NAHCON ta kammala jigilar maniyyata aikin hajjin 2025
Published: 29th, May 2025 GMT
Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta kammala jigilar maniyyatan Najeriya zuwa ƙasar Saudiyya domin gudanar da aikin hajjin shekarar 2025.
Da yake jawabi ga manema labarai a filin jirgin sama na Nnamdi Azikiwe da ke Abuja kafin jirgin maniyyatan ya tashi zuwa Saudiyya, Shugaban Hukumar NAHCON, Farfesa Abdullahi Saleh Usman, ya ce aikin Hajjin bana ya samu nasarori da dama da suka nuna ci gaba da inganta aikin hajjin Nijeriya.
Ya ce, an yi jigilar maniyyata 41,568 ta jiragen sama 105.
Hakan na zuwa ne a daidai lokacin da ya nuna matuƙar godiya ga shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu da mataimakin shugaban ƙasa, Sanata Kashim Shettima bisa gagarumin goyon bayan da suka bayar wajen ganin an gudanar da aikin Hajjin 2025 cikin nasara.
A cewarsa, duk da cewa aikin jigilar jirage ba abu ne mai sauƙi ba, tare da haɗin gwiwar masu ruwa da tsaki, hukumar ta samu nasarar kammala aikin.
Shugaban Hukumar NAHCON ya bayyana cewa, akwai ƙalubale a yayin aikin jigilar jiragen amma tare da haɗin gwiwar hukumar ta samu nasarar cimma burinta na ganin duk wani mahajjatan Najeriya ya tafi ƙasa mai tsarki tare da kula da su yadda ya kamata.
“Yayin da muke rufe shirin jigilar jirage zuwa aikin Hajjin 2025 na bana daga kason jihar, wannan lokaci ne mai matuƙar muhimmanci a gare mu baki ɗaya domin hakan na nufin mun samu nasarar kwashe dubban maniyyatanmu cikin ‘yan makonni.
“Ba abu ne mai sauƙi ba, amma da kyakkyawan tsari, bayan taimakon Allah Maɗaukakin Sarki da haɗin gwiwar da muka yi, mun kammala aiki cikin nasara, Alhamdulillah.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani
A bayan bayan nan, an aiwatar da jerin tattaunawa tsakanin Sin da Amurka karkashin jagorancin shugabanninsu, inda aka samu kyawawan sakamakon da ya kyautata alakarsu ta tattalin arziki da cinikayya. Wannan ya nuna shawarar da a kullum Sin ke bayarwa cewa, tattaunawa ita ce mafita ga dukkan rikice-rikice, maimakon amfani da karfi.
Kasar Sin ta sha nanata cewa, babu mai samun nasara a yakin cinikayya ko haraji. Mun ga yadda aka samu hauhawar farashin kayayyaki da karuwar rashin aikin yi da faduwar darajar hannayen jari a Amurka, a lokacin da ta kaddamar da yakin haraji, wanda ya nuna cewa, maimakon cimma abun da take fata na samun fifiko, asara aka samu da lalacewar muradun kamfanoni da ’yan kasuwar kasar.
Kowace kasa tana da cikakken iko da ’yancin zabar manufofi da matakan da ya dace da ita. Da Sin ta tsaya kai da fata cewa ba za ta ba da kai a yakin haraji da Amurka ta tayar ba, hakan ya sa Amurka yin karatun ta nutsu, kuma ta tuntubi bangaren Sin domin tattaunawa.
Wadannan misalai sun nuna mana cewa, akwai hanyoyi masu sauki da inganci na samun maslaha, kuma shawarwarin da Sin take gabatarwa, su ne suka dace da yanayin duniya a yanzu. Ba dole sai kowa ya samu abun da yake so ba, amma hawa teburin sulhu da tuntubar juna tana taka muhimmiyar rawa wajen warware sabani, da lalubo inda kowane bangare zai iya saki, domin a samu mafitar da za ta karbu ga kowa. Kuma irin wannan din, shi ne burin sabuwar Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya da shugaban kasar Sin ya gabatar a baya bayan nan. Duniya ba ta bukatar mayar da hannu agogo baya ta hanyar tayar da rikice-rikice da danniya da nuna fin karfi, zamani ya sauya kuma dole salon tafiyar da harkoki ya sauya, domin dacewa da yanayin da ake ciki.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp