Aminiya:
2025-05-30@16:26:39 GMT

An kama mutum 41 da ake zargi da kisan DPO a Kano

Published: 30th, May 2025 GMT

Rundunar ’yan sandan Jihar Kano ta ce, ta kama mutane 41 da ake zargi da hannu a kisan DPO ɗin Rano, CSP Baba Ali.

Rundunar ta bayyana lamarin, wanda ya janyo kace-nace, a matsayin harin kai tsaye kan sadaukarwar da jami’an tsaro ke yi, waɗanda suke sadaukar rayuwarsu domin kare al’umma.

NAHCON ta kammala jigilar maniyyata aikin hajjin 2025 NDLEA ta kama maniyyata aikin hajji ɗauke da hodar iblis

A wata sanarwa da kakakin rundunar ’yan sandan jihar, SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya fitar a ranar Alhamis, ya ce rundunar ’yan sanda na aiki tuƙuru domin ganin an gurfanar da duk waɗanda ke da hannu wajen kisan, da kuma masu alaƙa da ƙone-ƙone.

Sanarwar ta ƙara da cewa, “Rundunar ta bayyana kaɗuwarta da alhini dangane da kisan gillar da aka yi wa CSP Baba Ali a lokacin da yake bakin aiki, wannan kashe-kashen na rashin hankali babban hari ne ga al’ummarmu.”

Kiyawa ya ce Kwamishinan ’yan sanda, CP Ibrahim Adamu Bakori ya tabbatar wa mazauna Jihar Kano cewa, rundunar ta ci gaba da jajircewa wajen kare rayuka da dukiyoyin jama’a, kuma babu wani abin da za a bari wajen ganin an hukunta waɗanda suke da alaƙa da kisan jami’in.

Sanarwar ta ƙara da cewa, “Kwamishinan ya sake nanata cewa ’yan sanda ba za su ƙasa a gwiwa ba har sai an hukunta duk wanda ke da alaƙa da wannan ɗanyen aiki.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda DPO ɗin Rano

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban  Iran na ziyarar aiki a kasar Oman

Shugaban kasar Iran, Massoud Pezeshkian, ya fara wata ziyarar aiki a kasar Oman mai manufar karfafa dangantaka tsakanin kasashen biyu aminnan juna.

Shugaba Pezeshkian ya yaba da rawar da Oman ta taka a tattaunawar dake tsakanin Iran da Amurka, kuma tana fatan za a cimma sakamako mai kyau.

Pezeshkian ya bayyana hakan ne yayin ganawa da ya yi da Sultan Haitham bin Tariq na Oman a birnin Muscat a yammacin yau Talata.

Da yake jaddada matsayin kasar Oman a cikin manufofin ketare na Iran, Pezeshkian ya ce Tehran na da cikakkiyar amincewa ga Oman, kuma wannan amana na karfafa alaka tsakanin kasashen biyu.

Shugaban ya ce Iran a shirye ta ke ta inganta hadin gwiwa da Oman a dukkan fannoni, yana mai imani cewa kasashen biyu suna da karfin da za a iya amfani da su don cin moriyar juna da sauran al’ummomin yankin,” in ji shi.

Ya ce Iran a shirye take ta inganta hadin gwiwa da Oman a fannonin, kimiyya, ilimi, da fasaha, musamman a fannin likitanci.

A nasa bangare Sultan Haitham ya bayyana cewa ya yarda idan aka bude hanyoyin gudanar da harkokin kasuwanci, kasashen biyu za su samu gagarumin ci gaba a huldar dake tsakaninsu.

Dangane da tattaunawar dake tsakanin Iran da Amurka, Sultan Haitham ya ce Muscat ta shiga tsakani a tattaunawar da alheri,” in ji shi.

Sarkin na Oman ya kuma yaba da matsayin Iran na kare al’ummar Falasdinu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Yi Tsokaci Kan Hanyar Warware Takaddamar Shirin Makamashin Nukiliyar Iran
  • An Kama Mutane 49 Da Ake Zargi Da Damfara A Jihar Kogi
  • ‘Yansanda Sun Kama Mutane 41 Da Ake Zargi Da Kisan DPO A Kano
  • Makarantar ‘Ya’yan Sojoji Ta Zaria Ta Yi Bukin Cika Shekaru 70 Da Kafawa
  • Kotu ta yanke wa Murja Kunya hukuncin dauri a gidan yari
  • Babu Wata Sauran Mafaka Ga ‘Yan Ta’adda, In Ji Shugaban Rundunar Sojin Sama
  • Shugaban  Iran na ziyarar aiki a kasar Oman
  • ‘Yansanda Sun Kama Wanda Ake Zargi Da Kisan Wata Matar Aure, ‘Yar shekara 22 A Kano
  • CMG Ta Cimma Nasarar Gudanar Da Gasar Mutum-Mutumin Inji Ta Kasa Da Kasa