Janar Musa ya fallasa ƙasashen da ke ɗaukar nauyin Boko Haram
Published: 16th, February 2025 GMT
Babban Hafsan Hafsoshin Tsaron Najeriya, Janar Christopher Musa, ya sake jaddada cewa ƙasashen waje ne ke tallafa wa ’yan ta’addan Boko Haram da kuɗi da makamai.
A wata hira da ya yi da Al Jazeera, Janar Musa ya nuna damuwa kan yadda ƙungiyar ke ci gaba da aikata ta’addanci sama da shekaru 16, duk da ƙoƙarin da sojojin Najeriya ke yi na daƙile.
Ya bayyana cewa an kama wasu ’yan Boko Haram ɗauke da maƙudan kuɗaɗe da ke da alaƙa da ƙasashen ƙetare.
Ya nuna cewa akwai ƙasashen da ke taimaka wa ƙungiyar daga waje.
Janar Musa ya yi tambaya cewar: “Ta yaya Boko Haram suka ci gaba da kai hare-hare tsawon shekaru 15?”
Bayanansa sun samu goyon baya daga wani ɗan majalisar dokokin Amurka, Scott Perry, wanda ya zargi hukumar USAID da bai wa ƙungiyoyin ‘yan ta’adda, ciki har da Boko Haram, tallafin dala miliyan 697 a kowace shekara.
Perry, ya ce akwai shaidun da ke nuna cewa kuɗaɗen da ake warewa wasu ƙasashen duniya don tallafa wa al’umma, kamar Pakistan da Afganistan, ba sa zuwa inda ya kamata, maimakon haka, ana amfani da su wajen ɗaukar nauyin ’yan ta’adda.
Bincike, ya nuna cewa an ware dala miliyan 136 don gina makarantu 120 a Pakistan, amma babu wata shaida da ke tabbatar da cewa an gina waɗannan makarantu.
A cewar Janar Musa, akwai buƙatar a binciki waɗannan kuɗaɗe da ake samu a hannun Boko Haram.
Ya ce: “Ina suke samun kuɗin? Wane ne ke ba su horo da makamai?”
Samun ’yan Boko Haram sama da 120,000 da aka kama ɗauke da kuɗaɗen ƙasashen waje ya haifar da tambayoyi masu yawa kan haƙiƙanin tushen ƙungiyar.
Janar Musa, ya jaddada cewa ikon Boko Haram na ci gaba da kai hare-hare a Najeriya na nuna cewa suna samun tallafi daga ƙasashen waje.
Masana harkokin tsaro sun buƙaci gwamnati da sojojin Najeriya da su ƙara ƙaimi wajen bankaɗo waɗanda ke bai wa ’yan ta’adda goyon baya daga ƙetare.
Janar Musa, dai ya samu yabo kan yadda yake ƙoƙarin kawo ƙarshen ayyukan ta’addanci a Najeriya, yayin da ya ke ci gaba da jagorantar sojojin ƙasar wajen yaƙi da ‘yan ta’adda.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Boko Haram hare hare yan ta adda
এছাড়াও পড়ুন:
Mulkin Tinubu ya fi kowane muni tun bayan dawowar mulkin farar hula — Dalung
Tsohon Ministan Matasa da Wasanni, Solomon Dalung, ya ce shekara biyu da Bola Ahmed Tinubu ya yi a matsayin shugaban ƙasa sun fi kowane lokaci muni tun bayan dawowar mulkin dimokuraɗiyya a ƙasar.
Yayin da yake magana da BBC a ranar Dimokuraɗiyya da Najeriya ke cika shekaru 26 tana mulkin farar hula, Dalung ya ce ba wani abin arziƙi da talaka ya amfana da shi daga wannan gwamnati.
An kama ’yar Najeriya da laifin safarar ɗalibai 15 a Australia Abin da muke da shi a Najeriya ba cikakkiyar dimokuraɗiyya ba ce — FayemiYa ce: “Kawai abin da talaka ya samu daga gwamnatin Tinubu shi ne tsadar rayuwa, yunwa, wahala da matsalar tsaro.”
Ya zargi gwamnatin da cewa cire tallafin man fetur ba tare da shiri ba, kuma hakan ya jefa mutane cikin ƙuncin rayuwa.
“Talakawa na mutuwa saboda yunwa, amma idan an tambayi Shugaba Tinubu, sai ya ce bai yi nadamar cire tallafin ba,” in ji Dalung.
Gwamnatin Tinubu dai ta ce ta cire tallafin ne domin hana wasu tsiraru ci gaba da cin gajiyarsa da kuma bunƙasa tattalin arziƙin ƙasa.
Amma Dalung ya ce gwamnatin ba ta talaka ta ke ba: “Idan ba canza motoci da jirage da gina sabon gida ga mataimaki ba, to babu wani abu da talaka ya gani.”
Dalung ya ce dimokuraɗiyya na cikin mawuyacin hali tun zuwan Tinubu, ya zargi gwamnati da kama waɗanda ke sukar ta da kuma sayen abokan hamayya wajen komawa APC.
“Mun ga yadda ake kama ‘yan gwagwarmaya saboda kawai sun faɗi ra’ayinsu. Kuma wasu na komawa jam’iyyar APC bayan an saye su,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa gwamnati na barazana ga ci gaban ƙasa idan ba a gyara lamarin ba.
Dalung, ya ce duk da rahoton Bankin Duniya da ke cewa tattalin arziƙin Najeriya na bunƙasa, bai yarda ba.
“Ta yaya za ku ce tattalin arziƙin da ke cikin matsin lamba yanzu yana bunƙasa? Wannan fa ba gaskiya ba ce.”