‘Yan Wasan Kano Sun Rasu Sanadiyar Hadarin Mota Yayin Dawowa Daga Gasar Wasanni Ta Kasa
Published: 31st, May 2025 GMT
Aƙalla ‘yan wasa 20 daga tawagar jihar Kano ne suka rasu, yayin da da dama suka jikkata, sakamakon mummunan hatsarin mota da ya faru a gadar Dakatsalle, sa’ilin da suke dawowa daga Gasar Wasanni ta Kasa da aka kammala kwanan nan a Abeokuta.
Shugaban Hukumar Wasanni ta Jihar Kano, Umar Bala Fagge, ya tabbatar da faruwar lamarin.
Ya bayyana cewa motar da ke ɗauke da ‘yan wasan, wadda ke ɗauke da mutane 30, ta faɗa gadar ta Dakatsalle da ke jihar ta Kano.
“Yayin da nake magana da ku yanzu, mun kirga gawarwaki 19,” ya fada cikin tashin hankali.
Ado Salisu, tsohon Mataimakin Shugaban Kungiyar ‘Yan Jarida da ke kula da lamuran Wasanni ta Najeriya (SWAN), ya ce an kai waɗanda suka jikkata babban asibitin gwamnati da ke Kura.
Daga cikin waɗanda suka rasu akwai ɗan Salisu Jegu, ɗan jarida a fannin wasanni na gidan rediyon Express Radio.
Daga Khadijah Aliyu
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Hatsari
এছাড়াও পড়ুন:
Jami’an Tsaro Sun Ceto Mutum 11 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Sakkwato
Gobir ya bayyana cewa kowanne daga cikin waɗanda aka ceto zai samu Naira 100,000, buhun gero ɗaya da buhun masara ɗaya a matsayin tallafi.
Shi ma da yake magana, Shugaban ƙaramar hukumar Isa, Alhaji Sherifu Abubakar Kamarawa, ya gode wa gwamnatin jihar bisa taimakon da ta bayar, yana mai cewa hakan ya nuna damuwar gwamnati kan tsaron rayuka da jin daɗin al’umma.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp