An kama mutum 41 da ake zargi da kisan DPO a Kano
Published: 30th, May 2025 GMT
Rundunar ’yan sandan Jihar Kano ta ce, ta kama mutane 41 da ake zargi da hannu a kisan DPO ɗin Rano, CSP Baba Ali.
Rundunar ta bayyana lamarin, wanda ya janyo kace-nace, a matsayin harin kai tsaye kan sadaukarwar da jami’an tsaro ke yi, waɗanda suke sadaukar rayuwarsu domin kare al’umma.
NAHCON ta kammala jigilar maniyyata aikin hajjin 2025 NDLEA ta kama maniyyata aikin hajji ɗauke da hodar iblisA wata sanarwa da kakakin rundunar ’yan sandan jihar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya fitar a ranar Alhamis, ya ce rundunar ’yan sanda na aiki tuƙuru domin ganin an gurfanar da duk waɗanda ke da hannu wajen kisan, da kuma masu alaƙa da ƙone-ƙone.
Sanarwar ta ƙara da cewa, “Rundunar ta bayyana kaɗuwarta da alhini dangane da kisan gillar da aka yi wa CSP Baba Ali a lokacin da yake bakin aiki, wannan kashe-kashen na rashin hankali babban hari ne ga al’ummarmu.”
Kiyawa ya ce Kwamishinan ’yan sanda, CP Ibrahim Adamu Bakori ya tabbatar wa mazauna Jihar Kano cewa, rundunar ta ci gaba da jajircewa wajen kare rayuka da dukiyoyin jama’a, kuma babu wani abin da za a bari wajen ganin an hukunta waɗanda suke da alaƙa da kisan jami’in.
Sanarwar ta ƙara da cewa, “Kwamishinan ya sake nanata cewa ’yan sanda ba za su ƙasa a gwiwa ba har sai an hukunta duk wanda ke da alaƙa da wannan ɗanyen aiki.”
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Yan Sanda DPO ɗin Rano
এছাড়াও পড়ুন:
Zamfarawa sun yi zanga-zanga kan kisan sama da mutum 100
Wasu mazauna Ƙaramar Hukumar Gusau da ke Jihar Zamfara, sun yi zanga-zangar lumana tare da neman gwamnati ta ɗauki kan ƙaruwar hare-haren ’yan bindiga a yankin.
Zanga-zangar ta fara ne da misalin ƙarfe 12 na ranar Laraba.
Nentawe Yilwatda ne zai zama sabon shugaban APC na ƙasa Sojoji sun kashe Kwamandan Boko Haram Ibn Khalid a BornoJama’a da dama sun halarci zanga-zangar; wasu a kan babura, wasu a cikin motoci, wasu kuma a ƙafa.
Kuma sun taru a ƙofar gidan gwamnatin Jihar da ke Gusau domin nuna damuwarsu.
Ƙauyukan da abin ya fi shafa sun haɗa da Mada, Ruwan Bore, Fegin Baza, Bangi, Lilo, Wonaka, da Fegin Mahe.
Mazauna yankunan sun ce sama da mutum 100 ’yan bindiga suka kashe a baya-bayan nan.
Wani daga cikin masu zanga-zangar, Malam Abubakar Abdullahi daga ƙauyen Fegin Mahe, ya ce ’yan bindiga sun kashe ’yan uwansa da dama, sannan kuma sun sace musu kaya da darajarsu ta haura Naira miliyan ɗaya, ciki har da buhun taki guda 500.
Hare-haren sun hana manoma yin aiki a gonakinsu, saboda rashin tsaro a yankin.
Shugaban Ƙaramar Hukumar Gusau, Abubakar Iman, ta bakin wakilinsa Aminu Wakili Mada, ya ce ya fahimci ƙorafin jama’ar yankunan.
Ya tabbatar da cewa gwamnati tare da jami’an tsaro suna aiki tare domin tabbatar da zaman lafiya, kuma za a tura ƙarin jami’an tsaro zuwa wuraren da suka fi fama da matsala nan ba da jimawa ba.
Yunƙurin jin ta bakin kakakin rundunar ’yan sandan jihar, DSP Yazid Abubakar, ya ci tura domin bai amsa waya ba.
A wani labarin kuma, jami’an tsaro sun ceto mutum 11 da aka sace a dajin da ke Ƙaramar Hukumar Zurmi a Jihar Zamfara.
An sace mutanen ne a ƙauyen Kaibaba da ke gundumar Turba a Ƙaramar Hukumar Isa a Jihar Sakkwato.
An miƙa su ga Gwamnatin Jihar Sakkwato a ranar Laraba.