Nau’ikan Amfanin Gona Da Ke Saurin Girma Cikin ‘Yan Watanni
Published: 31st, May 2025 GMT
Akasari kafin a girbe ta, tana kaiwa kwanaki 60 zuwa 100 bayan an shuka ta. Kazalika, cikin sauki ake mallakar gonar da ake shuka Masara a Nijeriya, ana kuma shuka Irinta sannan a sayar da ita ga makwabta.
Dankali: Dankali na dauke da sinadarin ‘calories’ dan kadan, sannan mutane da dama na kasar nan na sarrafa shi a matayin abinci tare da yin amfani da shi.
Tumatir: Ana matukar amfani da tumatir a Nijeriya, ko danyensa ko kuma busasshe. Yana dauke da sanadarin ‘bitamin C’, yana kuma taimakawa wajen rage kamuwa da cututtuka kamar wadanda ke yi wa zuciya illa, ciwon siga da kuma cutar daji.
Ana son a shuka Irinsa a kasar noma mai kyau tare da yi masa ban ruwa. Bayan an shuka Irin nasa, ana fara girbe shi daga watanni 2 zuwa 3, ya danganta da nau’in Irin da aka yi amfani da shi wajen shukawa.
Kankana: Duk yayin da aka shuka Irin Kankana, cikin dan gajeren lokaci ake girbe ta. A Nijeriya, daga wata 3 ake fara girbe ta, sannan ana iya shuka Irinta a kowanne bangare na fadin wannan kasa. Wakazalika, kankana na dauke da sinadarin ‘bitamin A’ da kuma ‘bitamin C’ mai yawan gaske.
Tattasai: Bayan shuka Irin tattasai, ana girbe shi cikin watanni uku kacal. Kazalika, ana iya cewa kusan kowane gida a fadin Nijeriya na yin amfani da shi. Ana kuma sayar da tattasai a kasuwanni da dama a wannan kasa, sannan wadanda ke yin sana’arsa na matukar samun rufin asiri ko kudaden shiga. Hatta a bayan dakin gidanka, za ka iya shuka Irin Tattasai ya girma ya kuma bayar da abin da ake so.
8. Kokumba: Kokumba na daya daga cikin sanannin kayan marmari ko lambu, ana kuma yin noman sa a wurare da dama na fadin Nijeriya. Wasu na cin sa tsurarsa, domin alfanun da yake da shi musamman a fannin kiwon lafiya. A duk lokacin da aka shuka Irinsa yana da matukar saurin yin girma, ana kuma girbe shi bayan akalla watanni 3. Sannan yana da saurin tafiya a kasuwa, ma’ana mutane suna son sa kwarai da gaske sakamakon amfaninsa ga lafiyar dan Adam.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Yadda ambaliyar Neja ta ci mutum 12 ’yan gida daya
Wasu mutum 12 ’yan gida daya da almajirai sama da 50 na cikin mutanen da suka rasu a ambaliyar ruwan da ta afka wa yankin Tiffin Maza da Anguwan Hausawa na karamar hukumar Mokwa a jihar Neja a ranar Laraba.
Ambaliyar, wacce ta biyo bayan wani mamakon ruwan sama da aka tafka a daren na Laraba, ta kuma lalata dukiyoyi da dama, yayin da har yanzu ake ci gaba da neman wasu mutanen da suka bace.
Garin Mokwa dai ya shahara da zama wani zango na direbobin manyan motoci, wanda hakan ya sa garin ya zama daya daga cikin mafiya hada-hadar mutane a jihar ta Neja.
NAHCON ta kammala jigilar maniyyata aikin hajjin 2025 Ambaliyar ruwa ta kashe sama da mutum 50 a NejaAminiya ta gano cewa akasarin wadanda iftila’in ya fi shafa mata ne da kananan yara.
Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Jihar Neja (NSEMA) ta tabbatar da mutuwar mutum 21, amma mutanen yankin sun ce wadanda suka mutu za su iya haura 60.
Daga cikin mutanen da suka rasu a ambaliyar har da wata dalibar Kwalejin Kiwon Lafiya ta Jihar Neja mai suna Binta, wacce ta je garin na Mokwa domin yin hutu, kuma tuni har an samo gawarta.
Wata ’yar yankin mai suna Hajiya Hassana Mokwa, ta shaida wa wakilinmu cewa akalla danginta 12 zuwa 13 ne suka rasu a ambaliyar, wanda kawai ya saura kuma yanzu haka yana can a kwance a asibiti ranga-ranga.
Ta kuma ce akwai wasu daliban makarantar Alkur’ani mallakin dan uwanta da su ma suka rasa ransu.
“Akwai almajirai da dama a makarantar Alkur’anin dan uwana da su ma suka rasu. Babu wanda ya saura da rai a cikin gidan, gaba daya gidan nitsewa ya yi. Idan ka je wajen yanzu, ba za ka taba tinanin ma an taba yin gini a wajen ba,” in ji Hajiya Hassana.