Aminiya:
2025-07-26@17:11:58 GMT

NAHCON ta kammala jigilar maniyyata aikin hajjin 2025

Published: 29th, May 2025 GMT

Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta kammala jigilar maniyyatan Najeriya zuwa ƙasar Saudiyya domin gudanar da aikin hajjin shekarar 2025.

Da yake jawabi ga manema labarai a filin jirgin sama na Nnamdi Azikiwe da ke Abuja kafin jirgin maniyyatan ya tashi zuwa Saudiyya, Shugaban Hukumar NAHCON, Farfesa Abdullahi Saleh Usman, ya ce aikin Hajjin bana ya samu nasarori da dama da suka nuna ci gaba da inganta aikin hajjin Nijeriya.

NDLEA ta kama maniyyata aikin hajji ɗauke da hodar iblis ’Yan bindiga sun kashe makiyaya 2, sun sace shanu 320 a Kaduna

Ya ce, an yi jigilar maniyyata 41,568 ta jiragen sama 105.

Hakan na zuwa ne a daidai lokacin da ya nuna matuƙar godiya ga shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu da mataimakin shugaban ƙasa, Sanata Kashim Shettima bisa gagarumin goyon bayan da suka bayar wajen ganin an gudanar da aikin Hajjin 2025 cikin nasara.

A cewarsa, duk da cewa aikin jigilar jirage ba abu ne mai sauƙi ba, tare da haɗin gwiwar masu ruwa da tsaki, hukumar ta samu nasarar kammala aikin.

Shugaban Hukumar NAHCON ya bayyana cewa, akwai ƙalubale a yayin aikin jigilar jiragen amma tare da haɗin gwiwar hukumar ta samu nasarar cimma burinta na ganin duk wani mahajjatan Najeriya ya tafi ƙasa mai tsarki tare da kula da su yadda ya kamata.

“Yayin da muke rufe shirin jigilar jirage zuwa aikin Hajjin 2025 na bana daga kason jihar, wannan lokaci ne mai matuƙar muhimmanci a gare mu baki ɗaya domin hakan na nufin mun samu nasarar kwashe dubban maniyyatanmu cikin ‘yan makonni.

“Ba abu ne mai sauƙi ba, amma da kyakkyawan tsari, bayan taimakon Allah Maɗaukakin Sarki da haɗin gwiwar da muka yi, mun kammala aiki cikin nasara, Alhamdulillah.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Anacláudia Rossbach: Ya Kamata Kasashen Afirka Su Koyi Darasi Daga Sin Na Kawar Da Talauci Da Kyautata Kauyuka Zuwa Birane

Kwanan nan, darektar zartaswa ta hukumar kula da matsugunan dan Adam ta MDD, Anacláudia Rossbach, ta yi hira da wakilin babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na Sin wato CMG, a hedkwatar hukumar kula da matsugunan dan Adam ta MDD dake Nairobi, babban birnin Kenya.

Yayin da aka ambato sakamakon da ya fi jawo hankali da Sin ta samu yayin kyautata kauyuka zuwa matsayin birane da garuruwa, Rossbach ta bayyana cewa, Sin ta cimma nasarar kawar da talauci ga mutane miliyan 800, da kuma tafiya a kan hanyar kyautata kauyuka zuwa birane da garuruwa, kuma wannan darasi ne da ya cancanci kasashen Afirka wadanda suke fuskantar kalubalen kyautata kauyuka zuwa birane su yi koyi da shi.

Ta ce, nan da shekaru 25 masu zuwa, mutane kusan miliayn 800 na kasashen Afirka da na Latin Amurka za su yi kaura zuwa birane, kuma kasashen Asiya da dama su ma suna fuskantar kalubalen fama da talauci. A cewarta, birane na da muhimmanci sosai wajen kawar da talauci, kuma ba ma kawai ya kamata a ba da wurin kwana ga mutane a cikin birane ba, har ma ya dace a ba su damammakin samun ilmi, da guraben ayyukan yi da sauransu, da kuma samun hidimomin kiwon lafiya don kiyaye koshin lafiyarsu, kana ta ce, wannan shi ne muhimmin abun da za mu ci gaba da gudanarwa da kuma tattaunawa a kai. (Safiyah Ma)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Za a ɗauke wuta na tsawon kwanaki 25 a Legas — TCN
  • WAFCON 2025: Yau Nijeriya Za Ta Kece Raini Da Moroko A Wasan Ƙarshe
  • Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50
  • Rayuwar Aso Rock: Shugabannin Nijeriya 4 Da Suka Mutu Bayan Kammala Wa’adin Mulki
  • Gwamnan Jigawa Ya Rattaba Hannu Kan Kudirin Dokar Tabbatar Da Hisbah
  • NAJERIYA A YAU: Yadda masu yi wa kasa hidima za su ci arzikin yankunan da suke aiki
  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Da Karamar Hukumar Dutse Za Su Shirya Taron Bita Ga Kansiloli
  • Anacláudia Rossbach: Ya Kamata Kasashen Afirka Su Koyi Darasi Daga Sin Na Kawar Da Talauci Da Kyautata Kauyuka Zuwa Birane
  • NAJERIYA A YAU: Cututtukan da rumar daki ke haifarwa ga jikin mutum
  • Zan Ci Gaba da Taka Leda A Kano Pillars Duk da Matsayin Da Na Samu — Ahmed Musa