Rufai
  • Sojoji sun halaka mayakan ISWAP da dama a Borno