Leadership News Hausa:
2025-07-13@03:07:04 GMT

Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Gana Da Jakadun Kasashen Afirka

Published: 28th, May 2025 GMT

Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Gana Da Jakadun Kasashen Afirka

Sun kara da cewa, kasashen Afirka za su kafe kai da fata wajen mutunta ka’idar Sin daya tak a duniya, da goyon bayan duk kokarin da kasar Sin ta yi na kare ikon ’yancinta da cimma burin sake hadewar kasar, da yin adawa da tsoma baki a harkokin cikin gidan kasar Sin, kana suka ce, kasashen Afirka za su kiyaye manufofi da ka’idojin yarjejeniyar kafa MDD, tare da kare muradu na bai daya na kasashe masu tasowa da kasar Sin.

(Abdulrazaq Yahuza Jere)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Mauritaniya Ta Karyata Rahoton Cewa Shugaban Kasarta Ya Gana Da Netanyahu

Gwamantin kasar Mauritaniya ta musanta cewa shugabanta ya gana da Netanyahu, ta yi kira ga tashar Al Arabiya da ta tabbatar da sahihancin rahoton kafin watsa shi

Ministan al’adu da sadarwa na Mauritaniya kuma mai magana da yawun gwamnatin kasar Hussein Ould Maddou ya musanta sahihancin rahotannin ganawar da ake zargin shugaban kasar Mauritaniya da Fira ministan haramtacciyar kasar Isra’ila Benjamin Netanyahu.

Kamfanin dillancin labaran Jamus ya nakalto ministan na cewa rahoton da tashar Al Arabiya ta watsa game da ganawar da ake zargin shugaba Mohamed Ould Ghazouani da Fira ministan Igwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ba shi da tushe balle makama.

Ya yi nuni da cewa, labaran ba su da inganci, inda ya yi kira ga tashar Al-Arabiya da ta kasance mai gaskiya wajen samun bayanai tare da kaucewa yada labaran karya.

Kakakin gwamnatin ya kuma jaddada cewa: Daya daga cikin muhimman ayyuka na sana’ar jarida shi ne dogaro da majiyoyin hukuma, musamman idan aka yi la’akari da budi da saukin da ake baiwa wadannan majiyoyi manyan a tsakanin kafafen yada labarai masu neman sahihan bayanai.

Shugaban Mauritaniya ya halarci taron hadin gwiwa tsakanin shugaban Amurka Donald Trump da wasu shugabannin Afirka biyar kan hadin gwiwar tattalin arziki.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 
  • Gwamnatin Mauritaniya Ta Karyata Rahoton Cewa Shugaban Kasarta Ya Gana Da Netanyahu
  • Kyautar ‘Jakadan Abota’ Na Kasar China Ya Shiga hannun Iran
  • Lavrov: Shuwagabannin Kasashen Yammacin Turai Suna Son Shiga Yaki Da Rasha
  • “Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai
  • Wang Yi Ya Gana Da Sakataren Harkokin Wajen Amurka
  • Najeriya Ba Za Ta Karbi ‘Yan Ci Ranin Kasar Venezuela Da Amurka Za Ta Kora Ba
  • Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ya Yi Allah  Wadai Da Kakaba Takunkumi Kan Jami’ar Majalisar Dinkin Duniya
  • Mataimakin Babban Magatakardan MDD: Sin Aminiya Ce Da Afirka Za Ta Iya Dogaro Da Ita
  • Aragchi Ya Tattauna Da Bin Salman Kan Karfafa Zumunci Tsakanin Kasashen Biyu